← Book details Kaddarar Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 29

Sashe 13

Kaddarar Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

      Ba shkurah ba, harta Umma da ta mika mama wayarta sunyi waya da Ammar ɗan Mama da Alhaji Hammayo ya kora sabida yana shaye shaye da ɗauke ɗauke.
Sake wayar mama tayi cike da tsoro suma zubawa shkurah ido sukayi

_Nima zubawa Shkula ido nayi Aunty Ruky ayi min afuwa bansan yanda zan muku kuji daɗi ba wallahi da nayi kaddaranta ce tazo a haka, kunci da bakin ciki sunfi farin ciki da soyayyan cikin rayuwarta yawa_

*Ina yinku*💋
3/4/21, 9:45 AM - Ummi Tandama: *🙆QADDARAN RAYUWATA🙆*
_SHUKRAH_
Mai_Dambu

'''Watan azumin da ya wucce an tambayi Iman Zubairu Madaki, dangane da meye illar koran yaro daga gidan idan yayiwa iyayenshi kuskure, malam yace, illar koran yara daga gida shine, idan kakore shi zaifita yacigaba da abinda ka koreshi akanshi, zai ɓata maka suna, zai kasance yana jin zafinka zai aikata duk abinda yasan ranka zai ɓaci, Uwa uba ta sanadin shi zaka mutu, ko kashiga mugun hali, kuma zai zamewa al'umma fitina dan haka yake jan hankali ga iyayen da suyi hakuri da yaransu Allah yasa mudace'''

       next page zan kawo sauran bayanan.

Al-Muizzu Al-Sammeu Al-Baseer Al-Hakamu👏👏👏👏👏

*Sadeeya Zabura wannan shafin nakine*💋💜

*page 11*

Duk ilahin mutane,wajen shkurah, suka zubawa idanun dan son sanin sahihin gaskiyar abinda Aunty amarya ta faɗa.

         Jikinta rawa ya ɗauka tuni kofin glass ɗin hanunta ya faɗo kasa, sai ja da baya take,
         buga mata tsawa Alhaji Hammayo yayi cike da tashin hankali yace.
"Cikin waye a jikinki *?*"

Wani irin tsoro da firgici ne suka diro mata lokaci guda, durkusawa tayi ta kifa kanta a cinyarta, sannan ta ɗaga hanunwanta ta kare kanta, ciki da tashin hankali.

    Abinda ya farune da ita ya shiga dawo mata,sam bata zata rashin ganin period ɗinta zai yana nufin cikine da ita, fashewa da kuka tayi yana, zuwa ya rufeta da wani irin duka yana yi da hanun yana haɗawa da kafa, duka yake mata, irin wanda za'a yiwa Yaya sadeeq, yana tambayarta ciki waye a jikinta.

          Mama da Ummi ne suka kai mata, ya juya a fusace yace,
"Duk wacce tazo nan, a bakin aurenta." dan dole suka koma baya, umma tana tsaye kanta a sunkuye,  wani irin ciwo da zafin abinda ya faru da shkurah take ji,

      A hankali, tashiga nazarin ciwon da shkurah tayi a matsayinta na me ilimin halayar dan adam wato(Psychology) yaci ace ta karanci shkurah, taya haka ya faru.

Dukan da Alhj hammayo yakewa Shkurah wanda tun tana ihu har tayi shiru, shi ya dawo da Umma daga duniyar tunani cikin zafin, nama tashiga tsakaninsu, ɗaga shkurah tayi wacce hancinta da bakinta ke fida jini, ta rungumota zata shigar da ita cikin part ɗinta, a zafaffe yace.
"Wallahi karki sakata a cikin gidana, dan ba zan zauna da mazinaciya ba, indai karuwanci kika ce zaki jeki na sallamawa duniya ke, kuma kushaida nacire Zainab a cikin y'ayana, kaman yanda kika sani bakin ciki ba zaki ga me kyau ba, Allah ya wadaranki zainab haka zaki dawwama a cikin karuwanci."

Fisgota yayi ya hankadata zai fita da ita waje, duk cikin mutanen gidan aka rasa wanda zai ce masa yayi hakuri.

      rungume hanun umma tayi a kirji tana kallon shi yana hankaɗa Shkurah sai da ya tunkuɗata waje ta faɗi sannan Umma tace.

"Kaman yanda ka fitar da ita daga cikin gidan nan haka kaima, ka tsaya a waje sabida gidan da kake ihun bazata zauna ba a ciki mallakina ne,"

           A razane ya ɗago kanshi yana kallonta cike da mamaki, abinda tai masa, akan shkurah take sauran mutanen suka maida kallonsu kanta. murmushi tayi cike da izza da jin kai, ta karasa gaban Aunty Amarya tana kallonta.

      k'warjini Umma tayi mata, tsoro da shakkar umma suka bayyana a cikin idanunta, wani kasaitacciyar murmushi umma tayi, yanda kuka san jinin sarauta haka takoma tace.
"Mijinki bai taɓa faɗa miki, dukiyar da yake tak'ama da shi mallakina bane, ko ance miki dai dai da wanda yake baki ban sani bane, kin ɗauka na mallake kowa a gidan nan sabida, shine ko ance miki ni irinki ce wacce take zaune sabida abin duniya,"

        juyawa tayi cike da ɓacin rai tace.
"Na baka nan da awa uku, ka haɗa min kan dukiyata, itakuma zan kaita inda zata zauna,"

           ɗakinta ta koma ta ɗauki himar ɗinta da wani babban akwati ta shiga ɗakinsu shkurah ta haɗa kayan shkurah tsab tana kuka, sannan ta ɗauko atm da sabowar wayar da tasa bilal ya ɗauko mata a shagon da yake saida wayoyi idan yana gari.

       Jan jakar tayi tafita da shi, duk mutane kowa na tsaye kaman an shuka dusa, kiran bilal tayi tace.
"ɗauko motar can ka, kaimu Tashan yankari,"

      gefe ɗaya tana, kiran wani layi da wayarta kiran na shiga ta juya fulatanci,can ta maida shi da hausa tace.
" Ga me sunan, Ya goggo nan, zuwa next week idan nagama abinda ke gabana nima zan dawo, gida zan dawo cikinku koda kasheni zakuyi Zaituna, ga Shkurah nan zuwa."

           Bilal yana zuwa,da motar ya fito ya ɗauki a kwatin ya saka a motar, sannan umma ta shiga suka fita tana zaune a gefe yara sun cika inda take sai tattara rigarta take tana ɓoye fuskanta, kaman dai yanda tayi a baya faruwa, abin ciwon haukar ya dawo mata sabo fil, bilal ne yafi dan ya shigo da ita motar ta shiga ja da baya, tana gurnani, umma naganin haka ta kalle shi tace.
"koma mota zan shigo da ita, yanzun,"

     zuwa gurinta tayi cikin rarrashi take mata magana har ta amince tazo tashiga motar suka wucce tasha, inda suka nemi motar da zai tafi yola,  a lokaci nan aka biya kuɗin motar saura pasinja biyu a mota umma ta kalle cikin nutsu tace.
"Nasan duk da yanzun kina cikin wani, hali amma ai zaki iya faɗa min kome, tunda kina iya gane ni."

           Kallon Umma tayi cikin kuka ta rike kanta, tace.
"Shine"

"Mashkur" inji umma.

"A'a" tace,
"toh waye shi ɗin?" inji umma ta jefa mata tambaya,

Kwanciya tayi a jikin umma kin shashekar kuka, tace " umma Maina ne ranar saukarmu....."

       Ba umma kaɗai ba har bilal da yake gaban mota kuka yake, shafa kanta umma tayi sannan tace.
"Da yardan Ubangiji ba za'a sake keta miki haddi ba, babu wanda ya isa ya kusanceki da niyyar zina, zaki kasance cikin kariyar umma ubangiji,anyi na farko anyi na karshe, ba za'a sake ba kinji."

Rarrashinta take, har tayi shiru, sake kiran layi Zaituna tayi, sannan tace.
"Gamu a tasha insha Allah ynz zasu taso don Allah idan taxo ki kaimun ita asibiti, zaituna zan zo, akwai damu don Allah ki kai taga likitan k'wak'walawa don Allah sannan kisa min akanta karta taɓa lafiya cikin jikinta pls ."

        Kashe wayar tayi sannan suka fita sakamakon maganar da aka musu na ansami mutum biu duk matane uwa da y'a wajen matar taje suka gaisa sannan umma tace.
"Yola zaki ko, don Allah ga yarinyata bata da ishshiyar lafiya, ki luran min da ita don Allah na baki amanarta don Allah, ta karshe maganar idanunta cike da k'walla.

     "Insha Allah, zan rike miki ita, har ta isa inda kika turata." inji matar.

Umma tayi ɗan murmushi kafin tace.
"Kuna zuwa tasha, zaku same wacce zata ɗauketa, kanwata zatazo"

                  duk da halin da take ciki, bai hanata kallon Mahaifiyarta ba, cikin kuka tace.
"Umma haihuwa bata da amfani, umma ina jin idan na tafi, ba zan sake dawowa ba, umma ki yafe min saki kuka da nayi, kice baba ya yafe min, Don Allah Umma karki rabu da Baba sabida, ki min alkawarin a kullum zaki min addu'a dukda nasan kinayi," rungumeta umma tayi tana kuka tace.
Nayi miki alkawari, insha Allah zamu sake haɗuwa, kinji ko Shkurahta."

    Sai da aka musu magana sannan suka rabu tashiga mota kallon umma take sosai hawaye na zuba daga idanunta, har suka bar tashan mass.

         Komawa gida umma sukayi tayi parking kayanta baki ɗaya ta ɗauki mukulin ɗaya daga ciki gidajenta tasa bilal ya kwashe mata, zuwa gidanta dake makama new extension sai a lokacin mutane suka shiga bata hakuri koda albarkacin y'aya ta zauna, kuskure ne dai shkurah tayi, bau kyautu ace an rabu ba, ai haka ba daɗi, gashi ana cikin hidiman baki,  duk da me laifi amarya ce, amma tayi hakuri.

Dariya umma tayi sannan tace.
"Da yake dukanta wacece ta dakarta da shi da Mama da Ummi suka nemi dakarta da shi cewa yayi a bakin aurensu,"

      sake kallon matar da tayi maganar tayi tace.
"Shekaru talatin da uku zuwa da huɗu, baya ke kikace, hammayo ya auro me bakar kafa, lokacin da nake zuwa wajenki ki samin abinci sabida cikin jikina cewa kike ba zaki ba yar ba, dan baki sashi ya auro faran mace me farar kafa, ko ba haka ba, da Allah ya buɗa mashi kika ce ya kara aure, dan ba zaku so ya zauna da mace me fara kafa ba, ko ance miki ban san me nake ba yi bane, ki wuce kici arziki iya na yau gobe kuma a kama hanya,"

dakyar umma ta amince ta xauna sai da Hammayo yasa aka shigo da limamin dake sallah a masalacin gidan yayi mata nasiha, sannan ya koma kan Alhaji hammayo sosai yayi masa nasiha me shiga jiki, san yace ya yafewa shkurah wallahi ko shi ya shaida halinta kaddara ce ta faɗa mata, kuma babu wanda ya wucce haka,

             ***
Cikin awa huɗu suka isa, garin gombe, tafiya suke har suka wucce ako, sun nufi kaltingo nan suka samu ana ruwan sama kaman da bakin k'warya sabida karfin ruwan sauka sukayi akan hanya suka, tsaya kafin ruwan ya tsagaita.
Chapter 13 · 0% Book details