Sashe 28
Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tayi kyau cikin red hijab nata ,kasancewar ta fara ,ga kuma ɗan ramar da fuskarta tayi se hakan yaƙara hasaka mata fuska ,yau dai ta ɗan shafa farar powder da kwalli a idon ta ,sannan ta fito dan yiwa Aunty sallama,anan ta sheda mata komawar da Yaya Labaran xeyi wurin aiki a yau ɗin nan ,dan haka ta shiga tayi masa sallama ,kuɗin acaɓa ya bata ,tayi godiya ta tafi
Tun da ta tun karo gidan taji gabanta yana faɗuwa abinda bata taɓa ji ba kenan ko zuwanta na farko a gidan ,dan haka tafara addu'a cikin zuciyarta har tayi knocking me gadi ya buɗe mata ƙofa ta shiga
su Nawwara da ke shirin shiga Mota za'a kaisu school se ga idon ta ya hango mata Meerah aiko se ta saki murfin mota ,da gudu tazo tana oyoyo Aunty Meerah ,ashe zaki zo ,shafa kanta tayi tana murmushi tace "ba gashi kin gani ba Auta school zakuje ? Ehhh Aunty baki zo min da komai ba? Ayya na manta ne amma next time Insha'Allah zan zo miki da wani abun Kinga kiyi sauri driver yana jiranki karku makara ,ina Nurain? yana motor ,idan nadawo school zan zo wurinki ,ki jirani a falo kinji ,Kinga Mama bazata barni na shigan muku ɗaki ba " to karki damu anan waje ma zan jira dawowar ku ,maza kitafi kiyi karatu da yawa kinji "da murna Nawwara ta koma mota ,ita kuma Meerah ta shige part din uwar gijiyar ta.
da Larai tafara cin karo ,suka gaisa cikin mutun ci kamar yadda suka saba ,tace " lafiya dai Ameerah kwana biyu bakixo aiki ba? "Wlh Aunty yau da gobe ne naɗanyi rashin lafiya ne amma Alhmdulilah naji sauƙi " ayya sannu Allah ya ƙara lafiya " da Ameen ta amsa tana karasawa cikin falon ,da alama mutanen gidan basu tashi ba ,dan haka kawai ta fara gyaran falon ,aikin da ya dauketa lokaci dan yanayin falon ya nuna mata tunda ta tafi ba'a sake gyaransa ba duba da irin ƙurar da falon yayi ,dole ta cire hijab nata ta ninkeshi ta ajiye a kan kujera dan ba taso yayi ƙura.
haka ta zage ta gyarashi tsaf ,cikin ɗan lokaci sega falon yayi ƙar² ,ganin har ta kammala Rufee bata sauko ba hakan yaba ta tabbacin cewar basu tashi daga bacci ba ,dan haka ta tafi wurin flowers ɗin nan da take zama ,ta zauna ,tana shaƙar sanyin wurin ,zaune kawai take amma xuciyarta ta tafi duniyar tunani ,tsayuwar mutum da taji akan ta ne yasakata ɗaya dara-daran idon ta ta sauke cikin nasa ,da sauri ta janye idon ta ɗan ganin irin kallon da yake mata wanda bazata iya cewa ga ko nami bane ,hakan be sashi yafasa kallon ta ba ,kafin ya buɗe baki yace " kinji sauƙi ne da kika zo aiki yau? Ta ƙasan ido ta harareshi ,ta yanda tasan cewar baze iya jinta ba tace " idan banji ba zakagnni ne " sarai ya ji abinda tace dan haka yace " me kika ce? Da sauri ta kalleshi cikin inda-inda tace " am.un.nace naji sauƙi Alhmdulilah " me yasa ke sam baki iya gaida mutane ne? turo baki tayi batace komai ba " banason inyi magana ashareni ko bakiji me nace bane ,ko Hausar ce bakyaji ? Yanzu ma ƙasa kasa tayi magana " aikasan baroro ce taya zanji Hausa "batayi aune ba se jin saukar(Ƙoso) ranƙwashi tayi akan ta ,da sauri ta dafe kan ,tana kallon sa tama kasa magana dan sosai taji zafin ƙoson ba ƙaɗan ba ,harara ya ɓalla mata tare da faɗin " dena kallo na da wannan idon naki kar ki cinyeni ,kefa na kula da irin kallon da kikeyimin a gidan nan ,wlh ki kul dan ni ba sa'an ki bane ,kinsani Matata ma ta isheki " sakin kan da ta dafe tayi tana jan tsaki " kaine kasan dani har kake ganin kamar ina kallon ka ,yalwar ido ne da Allah yayimin ,shiyasa kake ganin haka ,kuma kai kasan wata matar ka ,dakai da ita bandamu daku ba ,nide aikina nakeyi fatana a biyani haƙƙina shikenan ,kuma banyafe cin zallin nan da kayimun ba a banza Allah yasa wani yayiwa Matarka haka " ta faɗa da sauri tana barin wurin dan tsoron kar ya sake mata wani abun.
karo sukaci itada Rufee ,saboda zuwan da tayi da gudu bata duban gabanta ,cikin zafin rai Rufee ta kife ta da mari" ke wace irin Mahaukaciyar yarinya ce a komai se kin nuna hauka da jahilci ,dubi yanda kike tafiya wawuya dake mtsswww" ta ja dogon tsaki zata rabata ta fita ,itama meerah da sauri ta fizgota wannan karon kam murmushin da ta saba yakasa samuwa a fuskarta cikin fushi tace " ni ba Mahaukaciya bace nasan abinda nakeyi ,se ki tambayeni me yasa nashigo nan da gudu ,to macucin yayanku ne yaci zalina ,kawai saboda wata yarinya tazo gidan nan shine taganni ta tambayeni shi wai gunsa tazo nikuma se na tambaye ta wacece ita se take sanar dani wai ita budurwar sa ce shine nafaɗa mata cewar karta sake zuwa gidan nan dan yanada wacce yakeso ze aura kuma a gidan nan kike ,inacikin faɗa mata ne ashe yazo ban sani ba ,shine yafara marina ,yana faɗin shi shine yafaɗamin yana sonki ,itace zaɓinsa ,daga nace zan faɗa Miki shine yabiyoni da gudu ze sake buguna, shine cikin rashin Sa'a mukayi karo ke kuma kika karamin marin" shikenan ngd "ganin yanda hankalin Rufee ya tashi ne yasakata sakin Daria a ɓoye a ranta take furta Alhmdulilah " ai shina na janyo masa jaraba ,dan nasan yau zesha tijara ga wannan wawuyar da yake kira da matar sa ,madadin ranƙwashina da yayi "a fusace Rufee ta fita dan ganin wace shegiyar ce tazo har gidansu da sunan zuwa wurin Mu'aisam........
Comments and share pls
Real Bazamfaria ce ❤️
*INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION*
( *On* *word* *together* )
*MABARACIYA*
*Story* *and* *writing*
*By*
*FIDDAUSI* *SANI*
(damsel feedorh)
🅿️:2️⃣8️⃣
ganin bata gansa a compound ba se ta nufi sashen su ,lokacin ya fito yanayiwa Ammi sallama ze fita wurin aikin sa ,se shigowar ta suka gani cikin tsananin fushi ,kallo ɗaya yayi mata ,ya ɗauki keys ɗin sa ze fita ganin haka se ta sha gabansa ,cikeda hargowa tace " se ka faɗa min wace yar iskar ce tasamu lasisin zuwa har cikin gidan nan da sunan nemanka ,kuma saboda bakada adalci har kake confessing cewar am not ur choice wlh tayi arxiƙin ban fito na sameta ba da yau nafiso idan na kashe ta nima se a kashe Ni, inaso kasan wani abu Yaya matuƙar ina raye to kowace mace ta haramta a gare ka ,bazan taɓa barinka haɗani kishi da wata ba, idan ma da wannan tunanin a xuciyarka to tun wuri ka Dena dan wlh kaida mata sedai hange.
daga shi har Ammi da kallon mamaki suke binta dan basu san miye dalilin wannan kalaman nata ba
" Ke wai yaushe raini yafara shiga tsakanina dake ,yaushe nafara wasa dake ,ko dan saboda Abba yace na aureki shine ƙwaƙwalwar ki ke gaya miki cewar yanzu daidai kike dani, idan mace 4 nace inaso na aura ke har kin isa ki hanani ,to kisa a ranki cewar auren alfarma ne xanyi miki ,Kinga kuwa dole ki lallaɓani ,kuma zancen wata tazo wurina kar na sake jin wannan a bakin ki dan baxaki zubar min da mutunci a idon iyayena ba dan bansani ba ko aljanunki ne suka nuna miki cewar wata taxo wurina " itama cikin hargowa tace aljanu ka gani a kanku wlh bade ni ba kuma ko aljanu ne dole kai tashafa dan za'a kiraka da mijin me Aljanu ko kana nufin waccen yarinyar bata ganku tare ba ,datayi magana ƙarshe ka mareta ,idan ni karya nayi itama zatayi maka ƙarya ne kome?".
"wai wace yarinya kike magana? Wacce keyimana aiki wa naji kuna kiranta ,itace ta shedamin hakan ,kuma har marinta kayi ,ko ba'ayi haka ba? " wai tana nufin wannan yarinyar abinda taje ta faɗa wa Rufee kenan ,lalllai kuwa itace green snake under green grass, to miye dalilinta na faɗa wa Rufee haka " Mu'aisam wai duk me ya janyo wannan ne wace yarinya ce naji kuna faɗar tazo gunka? Murmushi yayi yace " Ammi yadda kikaji zancen haka naji shi nifa bansan me take nufi ,sedai tayi miki ƙarin bayani ,nikam aiki zan tafi " to shikennan, Mu'aisam Allah yabaka Sa'a a dawo lafiya "ai Rumaisa tanajin haka se ta fashe da kukan baƙin ciki tafara surutai.
" yanzu Ammi kinajin cewar Yaya yafara kawo mata cikin gidan nan ,amma shine bazakice komai ba,ko saboda ba Rumaisa xe aura ba ne na tabbatar idan da kinsan itace ,to da baxaki lamunta ba segashi har kina yi masa addu'a,shin me nayi muku a rayuwa da baku ƙauna ta ,kituna Abba ne yaga dacewar mu nidashi shiyasa ya haɗamu aure ,da kikasan cewar bakison haɗin ai da tun a wurin seki faɗa bawai kiriƙa yi mana bita da ƙulli ba dan na tabbata kina sane da komai " ikon Allah na kwance ya faɗi ,zo zauna Rufaidah,ki faɗa min shin me yake faruwa dan ni sam nakasa fahimtar ku " tsaki ta ja ta ce " ai da kinason kiji meyake faruwa da baki barshi ya tafi ba ,abu ɗaya nakeso kisani ,ko kinƙi ko kin so wlh zan auri Mu'aisam sedai duk wanda ke baƙin ciki ya mutu"
tagama faɗar hakan tare da jan tsaki tana fita daga falon ,girgiza kai Ammi tayi tana faɗin " yanzu irin macen da mu'aisam xe aura kenan ,Allah kazaɓa mana mafi alkhairi
Tun da ta tun karo gidan taji gabanta yana faɗuwa abinda bata taɓa ji ba kenan ko zuwanta na farko a gidan ,dan haka tafara addu'a cikin zuciyarta har tayi knocking me gadi ya buɗe mata ƙofa ta shiga
su Nawwara da ke shirin shiga Mota za'a kaisu school se ga idon ta ya hango mata Meerah aiko se ta saki murfin mota ,da gudu tazo tana oyoyo Aunty Meerah ,ashe zaki zo ,shafa kanta tayi tana murmushi tace "ba gashi kin gani ba Auta school zakuje ? Ehhh Aunty baki zo min da komai ba? Ayya na manta ne amma next time Insha'Allah zan zo miki da wani abun Kinga kiyi sauri driver yana jiranki karku makara ,ina Nurain? yana motor ,idan nadawo school zan zo wurinki ,ki jirani a falo kinji ,Kinga Mama bazata barni na shigan muku ɗaki ba " to karki damu anan waje ma zan jira dawowar ku ,maza kitafi kiyi karatu da yawa kinji "da murna Nawwara ta koma mota ,ita kuma Meerah ta shige part din uwar gijiyar ta.
da Larai tafara cin karo ,suka gaisa cikin mutun ci kamar yadda suka saba ,tace " lafiya dai Ameerah kwana biyu bakixo aiki ba? "Wlh Aunty yau da gobe ne naɗanyi rashin lafiya ne amma Alhmdulilah naji sauƙi " ayya sannu Allah ya ƙara lafiya " da Ameen ta amsa tana karasawa cikin falon ,da alama mutanen gidan basu tashi ba ,dan haka kawai ta fara gyaran falon ,aikin da ya dauketa lokaci dan yanayin falon ya nuna mata tunda ta tafi ba'a sake gyaransa ba duba da irin ƙurar da falon yayi ,dole ta cire hijab nata ta ninkeshi ta ajiye a kan kujera dan ba taso yayi ƙura.
haka ta zage ta gyarashi tsaf ,cikin ɗan lokaci sega falon yayi ƙar² ,ganin har ta kammala Rufee bata sauko ba hakan yaba ta tabbacin cewar basu tashi daga bacci ba ,dan haka ta tafi wurin flowers ɗin nan da take zama ,ta zauna ,tana shaƙar sanyin wurin ,zaune kawai take amma xuciyarta ta tafi duniyar tunani ,tsayuwar mutum da taji akan ta ne yasakata ɗaya dara-daran idon ta ta sauke cikin nasa ,da sauri ta janye idon ta ɗan ganin irin kallon da yake mata wanda bazata iya cewa ga ko nami bane ,hakan be sashi yafasa kallon ta ba ,kafin ya buɗe baki yace " kinji sauƙi ne da kika zo aiki yau? Ta ƙasan ido ta harareshi ,ta yanda tasan cewar baze iya jinta ba tace " idan banji ba zakagnni ne " sarai ya ji abinda tace dan haka yace " me kika ce? Da sauri ta kalleshi cikin inda-inda tace " am.un.nace naji sauƙi Alhmdulilah " me yasa ke sam baki iya gaida mutane ne? turo baki tayi batace komai ba " banason inyi magana ashareni ko bakiji me nace bane ,ko Hausar ce bakyaji ? Yanzu ma ƙasa kasa tayi magana " aikasan baroro ce taya zanji Hausa "batayi aune ba se jin saukar(Ƙoso) ranƙwashi tayi akan ta ,da sauri ta dafe kan ,tana kallon sa tama kasa magana dan sosai taji zafin ƙoson ba ƙaɗan ba ,harara ya ɓalla mata tare da faɗin " dena kallo na da wannan idon naki kar ki cinyeni ,kefa na kula da irin kallon da kikeyimin a gidan nan ,wlh ki kul dan ni ba sa'an ki bane ,kinsani Matata ma ta isheki " sakin kan da ta dafe tayi tana jan tsaki " kaine kasan dani har kake ganin kamar ina kallon ka ,yalwar ido ne da Allah yayimin ,shiyasa kake ganin haka ,kuma kai kasan wata matar ka ,dakai da ita bandamu daku ba ,nide aikina nakeyi fatana a biyani haƙƙina shikenan ,kuma banyafe cin zallin nan da kayimun ba a banza Allah yasa wani yayiwa Matarka haka " ta faɗa da sauri tana barin wurin dan tsoron kar ya sake mata wani abun.
karo sukaci itada Rufee ,saboda zuwan da tayi da gudu bata duban gabanta ,cikin zafin rai Rufee ta kife ta da mari" ke wace irin Mahaukaciyar yarinya ce a komai se kin nuna hauka da jahilci ,dubi yanda kike tafiya wawuya dake mtsswww" ta ja dogon tsaki zata rabata ta fita ,itama meerah da sauri ta fizgota wannan karon kam murmushin da ta saba yakasa samuwa a fuskarta cikin fushi tace " ni ba Mahaukaciya bace nasan abinda nakeyi ,se ki tambayeni me yasa nashigo nan da gudu ,to macucin yayanku ne yaci zalina ,kawai saboda wata yarinya tazo gidan nan shine taganni ta tambayeni shi wai gunsa tazo nikuma se na tambaye ta wacece ita se take sanar dani wai ita budurwar sa ce shine nafaɗa mata cewar karta sake zuwa gidan nan dan yanada wacce yakeso ze aura kuma a gidan nan kike ,inacikin faɗa mata ne ashe yazo ban sani ba ,shine yafara marina ,yana faɗin shi shine yafaɗamin yana sonki ,itace zaɓinsa ,daga nace zan faɗa Miki shine yabiyoni da gudu ze sake buguna, shine cikin rashin Sa'a mukayi karo ke kuma kika karamin marin" shikenan ngd "ganin yanda hankalin Rufee ya tashi ne yasakata sakin Daria a ɓoye a ranta take furta Alhmdulilah " ai shina na janyo masa jaraba ,dan nasan yau zesha tijara ga wannan wawuyar da yake kira da matar sa ,madadin ranƙwashina da yayi "a fusace Rufee ta fita dan ganin wace shegiyar ce tazo har gidansu da sunan zuwa wurin Mu'aisam........
Comments and share pls
Real Bazamfaria ce ❤️
*INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION*
( *On* *word* *together* )
*MABARACIYA*
*Story* *and* *writing*
*By*
*FIDDAUSI* *SANI*
(damsel feedorh)
🅿️:2️⃣8️⃣
ganin bata gansa a compound ba se ta nufi sashen su ,lokacin ya fito yanayiwa Ammi sallama ze fita wurin aikin sa ,se shigowar ta suka gani cikin tsananin fushi ,kallo ɗaya yayi mata ,ya ɗauki keys ɗin sa ze fita ganin haka se ta sha gabansa ,cikeda hargowa tace " se ka faɗa min wace yar iskar ce tasamu lasisin zuwa har cikin gidan nan da sunan nemanka ,kuma saboda bakada adalci har kake confessing cewar am not ur choice wlh tayi arxiƙin ban fito na sameta ba da yau nafiso idan na kashe ta nima se a kashe Ni, inaso kasan wani abu Yaya matuƙar ina raye to kowace mace ta haramta a gare ka ,bazan taɓa barinka haɗani kishi da wata ba, idan ma da wannan tunanin a xuciyarka to tun wuri ka Dena dan wlh kaida mata sedai hange.
daga shi har Ammi da kallon mamaki suke binta dan basu san miye dalilin wannan kalaman nata ba
" Ke wai yaushe raini yafara shiga tsakanina dake ,yaushe nafara wasa dake ,ko dan saboda Abba yace na aureki shine ƙwaƙwalwar ki ke gaya miki cewar yanzu daidai kike dani, idan mace 4 nace inaso na aura ke har kin isa ki hanani ,to kisa a ranki cewar auren alfarma ne xanyi miki ,Kinga kuwa dole ki lallaɓani ,kuma zancen wata tazo wurina kar na sake jin wannan a bakin ki dan baxaki zubar min da mutunci a idon iyayena ba dan bansani ba ko aljanunki ne suka nuna miki cewar wata taxo wurina " itama cikin hargowa tace aljanu ka gani a kanku wlh bade ni ba kuma ko aljanu ne dole kai tashafa dan za'a kiraka da mijin me Aljanu ko kana nufin waccen yarinyar bata ganku tare ba ,datayi magana ƙarshe ka mareta ,idan ni karya nayi itama zatayi maka ƙarya ne kome?".
"wai wace yarinya kike magana? Wacce keyimana aiki wa naji kuna kiranta ,itace ta shedamin hakan ,kuma har marinta kayi ,ko ba'ayi haka ba? " wai tana nufin wannan yarinyar abinda taje ta faɗa wa Rufee kenan ,lalllai kuwa itace green snake under green grass, to miye dalilinta na faɗa wa Rufee haka " Mu'aisam wai duk me ya janyo wannan ne wace yarinya ce naji kuna faɗar tazo gunka? Murmushi yayi yace " Ammi yadda kikaji zancen haka naji shi nifa bansan me take nufi ,sedai tayi miki ƙarin bayani ,nikam aiki zan tafi " to shikennan, Mu'aisam Allah yabaka Sa'a a dawo lafiya "ai Rumaisa tanajin haka se ta fashe da kukan baƙin ciki tafara surutai.
" yanzu Ammi kinajin cewar Yaya yafara kawo mata cikin gidan nan ,amma shine bazakice komai ba,ko saboda ba Rumaisa xe aura ba ne na tabbatar idan da kinsan itace ,to da baxaki lamunta ba segashi har kina yi masa addu'a,shin me nayi muku a rayuwa da baku ƙauna ta ,kituna Abba ne yaga dacewar mu nidashi shiyasa ya haɗamu aure ,da kikasan cewar bakison haɗin ai da tun a wurin seki faɗa bawai kiriƙa yi mana bita da ƙulli ba dan na tabbata kina sane da komai " ikon Allah na kwance ya faɗi ,zo zauna Rufaidah,ki faɗa min shin me yake faruwa dan ni sam nakasa fahimtar ku " tsaki ta ja ta ce " ai da kinason kiji meyake faruwa da baki barshi ya tafi ba ,abu ɗaya nakeso kisani ,ko kinƙi ko kin so wlh zan auri Mu'aisam sedai duk wanda ke baƙin ciki ya mutu"
tagama faɗar hakan tare da jan tsaki tana fita daga falon ,girgiza kai Ammi tayi tana faɗin " yanzu irin macen da mu'aisam xe aura kenan ,Allah kazaɓa mana mafi alkhairi