Sashe 22
Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar Suna kam anyi bidiri wanda daga ƙarshe Saudah rufe party ɗin ta tayi ,dan taso barin gidan ne seda Alh Yusuf ya tabbatar mata da matuƙar tafita to kar ta dawo masa gida kuma duk inda zataje karta fitar masa da yaran shi ,dan haka ma da kanshi yayiwa Nanny magana tayi musu wanka aka shirya su ,ya tafi dasu sashen Ammi ,ya kaisu ga dangi dan suma a san su ,dan yanajin tsegumin da sukeyi akan Saudah.
Macen kirki ce za'a ce iyaye da ƴan uwan mijinta sun zo amma ta kasa zuwa ta gaishesu tsawon sati ɗaya,ga ko da wasa basuga ta shigo yiwa abokiyar zamanta Barka ba ,lallai kam sun tabbatar da Yusuf yayi auren bariki dama kaɗawa ba kunyane da su ba ,da yasan yana son ƙarin aure ai da se ya koma gida ya auro kamar dai yanda yayi auren fari "ire-iren maganganun da sukeyi kenan ,wanda shi kansa yasan Saudah bata kyauta ba sedai shi mutum ne da baya damuwa da abinda be ahafeshi ba a ganinsa ba dole se tayi mu'amala da dangin sa ba tunda shi take aure ba su ba , sedai baƙinciki da ta nuna akan samun Rumaisa ne abun ya tsaya masa arai.
Kwana biyu da gana suna ,kowa yakama gaban sa ,gidan ya dawo kamar ba'a taɓa taro ba ,da Abba ze koma aiki yace ze nemowa Ammi Yar'aikin da zata riƙa tayata saboda yanzu abubuwan ze yi mata yawa ga raino ga kula da gida ,sedai fir taƙi yarda saboda ita sam bata da ra'ayin masu aiki a gidan ta ,tafiso takula da yaranta dan samun shaƙuwa da soyayya ,abinci kuma bazata ci na masu aiki ba , sharane se mofin dama Mu'aisam keyi mata ,to saboda haka bataga dalilin tara mata a gidan ta ba ,da wanna taci gaba da kula da yaranta
kwanan ta 40 da haihuwa itama Ummah ta haihu ta sake haifar mace ta ci suna Amrah , bayan tayi 40 suka shirya itada Ammi da yaransu suka tafi ɗakin gari ,wanda shine zuwan Ammi na farko tun bayan barin ta garin.
Haka rayuwar sa taci gaba ,tsakanin ta da Saudah se ido ,idan kuwa magana ta haɗa su to Khadijah ce ta shigo sashen Ammi shine fa Saudah zata biyota tayita zaginta, kuma baze hana anjima yarinyar ta sake shigowa ba ,saboda tana son Rumaisa idan ta shigo haka take zama tace Ammi ta goya mata ƙanwarta ,ita kuma Ammi ta goya mata ,kuma duk jarabar da Saudah xatayi baze hanata kula Khadijah idan ta shigo ba ,a cewar ta ita takawo kanta ba itace ta kira ta ba .
shekarar Rumaisa 7 ,lokacin ita Rufaidah tana cikin na 9 amma cikinsu babu wacce ta sake yin ko ɓarin ciki ,kuma hakan yayiwa Saudah daɗi dan tana tsoron ace Ammi ce zata haifi na miji ba ita ba ,gashi itakuma ba son haihuwar takeyi ba ,dan yanzu ma rabonta da wani muaamalar aure ya haɗa ta da Alh har ta manta dan kuwa baya gabanta a cewar ta ,tana samun fiye da abinda zata samu a wurin sa ga kuma kudi da suke shigo ta ,to miye matsalar ta bayan wanann ?
Sedai abinda bata sani ba ita kam Ammi tana ɗauke da ciki har na tsawon 3 months ,wannan karon kam da wuri Saudah ta falga dan babu lefi cikin yazo mata da laulayi ba kamar na Rumaisa ba ,iya tashin hankali ta shige shi ,tana shirye shiryen yadda zata barar da cikin ,wata ƙawarta ta gayyace ta biki Niger , wanda zuwan ta Niger ya kara sauya mata rayuwa dan ta haɗu da manyan mata masu ji da kuɗi ,anan take koka musu halin da take ciki na kishiyar ta tana da ciki kuma tana tsoron ta haife namiji " ke miye naki idan ta haife namijin? Yanzu fa andena dogoro da dukiyar namiji dan ba ƙaramin raini hakan yake janyo wa ba ,tashi zakiyi kinemi naki, idan kinso ma har shi mijin se kin fishi kuɗi" anan suka dorata a seti ,se ta watsar da zancen cikin
Bayan wata 7 Ammi ta haihu wannan karon ma macecen ce ,taci sunan Mahaifiyar Abba Mariya suke kiranta Mimi.
Wannan karon Ammi bata wani daɗe ba dan Mimi tanada shekara 2 ta samu ciki ,ta haife twins Mace da Namiji ,wanann karon kam Alh Yusuf yayi bikin da be taɓa yi ba ,hakika jahar Kaduna sun sanda samun magaji da yayi anyi shagali an kashe kuɗi
Saudah ta kasa ɓoye bakin cikinta, wanda har se da tayi wa Abba kuka ,shi kuma se yazata ko dan saboda haihuwar ta da ta tsaya ne shiyasa ya tausaya mata ,tare da tambayar ta ta faɗi duk abinda take so shikuma ze mallaka mata.
Haka rayuwar gidan ta ci gaba ,wanda a lokacin Mu'aisam har ya kammala bautar kasar sa ,sedai be fara aiki ba ,tukuna
Indai Mu'aisam yana gida to zaka sameshi tare da twins kamar ma yafison su a duk yaran gidan ,ga biyayya da soyyaya da yake nunawa Ammi bazaka taɓa cewa ba ita ce ta haife sa ba ,haka yaran suna matukar girma mashi , twins na da wata 5 Allah yayiwa mijin Umma rasuwa ,wannan matuwar kam ta girgizasu matuka ,bayan anyi sakan 7 Abba yanemi Umma ta dawo gidan sa da zama amma se ta ki amin cewa ,daga lokacin ya ɗauki nauyin ta da yaranta shine ci da shansu da karatun su
lokacin da za'ayi wa kannen Mu'aisam aure ma duk abinda uba keyiwa yaransa shi yayi musu ,daga waje yayi musu ordern kaya , kasancewar dangin Babansu bawani ƙarfi ne dasu ba.
sam Khadija bata jin daɗin halin da mahaifiyar ta keyiwa Ammi ,gashi ita sam ba zama take tare dasu ba ,dan haka ko yaushe indai tana gida to tana sashen Ammi ,shiyasa su Rumaisa suka shaƙu da ita sosai dan tana son su ita kam ,ba kamar Rufaidah da tun tana karama halin uwarta ya bayyana a gareta ba sam bata da kunya ga shegen tsiwar tsiya Mu'aisam ne kawai take shakka a gidan ,shima saboda baya sake mata da ne ,ganin yadda yakeyiwa Rumaisa ,se itama tafara natsuwa idan ta ganshi da sauri zata gaida shi ,tun yana zaginta da me baƙin hali har ya dena bayan Ammi tayi masa faɗa tare da nuna masa ,yadena nuna mata wariya ,dan ko yaki ko yaso dai shiɗin yayanta ne ,daƙƴar yayi yaki da zuciyar sa ,har ya fara shiri da ita se daga baya ya fahimci tana da sauƙin kai kawai matsalar girma kai ne da aka tusa mata shi tun batasan wace ce ita ba
Comments and share
Real Bazamfaria ce ❤️
*INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION*
( *On* *word* *together* )
*MABARACIYA*
*Story* *and* *writing*
*By*
*FIDDAUSI* *SANI*
(damsel feedorh)
🅿️:2️⃣3️⃣
"Ammi tunanin me kikeyi haka ,kardai saboda wannan haɗin ne kika shiga damuwa?".
Dogon Nunfashi ta ja tana sauke ajiyar zuciya" ko ɗaya Mu'aisam , meyasa zan damu dan Alh yanuna ikon sa akan ka ,karka manta Rufaidah itama yatace ,dan kuwa jinin Alh ce , sedai fin karfin da yanuna ne ya taɓa zuciyata kuma na ta bbata saboda yasan bani ce na haife ka ba shi yasa yayi haka" haba Ammi dan Allah kidena faɗar hakan haihuwa ta ce kawai bakiyi ba ,amma wahalar da kikayi dani na tabbata ko kece kika haifeni iyaka kenan ,akaina menene ba'ayi miki ba a gidan nan kuma duk kika danne ,bantaɓa jin cewar bakece Mahaifiyata ba ,dan kin nuna min soyayyar da baki nunawa waƴanda kika haifa Ammi a lokacin da kika samu Rumaisa nayi tunanin zaki sassauta daga kaunar da kikeyimin amma se ma karuwa yayi ,Ammi kinsan ina sane da lokacin da Hajia saudah tayi makircin ta har ta hana Abba biyamin kudin school ,da kikayi magana lefin ya shafeki har yayi iƙirarin saki akan ki ,ke ce wacce kikaci gaba da ɗaukar dawainiyata da kuɗin ki da kuma ƙarfin ki ,a lokacin na sake tabbatar da kaunarki gareni ,naso nabar gidan nan tun a wancen lokacin dan kuwa har gida natafi amma se Umma tayi min tunin abinda namanta itace ta faɗa min cewar idan har nabar gidan nan to ke nayiwa butulci ba kowa ba ,kuma maƙiyanki zasuji daɗi ,nima na tabbatar da hakan shiyasa na dawo gareki ,Ammi ina zaune a gidan ne saboda ke da ke nayi sabon da banyi shi da wacce ta haifeni ba ,inayi miki so irin na ɗa da uwa ,taya zanjuya wa wacce ta sadaukar da komai nata saboda ni ,Ammi karki manta kece nan kika sakani fara kula Rufaidah ,har nafarajin ta kamar yadda nake jin yayarta Khadijah, wlh ban taɓa jin inayi mata wani so da ban ba kuma bana tunanin zan iya zama da ita a natsayin mata , musamman yanzu da na fahimci cewar ba ita bace zaɓin ki ,shirun da kikaji nayiwa Abba ,kece kika dorani akan hakan kin haneni dayin musu ga manya tun bansan amfanin hakan ba ,yanzu ma naji tsoron namusa masa ne ranki ya ɓaci shiyasa nayi shiru ,dan Allah Ammi karki saka damuwa a ranki ,dan kuwa koda ina son Rufaidah kikace batayi miki ba wlh zan canja ,bare ma bana son ta ,kinsani Ammi ni mutum ne me son ya auri macen da zata darajaki da kuma ni kaina ,kuma matuƙar na aureta hakan baze samu ba ,sam tarbiyyarta beyi min ba Ammi ,naga amfanin auren mace ta gari tun akanki irin yadda kikeyiwa Abba biyaya ,dan haka nima kiyi min addu'a Insha'Allah zaɓin Alkhairi ze zo ,dan Rufaidah ba Alkhairi bace a gareni".
Macen kirki ce za'a ce iyaye da ƴan uwan mijinta sun zo amma ta kasa zuwa ta gaishesu tsawon sati ɗaya,ga ko da wasa basuga ta shigo yiwa abokiyar zamanta Barka ba ,lallai kam sun tabbatar da Yusuf yayi auren bariki dama kaɗawa ba kunyane da su ba ,da yasan yana son ƙarin aure ai da se ya koma gida ya auro kamar dai yanda yayi auren fari "ire-iren maganganun da sukeyi kenan ,wanda shi kansa yasan Saudah bata kyauta ba sedai shi mutum ne da baya damuwa da abinda be ahafeshi ba a ganinsa ba dole se tayi mu'amala da dangin sa ba tunda shi take aure ba su ba , sedai baƙinciki da ta nuna akan samun Rumaisa ne abun ya tsaya masa arai.
Kwana biyu da gana suna ,kowa yakama gaban sa ,gidan ya dawo kamar ba'a taɓa taro ba ,da Abba ze koma aiki yace ze nemowa Ammi Yar'aikin da zata riƙa tayata saboda yanzu abubuwan ze yi mata yawa ga raino ga kula da gida ,sedai fir taƙi yarda saboda ita sam bata da ra'ayin masu aiki a gidan ta ,tafiso takula da yaranta dan samun shaƙuwa da soyayya ,abinci kuma bazata ci na masu aiki ba , sharane se mofin dama Mu'aisam keyi mata ,to saboda haka bataga dalilin tara mata a gidan ta ba ,da wanna taci gaba da kula da yaranta
kwanan ta 40 da haihuwa itama Ummah ta haihu ta sake haifar mace ta ci suna Amrah , bayan tayi 40 suka shirya itada Ammi da yaransu suka tafi ɗakin gari ,wanda shine zuwan Ammi na farko tun bayan barin ta garin.
Haka rayuwar sa taci gaba ,tsakanin ta da Saudah se ido ,idan kuwa magana ta haɗa su to Khadijah ce ta shigo sashen Ammi shine fa Saudah zata biyota tayita zaginta, kuma baze hana anjima yarinyar ta sake shigowa ba ,saboda tana son Rumaisa idan ta shigo haka take zama tace Ammi ta goya mata ƙanwarta ,ita kuma Ammi ta goya mata ,kuma duk jarabar da Saudah xatayi baze hanata kula Khadijah idan ta shigo ba ,a cewar ta ita takawo kanta ba itace ta kira ta ba .
shekarar Rumaisa 7 ,lokacin ita Rufaidah tana cikin na 9 amma cikinsu babu wacce ta sake yin ko ɓarin ciki ,kuma hakan yayiwa Saudah daɗi dan tana tsoron ace Ammi ce zata haifi na miji ba ita ba ,gashi itakuma ba son haihuwar takeyi ba ,dan yanzu ma rabonta da wani muaamalar aure ya haɗa ta da Alh har ta manta dan kuwa baya gabanta a cewar ta ,tana samun fiye da abinda zata samu a wurin sa ga kuma kudi da suke shigo ta ,to miye matsalar ta bayan wanann ?
Sedai abinda bata sani ba ita kam Ammi tana ɗauke da ciki har na tsawon 3 months ,wannan karon kam da wuri Saudah ta falga dan babu lefi cikin yazo mata da laulayi ba kamar na Rumaisa ba ,iya tashin hankali ta shige shi ,tana shirye shiryen yadda zata barar da cikin ,wata ƙawarta ta gayyace ta biki Niger , wanda zuwan ta Niger ya kara sauya mata rayuwa dan ta haɗu da manyan mata masu ji da kuɗi ,anan take koka musu halin da take ciki na kishiyar ta tana da ciki kuma tana tsoron ta haife namiji " ke miye naki idan ta haife namijin? Yanzu fa andena dogoro da dukiyar namiji dan ba ƙaramin raini hakan yake janyo wa ba ,tashi zakiyi kinemi naki, idan kinso ma har shi mijin se kin fishi kuɗi" anan suka dorata a seti ,se ta watsar da zancen cikin
Bayan wata 7 Ammi ta haihu wannan karon ma macecen ce ,taci sunan Mahaifiyar Abba Mariya suke kiranta Mimi.
Wannan karon Ammi bata wani daɗe ba dan Mimi tanada shekara 2 ta samu ciki ,ta haife twins Mace da Namiji ,wanann karon kam Alh Yusuf yayi bikin da be taɓa yi ba ,hakika jahar Kaduna sun sanda samun magaji da yayi anyi shagali an kashe kuɗi
Saudah ta kasa ɓoye bakin cikinta, wanda har se da tayi wa Abba kuka ,shi kuma se yazata ko dan saboda haihuwar ta da ta tsaya ne shiyasa ya tausaya mata ,tare da tambayar ta ta faɗi duk abinda take so shikuma ze mallaka mata.
Haka rayuwar gidan ta ci gaba ,wanda a lokacin Mu'aisam har ya kammala bautar kasar sa ,sedai be fara aiki ba ,tukuna
Indai Mu'aisam yana gida to zaka sameshi tare da twins kamar ma yafison su a duk yaran gidan ,ga biyayya da soyyaya da yake nunawa Ammi bazaka taɓa cewa ba ita ce ta haife sa ba ,haka yaran suna matukar girma mashi , twins na da wata 5 Allah yayiwa mijin Umma rasuwa ,wannan matuwar kam ta girgizasu matuka ,bayan anyi sakan 7 Abba yanemi Umma ta dawo gidan sa da zama amma se ta ki amin cewa ,daga lokacin ya ɗauki nauyin ta da yaranta shine ci da shansu da karatun su
lokacin da za'ayi wa kannen Mu'aisam aure ma duk abinda uba keyiwa yaransa shi yayi musu ,daga waje yayi musu ordern kaya , kasancewar dangin Babansu bawani ƙarfi ne dasu ba.
sam Khadija bata jin daɗin halin da mahaifiyar ta keyiwa Ammi ,gashi ita sam ba zama take tare dasu ba ,dan haka ko yaushe indai tana gida to tana sashen Ammi ,shiyasa su Rumaisa suka shaƙu da ita sosai dan tana son su ita kam ,ba kamar Rufaidah da tun tana karama halin uwarta ya bayyana a gareta ba sam bata da kunya ga shegen tsiwar tsiya Mu'aisam ne kawai take shakka a gidan ,shima saboda baya sake mata da ne ,ganin yadda yakeyiwa Rumaisa ,se itama tafara natsuwa idan ta ganshi da sauri zata gaida shi ,tun yana zaginta da me baƙin hali har ya dena bayan Ammi tayi masa faɗa tare da nuna masa ,yadena nuna mata wariya ,dan ko yaki ko yaso dai shiɗin yayanta ne ,daƙƴar yayi yaki da zuciyar sa ,har ya fara shiri da ita se daga baya ya fahimci tana da sauƙin kai kawai matsalar girma kai ne da aka tusa mata shi tun batasan wace ce ita ba
Comments and share
Real Bazamfaria ce ❤️
*INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION*
( *On* *word* *together* )
*MABARACIYA*
*Story* *and* *writing*
*By*
*FIDDAUSI* *SANI*
(damsel feedorh)
🅿️:2️⃣3️⃣
"Ammi tunanin me kikeyi haka ,kardai saboda wannan haɗin ne kika shiga damuwa?".
Dogon Nunfashi ta ja tana sauke ajiyar zuciya" ko ɗaya Mu'aisam , meyasa zan damu dan Alh yanuna ikon sa akan ka ,karka manta Rufaidah itama yatace ,dan kuwa jinin Alh ce , sedai fin karfin da yanuna ne ya taɓa zuciyata kuma na ta bbata saboda yasan bani ce na haife ka ba shi yasa yayi haka" haba Ammi dan Allah kidena faɗar hakan haihuwa ta ce kawai bakiyi ba ,amma wahalar da kikayi dani na tabbata ko kece kika haifeni iyaka kenan ,akaina menene ba'ayi miki ba a gidan nan kuma duk kika danne ,bantaɓa jin cewar bakece Mahaifiyata ba ,dan kin nuna min soyayyar da baki nunawa waƴanda kika haifa Ammi a lokacin da kika samu Rumaisa nayi tunanin zaki sassauta daga kaunar da kikeyimin amma se ma karuwa yayi ,Ammi kinsan ina sane da lokacin da Hajia saudah tayi makircin ta har ta hana Abba biyamin kudin school ,da kikayi magana lefin ya shafeki har yayi iƙirarin saki akan ki ,ke ce wacce kikaci gaba da ɗaukar dawainiyata da kuɗin ki da kuma ƙarfin ki ,a lokacin na sake tabbatar da kaunarki gareni ,naso nabar gidan nan tun a wancen lokacin dan kuwa har gida natafi amma se Umma tayi min tunin abinda namanta itace ta faɗa min cewar idan har nabar gidan nan to ke nayiwa butulci ba kowa ba ,kuma maƙiyanki zasuji daɗi ,nima na tabbatar da hakan shiyasa na dawo gareki ,Ammi ina zaune a gidan ne saboda ke da ke nayi sabon da banyi shi da wacce ta haifeni ba ,inayi miki so irin na ɗa da uwa ,taya zanjuya wa wacce ta sadaukar da komai nata saboda ni ,Ammi karki manta kece nan kika sakani fara kula Rufaidah ,har nafarajin ta kamar yadda nake jin yayarta Khadijah, wlh ban taɓa jin inayi mata wani so da ban ba kuma bana tunanin zan iya zama da ita a natsayin mata , musamman yanzu da na fahimci cewar ba ita bace zaɓin ki ,shirun da kikaji nayiwa Abba ,kece kika dorani akan hakan kin haneni dayin musu ga manya tun bansan amfanin hakan ba ,yanzu ma naji tsoron namusa masa ne ranki ya ɓaci shiyasa nayi shiru ,dan Allah Ammi karki saka damuwa a ranki ,dan kuwa koda ina son Rufaidah kikace batayi miki ba wlh zan canja ,bare ma bana son ta ,kinsani Ammi ni mutum ne me son ya auri macen da zata darajaki da kuma ni kaina ,kuma matuƙar na aureta hakan baze samu ba ,sam tarbiyyarta beyi min ba Ammi ,naga amfanin auren mace ta gari tun akanki irin yadda kikeyiwa Abba biyaya ,dan haka nima kiyi min addu'a Insha'Allah zaɓin Alkhairi ze zo ,dan Rufaidah ba Alkhairi bace a gareni".