← Book details Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 43

Sashe 26

Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

kallon su Rumaisa tayi tace" yaya yace nan ne gidan Aunty Ameerah mushiga mugani ,kallon mamaki sukayi masa sedai be basu damar magana ba ,sema cewa da yayi "Rumaisa kishiga kudubata sauri nakeyi " bin banyan Meerah tayi ,ita dai Rufee kamar wacce aka kafe a wurin tama kas motsi ,lokacin da suka kai kofar gidan yayi dai² da fitowar Meerah tare da Muhsin ,alamar rakiya tayo masa ,sam bata kula dasu ba se da Nawwara ta rungume ta tana murnar ganin ,da mamaki ta cire hannayen ta da ta zagaye cikin ta dasu itama cikin jin daɗin ganin su tace " Auta waya nuna muku gidan mu? munxo ne muduba ki kwana biyu shiru ko bakida lafiya ne ,ashe ke kina nan soyayya ta ɓoyeki "ta faɗa cikin sigar zolaya "rufe ido Meerah tayi tana daria tace " Aunty ai wannan yaya ne ko? Tayi maganar tana kallon Muhsin ,se a lokacin Rumaisa ta gaidashi ,amsawa yayi yana shiga Mota tare da faɗin " bara na wuce tunda kinyi baƙi xamuyi waya dai Allah yaƙara lafiya"bata amsa shiba sedai ta ɗaga masa kai kawai tare dayimasa waving ,seda ya tada motar tukuna ta ja hannun Rumaisa tace" mushiga ciki Aunty " bin bayanta Rumaisa tayi.......

Comments and share pls

Real Bazamfaria ce ❤️
*INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION*
   ( *On* *word* *together* )

*MABARACIYA*

*Story* *and* *writing*

    *By*

*FIDDAUSI* *SANI*
      (damsel feedorh)

🅿️:2️⃣6️⃣

suka shiga gidan lokacin Aunty tashig ɗaki dan haka direct ɗakin ta ta shigar dasu ,a bakin katifar ta Rumaisa ta zauna ,dan itakam Nawwara tana maƙale da ita ,fita tayi tasanar wa Aunty zuwan su " to ki ɗauki ruwa a firjin ki kai musu mana " a plate ta ɗora ruwan ta kaiwa Rumaisa ,dukda bata jin ƙishi amma haka ta fasa ruwan ta ɗan sha saboda kartaji wani iri ,ajiye ruwan tayi tana kallon Ameerah da ke yiwa Auta magana " ashe bakiji daɗi ba ,kwana biyu bamu ganki ba ,shine muka tambayi uwar ɗakin ki gidanku ashe ma batasani ba se yaya ne ya kawo mu " yaya? Meerah ta tambaya cikeda mamaki "murmushi Rumaisa tayi tace " nima bansan ya akayi shi yasan gidan ba nayi tunanin ko yana zuwa zance ne" ta faɗa da sigar zolaya
Zare ido Meerah tayi tace" wane zance kuma ,rufamin asiri dan Allah ,idan ma zeje zance kinsan badai a irin unguwar nan ba ,nima tun ranar da nadawo nake fama da ciwon kai ,da safe har na shirya na taho se ga zazzaɓi ya rufeni seda nasha allura ,amma Alhmdulilah naji sauƙi dama gobe nike shirin dawowa " ayya sannu har kin faɗa kuwa ,amma Ameerah wannan da nagani shi zaki aura? Noce kai tayi bata ce komai ba ,dan haka Rumaisa taci gaba da faɗin " gaskiya kam nayi miki murna da ganin sa yana sonki sosai , sedai zan so ace karatu kikayi ba aure ba cox u'r teenager fa har yanzu under age kike ,dudu du baxaki fi 15-16 ba idan kikayi karatu zeyi miki amfani a rayuwa " hmmm Aunty Rumaisa kenan , bakisan wace ce Ameerah shiyasa kike wannan tunanin yarinyar da saboda rashi take zuwa aiki a gidanku ina kike tunanin zan samu damar karatu ,wannan tunanin se ku da kuke da gata kukeyin sa mukam ai bama wani kallon karatu" dukda haka dai Meerah gidanku bakuda irin raunin nan da xakice haka dube ku ba ,kamar baku cikin wani hali ,ni wlh se nake ganin ma sam babu wani wahala a tattare dake ,Ameerah kina kallon kanki kuwa ,duk inda wata mace me gata ke kaiwa kin kai koma nace kin zarta ,ni idan har zaki yarda zan temake ki kiyi karatu ,kinga yanzu Sis Rufee aure zatayi ,Kuma da tayi aure shikennan sedai mamanta ta tafi dake garin da take zama kici gaba da aiki a can ,me ze hana ,ki ajiye aikin tun yanzu Kinga ni kuma zanyiwa Yaya magana nasan ze temaka mana kici gaba da zuwa school "

Shiru Meerah tayi dan bata san me zata ce ba kuma ,saboda Rumaisa bata san cewar bawai iya aiki yakawo ta gidan ba ,amma a fili se tace " Masha'Allah ashe aure zatayi to Allah ya sanya Alkhairi "to baki tambayi wa zata aura ba " Aunty to miye nawa na tambayar wanda zata aura ,tunda dai aikine kawai nakeyi mata maganar arziki ma baya haɗamu " taɓe baki Rumaisa tayi tace " wai yayan mu zata aura " yayanku? yayanku fa kika ce dama mutum yana auren yayan sa ne? Se lokacin Rumaisa ta tuna Meerah bata san komai game da gidan su ba se kawai tace " kinsan yaya Mu'aisam cousin brothern mu ne ba Abba bane ya haifesa "ohhhh na fahimta to Allah yabasu zaman lafiya aikam sun dace ita jin kai shi izza" dariya Rumaisa tayi tace" yayan namu ne me izza"
"ohhhh yi haƙuri Aunty mantawa nayi" dariya Rumaisa tayi tace" idan kika faɗa a gaban sis Rufee,aikam zakisha tijara ,kinsan dai halinta ,kinga tare da yaya fa muke yana mota bara mu tafi karya mun shanyan shi ,amma bamu gaisa da Mama ba ko bata nan? Ohhhh yi haƙuri na manta ne wlh ,bara na kira ta ,har ta miƙe zata kira Aunty se gata ta shigo da fari'arta suka gaisa, sannan suka tashi dan tafiya Meerah ta bisu domin ta rakasu
Har bakin mota ta kaisu da alama lokacin Rufee suna faɗa ne da Mu'aisam ,akan kawota da yayi ya jiye a Wannan unguwar ,ganin Rumaisa da Meerah ne yasakata yin shiru ,a mamakin Mu'aisam ko kallon inda suke Meerah batayi ba bare ma yasamu gaisuwa ,shima se yayi kamar be ganta ba yacewa Rumaisa " shigo mutafi dan naga alamar wacce kikazo ganin ma lafiyar ta ƙalau ,sakarci ne yahanata zuwa aikin ta "kai Yaya Allah tayi rashin lafiya ne "seda ya kalli Meerah ta ƙasan ido kafin yace " amma zata iya fitowa wurin samarin ta aikine bazata iya zuwa ba ko?".

"tsaki Rufee ta ja tace" kaima yaya dai akwai ka da shiga abinda be ganoka ba ,to miye amfanin ta idan bata kula mazan ba ba karatu takeyi ba ba kuma kuɗin karatun ne dasu ba ,sedai nayi mamakin ganin wanda yazo wurin ta ,yayan ƙawata ne kuma babban mutum ne ,matar shi ta haɗa komai ga wayewa dan bama a ƙasar nan tayi karatu ba ,bansan me yake yi a Wannan unguwar ba koda ance dama haka yaran talakawan nan suke ,idan sukaga suna ɗan da hasken fata se su fara bibiyar mazan da suka fi ƙarfin su ,kasan dai babu abin da wannan zeyi da ita seko idan lalata sukeyi dan ta samu kuɗi kasan mutumin banza sam ba ya raina mace duk cunkushewar ta ,Allah dai ya kyauta " tun da tafara maganar cikin su kowa yayi shiru dan sam basuji daɗin cin fuskar da tayi ba , musamman Mu'aisam da yake ganin kamar shine sanadi tunda shine ya ɗauko zancen ,a mamakin su se sukaga Meerah tayi murmushi cikin sanyin muryarta tace " wai dama Hajia tare kuka zo ni ai sam banma ganki ba seda kikayi magana ,na tayaki murna ashe aure zakiyi Allah ya sanya Alkhairi" tafaɗa tana miƙa mata hannu ,wani irin kallo Rufee tayi mata ,ganin haka se ta janye hannun ta tace" au yi haƙuri fa na manta ni talaka ce amma duda haka yakamata mufara gaisawa tunda nan da wani ɗan lokaci na zama matar me kuɗin nima ko da inata wasa da dama na dan bansan matsayin wanda zan aura ba se ga zuwan ki ya wayar min da kai ashe babban mutum ne ,kinsan dama mu yaran talakawa irin su muke nema ko zamu ɗanɗana irin rayuwar da kukeyi ,gaskiya na gode Allah da yayi ni farar mace ,dan na fahimci yanzu kamar mune zaɓin mazan yanzu, gashi zan auri me kuɗi saboda hasken fatar kai Alhmdulilah dama iyayena sun daɗe suna faɗa min cewar ni matar manya ce dan ni ɗin kyakkawa ce ban yarda da hakan ba se da kema kika faɗa da bakin ki ,dan na kula kamar tsoron kyan nan nawa kikeyi saboda duk lokacin da zakiyi magana se kin ambacesa , shikenan Nagode da ziyara nakuma ji daɗin zuwa dubani da kikayi ,kigaishe da Hajia dan Allah kinsan yanzu ita zan cigaba da yiwa aiki
Chapter 26 · 0% Book details