← Book details Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 43

Sashe 37

Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

daganan ta wuce ɗakin Mu'aiseen,ba ta sameshi a ɗakin ba sedai motsin ruwa da taji a toilet haka ya tabbatar mata da wanka yakeyi ,ajiyar zuciya ta sauke don hakan yana nufin ya samu sauƙi kenan ,bata daɗe da zama ba ya fito daga wankan " Ammi na bakiyi bacci ba? Murmushi tayi masa " ina zanyi bacci banzo na duba ka ba Mu'aiseen , Alhamdulillah dai da alama jikin da sauƙi" ehhh naji sauki Ammi duk nacin ciwo idan uwar mutum tazo ai dole ya gudu "ya faɗa yana zura jalabiya ,dawo wa yayi inda take ya zauna " Ammi ke kanki hidimar bikin nan duk yasa kinyi wani iri ko da yake rabuwa da ɗa ba wasa ba"dariya tayi tace " ai shiyasa naga shi ɗan har da jinya saboda ze rabu da uwar sa "hmmmm Ammi kenan ni fa dama na dakatar da gyaran gidana , ina tunanin ana zamu zauna gaskiya ,saboda Ni dai bazan ɗauki masu aiki a gida na ba idan ma na ɗauka befi shara da morphing ba to dole ne yarinya indai har zata zauna a ƙarƙashina ta shiga kitchen ta girka min abinci ,dan haka Ammi na ta sabamin ban saba cin abinci masu aiki ba ,kinga idan muka zauna a nan zata koyi aiki a wurinki " kallon sa kawai Ammi keyi har yagama maganar sa kafin tace " to wacce daga cikin su zata zauna anan? Uwar gidan ko amaryar? "Haba Ammi kinfi kowa sanin ita kam na rasa ta rashi na har abada renon banza nayi a zuciyata shiyasa akace arashin tayi akan bar arha ,da tun lokacin da na samo ta na bayyana manufa ta da hakan be faru ba ,shiyasa ma na haƙura da Rufaida wataƙil ita ce Alkhairin da Ubangiji ya zaɓamin" sosai ya baiwa Ammi tausayi lallae ta yarda ba ƙaramin so yakeyiwa yarinyar ba ,murmushi tayi cikin ranta take kitsima irin farincikin da zeyi idan ya san fafutukar da tayi dan tabbatar masa da samun wacce ya daɗe da soyayyar ta ,amma a fili se tace " karka sare haka ,bakasan hukuncin Allah ba ze iya sauya ƙaddara a ko wane lokaci kaidai ka ƙarfafa wa kanka ,kuma ka cire damuwar nan insha'Allah zakayi farin ciki ,jibi iwar haka kana cikin iyalin ka yarona ya girma" rufe ido yayi yana daria ,kamar ba shine mara lafiyar da ke kwance a ɗazu ba ,haka kawai yakejin farin ciki na lulluɓe zuciyar sa ,bayan yasan kamata yayi ace yana cikin damuwa ze rasa abar ƙaunarsa nan da 44hours ,amma yarasa dalilin hakan.

Washe gari da zazzabi me zafi Rumaisa ta tashi ,Amrah tayi² ta sanar mata abunda ke damunta ganin yadda take ta faman kuka ,amma taƙi ma tayi magana ,ganin haka se ta ƙyaleta .

Rana bata ƙarya ,a yau 31/5 Yakama ranar daurin auren mutane shida ,tun safe Dady baya gida yana can wurin hidimar sauke bakin sa duk da tun a daren jiya wasu suka riga suka sauka ,idan kazo layin gidan lallai zaka sheda ana babbar hidma ne duk da ba'a nan ne za'a ɗaura auren ba amma talakawa sun cika layin gidan to sun sani sadaka ne dai se sun zamu a banza ma akayi bare ze aurar da yara har guda biyu dan ba su san da zancen auren Rumaisa ba ,musamman da sukaji ance macen ƴar Hajia Sauda ce me ruwan kudi wacce ta saba jiƙa su da kuɗi a duk lokacin da tazo gari to bare yanzu da zata aurar da ƴarta ,dan haka kowa be bari anbarshi a baya ba ,ƙarfe biyu aka saka ɗaurin auren ,wanda bayan daurin auren ya kammala akwai walima da Alh Abdullahi tsoho ya shirya ta zallar maza kawai ,ƙarfe ɗaya da rabi Dady ya shigo gidan don duba jikin Rumaisa da Umma tayi mishi waya cewa yayi tsanani ,ita dai tana ganin gara a fasa yi mata wannan auren dama ita can bata amince da wannan shawarar ta Ammi ba ,shi kansa hankalin sa ya tashi ganin yadda ƴar tasa ta koma cikin kwana biyu ,sedai da yace za'a fasa auren Rumaisa ta dage akan a ɗaura ita lafiyarta lau kawai dai batada ƙarfin jiki ne ,wannan karon Ammi ɓoyewa tayi tana kuka ,se yanzu take ganin rashin kyautatawar ta ga babbar ƴar ta ,gashi ita tana ƙoƙarin sanya ta farinci ki meyasa batayi tunanin hakan ba ,seda ta sha kukan ta me isa ta wanke fuska ta fito ,kiran da akyiwa Dady ne yasaka shi tashi dan yasan shi ake jira lokaci na ƙurewa za'a ɗaura auren har ya buɗe mota ze fita Sega Rufaida da gudu tana kwala masa kira tundaga nesa ta rugo da gudu se faman ihu take tana fadin "Dady karku ɗaura auren nan wlh na fasa bana son shi idan ka aura min shi wlh se na kashe shi ,ihun da takeyi ne ya janyo hankalin mutane da yawa da suka fara cika gidan bangaren Ammi ,Riketa Umma tayi dan gani tayi kamar ba'a hayyacin ta take ba ,cikin tsawa tace " ke natsu Rufaida waye bakiso? Cikin rawar Murya tace " Mu'aiseen ,idan aka aura min shi kashe shi zanyi in kashe kaina kowa ya huta "innalillahi wa'inna ilaihiraji'un mutanen wurin suka fara maimaita wa "ke kuwa kinsan baki son sa kika bari har se yanzu da babu mafita se ta ɗaura auren zakice kin fasa ? Dady daskarewa yayi yama kasa magana ,ga se kiran wayarsa akeyi ,dan haka be ce komai ba ya bude motar sa sedai tashin motar suka gani ,.

Kama Rufaida Umma tayi zata kaita can sashen su saboda ta fahimci ba'a hayyacin ta take ba ,cikin tsawa Hajia Inno tace " sake ta ta koma ai da kanta ta zo ,turo ta akayi ta isar da saƙon kuma ta isar , Alhamdulillah mu ba'a isa a kunyatamu ,kuwuce muci gaba da sha'anin mu babu fashi ,jikin kowa a sanyaye a koma ciki ,

Karfe biyu daidai ,Alkawarin Ubangiji ya tabbata wani baya auren matar wani ,kamar yadda rabon wani ke kashe wani ,to wannan karon dai Alhamdulillah don kuwa rabon beyi kisa ba sedai ya canja ƙaddarar mutane da yawa ,a lokacin da Mu'aiseen ke tunanin ya rasa a lokacin Allah ya dubi zuciyarsa ya dawo masa da abar son sa cikin sauƙi

An ɗaura auren Mu'aiseen da Ameerah
Mushin da Rumaisa

Auren da ya samu albarkar manyan malamai masu kudi da talakawa

Duk da shi Mu'aiseen be samu halartar daurin auren ba koda ya zo har anshafa fatiha ,kuma kaikaitar idon jama'a yayi ya sulalewar sa ,saboda haka yasan dai an ɗaura masa aure amma be san cewar bada Rufaida bane

Haka Meerah bata san cewar ba Muhsin bane angonta

To se muyi fatan dai samun zaman lafiya a tsakaninsu

Comment and share pls

08039228702

#Real@Bazamfari❤️
*MABARACIYA*

*ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾ'ى*  *ASSɷ* 📚✍*
  _{Onward Together}_

_STORY AND WRITTEN_
                  _BY_
////////////////////////////////////////////////////
*FIDDAUSI SANI* ( _Damsel Feedorh_ )
///////////////////////////////////////////////////

🅿3️⃣4️⃣

Ana shafa fatiha Dady ya ɗaga waya ya kira Ammi tana ɗagawa yace " Alhamdulillah an ɗaura aure se muyi fatan Allah ya sanya Alkhairi ya kuma sa hakan shine Alkhairi a garesu " cikin mutuwar jiki tace Ameen amma Alh ya maganar ita Rufaida ina fatan dai harda ita aka ɗaura" Kinga Hajia zamuyi wannan maganar daga baya ,dama ita ce ta sameni da kukan ta akan na aura mata shi batare da naji ra'ayin sa ba ba zartar da hukunci yanzu kuma a gaban kowa tace bata son sa saboda haka magana ta ƙare yanzu dai ya jikin Rumaisa ɗin fatan dai da sauƙi dan yau ɗin nan zata tafi ɗakin ta "dogon nunfashi Ammi taja tace " tana nan dai yadda kabarta Alh ,amma doctor ya sake rubuta wasu drugs na aika driver ya siyo mata insha'Allah zata samu sauki kafin anjima ni kaina nafiso akaita gidan ta a yau dinnan kamar ko wace mace "
Chapter 37 · 0% Book details