← Book details Bintu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 33

Sashe 9

Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"A kanki nake zaune?"
Cikin rashin fahimta ta dubeshi. Bazaka fahimci yanayin da ke a saman fuskartasa ba.
"Yaya bangane ba."
Ya ajiye gwangwanin Maltina bayan ya kur6a.
"Me kika cewa Hafsa?"
Gabanta ya fad'i, ashe yayi musu la6e? Oh, yanzu ya zatayi?
"Ko baki gane ba?"
Ta mik'e tana jijjiga Hanif wanda ke zullo shi a dole sai ta saukeshi.
"Saukeshi."
Ya fad'a, ta saukoshi ta rik'e.
"To ai ni bansan abinda na fad'a ba."
Shiru ya biyo baya, sai kur6ar lemunsa yakeyi yana dubanta rik'e da gudan jininsa. A hankali ya sauke ajiyar zuciya.
"Munyi dake ki nemamin matar aure ne?"
Yanda yayi zancen a sanyaye ya sanya ta d'ago dara-daran idanunta ta dubeshi, wani sassanyar kallo yake yi mata wanda yasa ta jin abinda tun da suke tare bata ta6a jinsa ba. A sannu ta sauke kanta ta maida ga Hanif wanda ke wasa da agogon hannunta.
"Baki ban amsa ba, meya kawomiki tunanin nemamin auren Hafsa?"
Gabanta ya soma fad'uwa ganin yanda yake maganar a sanyaye, ita fa tafi ganewa maganarsa a sama-sama yanda ya saba yi mata magana.
Ta zubawa Hanif ido, tana matukar son yaron. Batasan sadda ta soma fad'in zahirin abinda ke cikin zuciyarta ba.
"Tausayin Hanif nakeji. Kowane yaro yana so ya rayu tare da mahaifiyarsa, saidai Allah baiyi Hanif zai rayu da tasa mahaifiyar ba. Na sha gani yana faruwa a wasu wuraren, mijin yaya ya auri k'anwarta bayan rasuwarta saboda ta kula da 'ya'yan 'yar uwarta. Shine dalilina na yiwa Hafsa maganar. Kayi hakuri dan Allah."
Ta k'arashe cikin rawar murya. Alal hak'ik'a tana tausayin Hanif, har ta sha fad'a a gabansu Mami, ita kam duk radda tayi aure da Hanif zata tafi. Aisha kan tsokaneta, ya zatayi idan Yaya Ma'aruf yayi aure ya damk'awa matarsa Hanif.
"Wallahi idan muguwa ce, labari ya risk'eni ta ta6a lafiyarsa, ke zan biyo gidanki na kwasa muje muyi mata tsinannan duka."
Wannan ne furucinta, har ma ya basu dariya.
A wannan shirun da tayi, a nan ya samu damar nazartarta.
Gaba d'aya bai fahimci kansa ba. A sannu ya kai duba ga yaronsa, bai iya furta komai gareta ba. Can kuma ya samu damar magana.
"Nagode da wannan k'auna da kike nunawa d'ana. Amma ina mai gargad'inki, banaso ki k'ara yiwa Hafsat maganar nan. Daidai da Mami banason yaje kunnenta. Ni Ma'aruf bana tunanin aure yanzu, Asma'u..." Sai kuma ya fasa cewa uffan, ransa na sosuwa a duk lokacin da tunanin Asma'u ya fad'o mishi.
"You can go."
Ta mik'e rungume da Hanif tayi hanyar fita. Ta juyo kad'an ta dubeshi, idanunsa a kanta, tayi azamar d'auke kanta ta fice. Haka kawai ta rasa abinda yasa ta jin tausayin Ma'aruf a karo na biyu bayan rasuwar matarsa.
A farfajiyar gidan sukaci karo da Aisha wacce ta yiwa Hafsa rakiya.
"Ina kika shiga, Hafsa ta tafi."
Ta numfasa, maimakon tayi magana sai kawai ta mik'a mata Hanif tayi gaba. Aisha ta bi bayanta da kallo. Anya kuwa lafiyarta kalau? Ta bi bayanta zuaa d'aki ganin da tayi bata falon.
Ga mamaki, kuka ta tarar tana yi har da sheshshek'a.
"Ke lafiya kuwa? Meyafaru?"
Bata kulata ba, ganin tana niyyar zuwa kiran Mami ya sanya ta dakatar da ita.
"Tsaya, wallahi Yaya ne ya tunamin Anti Ma'u, duk sai ya bani tausayi."
Aisha ta numfasa. Bintu ta labarta mata abinda akayi bayan ta rok'eta alfarmar kada ya je kunnan Mami.
Aisha tayi murmushi.
"Allah Sarki, ai daman za'a sha wuya kafin Yaya ya amince yayi aure. Ashe Abba ma ya yi mishi zancen aure kwanaki, shine dalilin rashin lafiyar da ya yi a satin da ya wuce. Yanzu sai an had'a mishi da addu'a, Allah Ya sanyaya zuciyarsa. Ke nifa banga abin tashin hankali ba, duka-duka ko shekara ba'ayi da rashin Anti Ma'u ba, shima kingani ai Abban shiyasa bai k'ara maganar ba. Hum, wayasani ma ko 'yar gida zamuyi muku."
Ta k'arashe da zolaya. Ai tuni Bintu ta mance da kukanta. A harzuk'e tace.
"Wallahi yanzu zan d'ura miki ashariya, shegiya. Bakinki ya sari d'anyen kashi. Aka had'ani da Yaya Ma'aruf ai an nakasta rayuwata."
Gane inda ta nufa ya sanya Aisha tuntsirewa da dariya. Bintu tayi kwafa.
"Kya yi dariya mana, muguwa kawai. Ke kafin ma ayi wani batun, ko hoto akayimana da shi ai an cuceni. Mutum kamar zabiya, tab. Ai wallahi mata ma kad'ai sun isheni."
Aisha tana dariya ta amsa.
"Kuma bakisan wani abu ba, wallahi har zawrawa sonsa sukeyi. Kodayake ai ke shaida ce. Dubi k'awar Anti Amina, Iklima, da biyu matar nan ke kawowa Hanif ziyara. Mace babba mai shekaru talatin, kusan sa'arsa ce."
Kwafa Bintu tayi. A rayuwa babu wacce tafi jin haushi kamar Anti Iklima. Ta lura wayewarta ya yi over, ga afkin bleaching, har fuskarta tayi tabo. Ita a dole son Yaya Ma'aruf take.
"Ai ita wannan idan batayi hankali ba, wataran sai na koyamata hankali."
"Me zai dameki da ita? Wajenki take zuwa?"
Harararta tayi.
"Yaya Ma'aruf ai yayana ne inace? Shi kansa na kula baya k'aunarta wallahi. Daga ya ganta yakeyin kicin-kicin, ke dole ma na koyamata hankali."
Aisha na murmushi,
"Wai anya babu wata tsakanin..."
Ashar d'in da Bintu ta lailayo ya sanyata yin shiru da azamar rufemata baki tana jan a'uziyya.
"Baki da hankali?" Cewar Aisha.
Ta fisge hannunta.
"'Rainin wayo kai, na gayamiki babu komai tsakanina da Yaya Ma'aruf, sai kawomin k'abli da ba'adi kikeyi. Bar ganin kin fini jiki sai na zauneki na jibgi banza."
Aisha ta ajiye Hanif ta soma k'ok'arin mak'ureta. Ai da gudu ta fice tana dariya, daman sai cika bakin, amma babu k'arfin.
* * *
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<17>>
A kwana a tashi babu wuya wajen Mai Sama,
har gashinan an shiga satin bikin Hafsa da
Bashir. Nan fa Aisha ta zama busy, koyaushe
da ita Hafsa ke shirye-shirye kasancewarta
aminiyarta. Da zarar Aisha ta taso
makaranta, bata yo gida sai can gidansu.
Duk yanda tayi Bintu ta dinga taimakonsu da
wani abin, tace ba ruwanta ita bata kalan
dangi.
Ana gobe za'a soma biki, Aisha ta koma
gidansu Hafsa da zama. Bintu ta k'ek'eshe
tace ba da ita ba, gad'a a mak'ota. Babu
inda zata, dole Aisha ta fice da fushinta. Ko
a jikinta, acewarta babu dangin iya bare na
Baba, zata dai lek'a bikin.
Washegari asabar, misalin goma ba safe,
tana zaune a falo tana karyawa kasancewar
bata jima da tashi ba. Mami na zaune tana
bawa Hanif maganin mura, Ma'aruf yayi
sallama ya shigo. Bintu ta dubeshi, ya gama
had'ewa cikin tsadadden yadi kalar ruwan
toka, hannunsa sanye da agogo ruwan silver
sai zobunan azurfansa biyu a kowane hannu.
Yayi kyau har ya gaji da had'uwa. Ya gaishe
da Mami, ta amsa da murmushi.
"Yau babu baccin safen? Ina zuwa haka?"
Ya gyara zaman hularsa idanunsa akan
Hanif.
"Akwai wani abokina ne bai ji dad'i ba
kwana biyu, shi nakeson lek'awa."
Mami ta gyad'a kai. Sai lokacin Bintu ta
gaisheshi, ya amsa ba tare da ya dubeta ba,
ta ta6e baki. Yanzu mamakinsa takeyi, tun
maganar Hafsa da sukayi, kusan sati da 'yan
kwanaki kenan, ya chanja mata. Bai fiye
shiga harkarta ba, ko meyasa? Bata da
amsar hakan. Maganar Mami ta katseta.
"A'a, ga Bintu ku je tare ka sauketa a gidan
walimar nan tasu."
Hakan yasa ta dubansa, shima ita ya duba
kafin ya dubi Mami fuska a yamutse.
"Ina direban ya shiga ne?"
Mami ta 6ata fuska.
"Ai nasan da zamansa nace kuje tare. Ka
sauketa, yau ba zai zo ba."
Ya dubi Bintu fuska a 6ace sai kuma ya
mik'e.
"Idan ta shirya tayimin magana."
Daga haka ya fice, yana ji Mami nayi mata
maganar tayi sauri. Bintu ta mik'e fuska a
6ace, ita kam bataso aka had'ata tafiya da
Ma'aruf ba.
Ta ci wajen mintuna talatin da wankanta da
shirin. Walimar ba ta anko bace, yini ne na
'yan mata. Don haka ta sanya material
ruwan k'asa, d'inki mai matuk'ar kyau akayi
mata. Ya zauna d'abas a jikinta. Ta murza
d'aurin d'ankwalinta bayan ta kammala fente
fuskarta da kwalliya. Ta feshe jikinta da
turaruka masu sanyin k'amshi don ko kusa
Mami bata barinsu amfani da k'arfaffan
turaruka.
Ta fito, d'akin Mami ta soma shiga tayi mata
sallama, Mami ta bata kud'i ta zura a
jakarta. Saida ta shiga d'akin Hanif ta
sumbaci goshinsa kafin ta fice.
"Kwas, kwas." Take takunta da takalminta
mai d'an tsawo, tana son takalma masu tsayi
duk kuwa da cewar ba gajera bace. A haka
har ta nufi sashen Yaya Ma'aruf.
Ta shiga da sallama, yana kwance saman
kujera idanunsa a lumshe. Ta zuba mishi ido,
kamar wanda aka k'arawa haske da kyau. Ga
sajensa ya kwanta luf-luf. Haka kawai ta
tsinci kanta da dubansa, a sannu ya bud'e
idanunsa suka sauka cikin nata. Da sauri ta
kauda idanunta.
"Na shirya."
Ta fad'a cikin in-ina. Ba shi da niyyar
mik'ewa, saidai bai maida idanunsa ya rufe
ba, ya cigaba da dubanta.
Jin shiru yasa ta jin haushi, ta juya zata bar
d'akin.
"Ki jirani."
Ta bi umarninsa ta tsaya a k'ofar d'akin, ya
fito ya rufe da muk'ulli. Suka jero.
Abba yana zaune a 'yar barandarsa yana
karatun jarida, yayinda Mami ke k'ok'arin
zuba mishi ruwa a kofi. Hankalinsa ya kai
garesu, a gaban idonsa suka jero har
Ma'aruf ya bud'e mota suka shiga. A hankali
yakejin wani tunani yana d'arsuwa a
zuciyarsa. Muryar Mami ta katseshi.
"Abban Aisha, ga ruwan."
Ya numfasa ya kar6a ya sha alokacin da
maigadi ya maida kyauren ya rufe.
Bayan ya kammala sha ya ajiye kofin gami
da duban Matarsa da murmushi d'auke
saman fuskarsa....
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶

      ©Rufaida Omar 
         (July...2016)
Chapter 9 · 0% Book details