Sashe 21
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Tuni ta soma hawaye. Ya saki gashin. Ya kama hanyar fita yana fad'in.
"Ki kammala ki sameni a falo."
Ta tur6une fuska ta bishi da harara.
"Duk abinda ka tanada nima shi na tanada gareka."
Bayan ta kammala wanke komai ta ajiye ta d'auki d'ankwalinta ta d'ora shi tana fad'in, ba zata fasa murza d'aurinta yanda ranta ke so.
Ta share fuskarta, ba fa zatayi saurin karaya ba, yanzu aka fara wasan tsakaninsu tunda bazai gaji da zaluntarta ba.
Ta fito da wannan takunnata mai cike da yanga. A haka ta k'araso cikin falon, idanunsa a kanta yana duban ikon Allah. Ta zauna saman kujera. "Ganinan."
Ya ja fasali sannan ya soma maganarsa.
"Inaso ki kiyaye bakinki. Ki kuma kiyaye dukkan wani abu da zaki janyowa kanki na d'ora hannuna a jikinki. Banason raini, shine kuma babban abinda yafi had'amu kema kinsani. Sannan kina sane cewar Ma'aruf ba k'azami bane ko? Sai ki kiyaye ayyukanki, daidai da d'akina da toilet ban d'agamiki k'afa ba."
Yana murmushi ya d'aga mata gira. "Ai amarya ce, bata buk'atar 'yar aiki yanzu."
Takaici ya isheta, ta dauke idanunta ta turo baki.
"Ni ko a gida fa bana wankin band'aki, Aisha ke yi."
Ya harareta. "Gida daban, gidan aure daban. Banason maimaici. Na gama maganata ok?"
Ta amsa da toh sanin halinsa. Ta mik'e ta bar falon.
Kan gado ta fad'a tana tunanin yanda zata soma rayuwar nan a gidan Ma'aruf.
Bata kai ga tunanin komai ba har ta ji tsayuwar mota. Da sauri ta mik'e ta lek'a. Wani ihun murna ta saki ganin wadanda ke fitowa daga motar. A guje ta fito, bata lura ko da mutum ko babu ba a falon, ita dai burinta ta bud'e k'ofa ta ji ta ajikin 'yan uwanta. Ba zato ta ji an dakamata tsawa wanda ya sanyata juyowa ba shiri.
"Menene hakan?!"
Kafin ta ba shi amsa suka jiyo sallamar mutane tun kafin su k'araso jikin k'ofar. Ta shareshi ta juya ta bud'emusu. 'Yan Rano ne, yanmatansu da iyaye amma duk ciki banda Inna. Da sauri ta rungume Aisha tana murna sai kuma ra fashe da kuka. Wata cikin su, mai suna Gwaggo Sadiya ta kama baki
"Haba kekuwa Bintu, menene abin kukan kuma?"
Ma'aruf na murmushi ya amsa a kunyace.
"Shagwa6ar fa gwaggo?"
Suka k'araso ciki suna dariya. Aisha ta ja hannunta zasuyi d'aki saidai wata gwaggonsu ta dakatar da ita.
"To kekuma haka akeyi? Baki bari ta gaishemu sannan kuyi sirrinku?"
Aisha ta saketa suna dariya. Ta k'arasa ta fad'a jikin gwaggo Sadiya sannan ta gaishesu.
"Bintu da son jiki. Ashe sai abinda yayi gaba."
Ita dai murmushi tayi kawai. Ma'aruf take duba yanda yake wani sunne kai shi a dole kunya ga surukai. Ya dubi Aisha.
"Ke me ya hanaki tafiya makaranta?"
Ta sosa kai.
"To Yaya ai ba wani abun akeyi ba."
Ya harareta.
"Kedai kinzo ki takurawa Amaryata da gulmace gulmacenku."
Akayi dariya, Aisha dariyarta da biyu ce, har da mamaki. Ta dubi Bintu kallon ashe an shirya. Bintu ta murgud'a baki gefe kawai ta watsar. Ta lura wannan ce sabuwar kissar da Ma'aruf ya 6ullo da ita. Tayi kwafa, ai kuwa zata nunamasa ta fishi iyawa.
Ta narke fuska tana mishi wani irin duba.
"Allah Yaya ba wata gulma zamuyi ba, kaima kasan tun jiya nake kukan kewarta."
Bataji kunyar furucinta ba, sai gwaggonnin ne sukaji, 'yan matan kuwa sukayi makwas suna dariya ciki-ciki. Shi kuwa gogan ya maze, lallai ma yarinyar nan, kawai sai ya mik'e a kunyace yana murmushi kamar gaske ya bar wajen bayan ya jefeta da kallon zamu had'u. Ta bishi da murmushin da ta saba idan tayi wata muguntar. A ranta kuwa tace "Yanzu ka soma gani indai irin salon da ka za6a mana kenan."
Bayan fitarsa, yanmatan suka kwashe da dariya, gwaggonnin kuwa mik'ewa sukayi suka zagaya d'akunanta biyu da kicin, daman basu zo ba.
Aisha ta samu ke6ewa da Bintu.
"Gayamin Tawan, ya lamura?"
Bintu tayi murmushi, ai itama tasan me takeyi, ko Aisha bazata bari ta gane komai ba.
"Ke na durzu a hannunsa, ashe daman duk wani jan ajin da yakemin na k'arya ne, ban dauka komai zai wakana ba tsakani."
Aisha ta saki baki.
"To ya na ganki garau?"
Bintu ta ja tsaki.
"Kefa 'yar iska ce, wayagayamiki dole sai na kwanta ciwo? Saida fa ya had'a da kuka da magiya na amince. Ya kuma dauki alk'awarin daina musgunamin."
Aisha dagaske ta yarda, ai sai tayi wata shewa da dariya. Atika ta dubesu.
"Anayi babu mu."
Aisha ta harareta. "Maganarmu ce ta aminan juna."
Bintu tayi dariya kawai. Wannan Aishar ma karatun litattafanta ya tashi a banza.
"Amma da banason fallasa don Allah."
"Tsakaninmu babu haka Bintu, don Allah ki k'ara zage damtse wajen janyo hankalinsa. Ga k'ananun kayanki can acikin akwati da sauran kayayyakin ma, na had'omiki. Kada ki yarda ki ba shi (chance) na k'orafi."
"Naji karki cikani."
Aisha tayi dariya.
"Zan taho miki da books."
Bintu ta harareta. "Sanin kanki ko a gida bana karatun Hausa ballantana a gidan aure."
Aisha ta k'ara numfasawa.
"Wallahi mamaki nakeyi, daman fa na zargi yaya yana sonki kawai yana k'ok'arin 6oyewa ne irin abinnan."
Bintu ta ta6e baki.
"Shiyasani."
Aisha tace "Bawani, kukasani dai, kema ai kina so kike wani sharewa."
Dariya kawai Bintu tayi.
Basu jima sosai ba suka tafi. Bayan tafiyarsu shima ya fice ko sallama baiyi mata ba don dagaske yarinyar ta bashi mamakin furucinta.
Har sukayi sati cikin wannan zama nasu na doya da manja. Ta koma makaranta abinta shima ya koma aikinsa.
A gajiye ta dawo gidan misalin biyar na yamma, bayan sun gaisa da Audu maigadinsu ta shige ciki. Anan farfajiyar gidan ta hangi motarsa a fake. Wannan ya bata tabbacin ya dawo. Ta k'arasa shiga ciki a zatonta ya k'ulle da muk'ulli saidai tana murd'awa ta ji k'ofar a bud'e. Baya falon, wannan ya bata damar zubewa kawai akan doguwar kujera.
"Wash!" Ta fad'a a fili cike da jin wata iriyar gajiya. Ta lumshe ido jin dad'in iskar fankar dake kad'awa. Ta kwashi mintuna kusan uku anan kafin ta mik'e ta k'arasa d'akinta. Ta rage kayan jikinta ta fad'a wanka. Saida ta fito ta shirya cikin riga mai k'aramin hannu T-shirt ja an rubuta Baby a jiki, da wando short bak'i ko gwuiwarta bai k'arasa ba. Wannan karon dai ta samu kitso wajen 'yar wata makwafciyarsu. An yarfa mata su k'ananu. Ta tufke da manyan ribbons biyu bak'i da ja. Hoda kawai ta shafawa fuskarta sannan ta fito zuwa kicin domin d'ora girki. Har lokacin baya falon saidai ta ji muryarsa yana amsa waya daga d'akin. Ta ta6e baki tayi kicin, tasan bazai wuce sauran cocaine ba(Sa'a).
Ta rasa me zata girka, a k'arshe dai ta yanke shawarar yin jellop din taliya. Ta soma aikin ne tana yi tana wak'e-wak'enta ta ji kamar motsin mutum a bayanta. Wannan ya bata damar juyowa ta dubeshi.
Ganin haka ya nufi firij yana k'ok'arin bud'ewa.
"Yaushe kika dawo?"
Ta yi kamar bata ji ba. Ya gama shan ruwansa sannan ya juyo gareta.
"Ban hanaki yawo babu d'ankwali bane?"
Tayi narai-narai da fuska.
"Wallahi Yaya d'ankwalin takura gareshi."
Ya dubeta duban da ace ba matarsa bace bai kamatu ba.
"Nikuma bazan d'auka ba a gidannan, sai ki wuce ki rufe kanki."
Kamar bazata ajiye aikin ba, dole ta ajiye ganin ba shi da niyyar barin wajen. Ta giftashi ta fita. Ya sauke ajiyar zuciya, bai bita da kallo ba, don ba shi da jarumtar nan. Saida ya tabbatar ta shige sannan ya fito ya koma d'akinsa.
Acan d'inma duniyar tunani kawai ya lula, saidai duk yanda zuciyarsa ta kai ga fahimtar da shi wani abu, sam ya k'i aminta balle kuma ya bata dama. Ya ja tsaki ya mik'e, bayason tunanin abinda bazai amfana da shi ba.
* * *
[7/20, 8:05 PM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
"Ki kammala ki sameni a falo."
Ta tur6une fuska ta bishi da harara.
"Duk abinda ka tanada nima shi na tanada gareka."
Bayan ta kammala wanke komai ta ajiye ta d'auki d'ankwalinta ta d'ora shi tana fad'in, ba zata fasa murza d'aurinta yanda ranta ke so.
Ta share fuskarta, ba fa zatayi saurin karaya ba, yanzu aka fara wasan tsakaninsu tunda bazai gaji da zaluntarta ba.
Ta fito da wannan takunnata mai cike da yanga. A haka ta k'araso cikin falon, idanunsa a kanta yana duban ikon Allah. Ta zauna saman kujera. "Ganinan."
Ya ja fasali sannan ya soma maganarsa.
"Inaso ki kiyaye bakinki. Ki kuma kiyaye dukkan wani abu da zaki janyowa kanki na d'ora hannuna a jikinki. Banason raini, shine kuma babban abinda yafi had'amu kema kinsani. Sannan kina sane cewar Ma'aruf ba k'azami bane ko? Sai ki kiyaye ayyukanki, daidai da d'akina da toilet ban d'agamiki k'afa ba."
Yana murmushi ya d'aga mata gira. "Ai amarya ce, bata buk'atar 'yar aiki yanzu."
Takaici ya isheta, ta dauke idanunta ta turo baki.
"Ni ko a gida fa bana wankin band'aki, Aisha ke yi."
Ya harareta. "Gida daban, gidan aure daban. Banason maimaici. Na gama maganata ok?"
Ta amsa da toh sanin halinsa. Ta mik'e ta bar falon.
Kan gado ta fad'a tana tunanin yanda zata soma rayuwar nan a gidan Ma'aruf.
Bata kai ga tunanin komai ba har ta ji tsayuwar mota. Da sauri ta mik'e ta lek'a. Wani ihun murna ta saki ganin wadanda ke fitowa daga motar. A guje ta fito, bata lura ko da mutum ko babu ba a falon, ita dai burinta ta bud'e k'ofa ta ji ta ajikin 'yan uwanta. Ba zato ta ji an dakamata tsawa wanda ya sanyata juyowa ba shiri.
"Menene hakan?!"
Kafin ta ba shi amsa suka jiyo sallamar mutane tun kafin su k'araso jikin k'ofar. Ta shareshi ta juya ta bud'emusu. 'Yan Rano ne, yanmatansu da iyaye amma duk ciki banda Inna. Da sauri ta rungume Aisha tana murna sai kuma ra fashe da kuka. Wata cikin su, mai suna Gwaggo Sadiya ta kama baki
"Haba kekuwa Bintu, menene abin kukan kuma?"
Ma'aruf na murmushi ya amsa a kunyace.
"Shagwa6ar fa gwaggo?"
Suka k'araso ciki suna dariya. Aisha ta ja hannunta zasuyi d'aki saidai wata gwaggonsu ta dakatar da ita.
"To kekuma haka akeyi? Baki bari ta gaishemu sannan kuyi sirrinku?"
Aisha ta saketa suna dariya. Ta k'arasa ta fad'a jikin gwaggo Sadiya sannan ta gaishesu.
"Bintu da son jiki. Ashe sai abinda yayi gaba."
Ita dai murmushi tayi kawai. Ma'aruf take duba yanda yake wani sunne kai shi a dole kunya ga surukai. Ya dubi Aisha.
"Ke me ya hanaki tafiya makaranta?"
Ta sosa kai.
"To Yaya ai ba wani abun akeyi ba."
Ya harareta.
"Kedai kinzo ki takurawa Amaryata da gulmace gulmacenku."
Akayi dariya, Aisha dariyarta da biyu ce, har da mamaki. Ta dubi Bintu kallon ashe an shirya. Bintu ta murgud'a baki gefe kawai ta watsar. Ta lura wannan ce sabuwar kissar da Ma'aruf ya 6ullo da ita. Tayi kwafa, ai kuwa zata nunamasa ta fishi iyawa.
Ta narke fuska tana mishi wani irin duba.
"Allah Yaya ba wata gulma zamuyi ba, kaima kasan tun jiya nake kukan kewarta."
Bataji kunyar furucinta ba, sai gwaggonnin ne sukaji, 'yan matan kuwa sukayi makwas suna dariya ciki-ciki. Shi kuwa gogan ya maze, lallai ma yarinyar nan, kawai sai ya mik'e a kunyace yana murmushi kamar gaske ya bar wajen bayan ya jefeta da kallon zamu had'u. Ta bishi da murmushin da ta saba idan tayi wata muguntar. A ranta kuwa tace "Yanzu ka soma gani indai irin salon da ka za6a mana kenan."
Bayan fitarsa, yanmatan suka kwashe da dariya, gwaggonnin kuwa mik'ewa sukayi suka zagaya d'akunanta biyu da kicin, daman basu zo ba.
Aisha ta samu ke6ewa da Bintu.
"Gayamin Tawan, ya lamura?"
Bintu tayi murmushi, ai itama tasan me takeyi, ko Aisha bazata bari ta gane komai ba.
"Ke na durzu a hannunsa, ashe daman duk wani jan ajin da yakemin na k'arya ne, ban dauka komai zai wakana ba tsakani."
Aisha ta saki baki.
"To ya na ganki garau?"
Bintu ta ja tsaki.
"Kefa 'yar iska ce, wayagayamiki dole sai na kwanta ciwo? Saida fa ya had'a da kuka da magiya na amince. Ya kuma dauki alk'awarin daina musgunamin."
Aisha dagaske ta yarda, ai sai tayi wata shewa da dariya. Atika ta dubesu.
"Anayi babu mu."
Aisha ta harareta. "Maganarmu ce ta aminan juna."
Bintu tayi dariya kawai. Wannan Aishar ma karatun litattafanta ya tashi a banza.
"Amma da banason fallasa don Allah."
"Tsakaninmu babu haka Bintu, don Allah ki k'ara zage damtse wajen janyo hankalinsa. Ga k'ananun kayanki can acikin akwati da sauran kayayyakin ma, na had'omiki. Kada ki yarda ki ba shi (chance) na k'orafi."
"Naji karki cikani."
Aisha tayi dariya.
"Zan taho miki da books."
Bintu ta harareta. "Sanin kanki ko a gida bana karatun Hausa ballantana a gidan aure."
Aisha ta k'ara numfasawa.
"Wallahi mamaki nakeyi, daman fa na zargi yaya yana sonki kawai yana k'ok'arin 6oyewa ne irin abinnan."
Bintu ta ta6e baki.
"Shiyasani."
Aisha tace "Bawani, kukasani dai, kema ai kina so kike wani sharewa."
Dariya kawai Bintu tayi.
Basu jima sosai ba suka tafi. Bayan tafiyarsu shima ya fice ko sallama baiyi mata ba don dagaske yarinyar ta bashi mamakin furucinta.
Har sukayi sati cikin wannan zama nasu na doya da manja. Ta koma makaranta abinta shima ya koma aikinsa.
A gajiye ta dawo gidan misalin biyar na yamma, bayan sun gaisa da Audu maigadinsu ta shige ciki. Anan farfajiyar gidan ta hangi motarsa a fake. Wannan ya bata tabbacin ya dawo. Ta k'arasa shiga ciki a zatonta ya k'ulle da muk'ulli saidai tana murd'awa ta ji k'ofar a bud'e. Baya falon, wannan ya bata damar zubewa kawai akan doguwar kujera.
"Wash!" Ta fad'a a fili cike da jin wata iriyar gajiya. Ta lumshe ido jin dad'in iskar fankar dake kad'awa. Ta kwashi mintuna kusan uku anan kafin ta mik'e ta k'arasa d'akinta. Ta rage kayan jikinta ta fad'a wanka. Saida ta fito ta shirya cikin riga mai k'aramin hannu T-shirt ja an rubuta Baby a jiki, da wando short bak'i ko gwuiwarta bai k'arasa ba. Wannan karon dai ta samu kitso wajen 'yar wata makwafciyarsu. An yarfa mata su k'ananu. Ta tufke da manyan ribbons biyu bak'i da ja. Hoda kawai ta shafawa fuskarta sannan ta fito zuwa kicin domin d'ora girki. Har lokacin baya falon saidai ta ji muryarsa yana amsa waya daga d'akin. Ta ta6e baki tayi kicin, tasan bazai wuce sauran cocaine ba(Sa'a).
Ta rasa me zata girka, a k'arshe dai ta yanke shawarar yin jellop din taliya. Ta soma aikin ne tana yi tana wak'e-wak'enta ta ji kamar motsin mutum a bayanta. Wannan ya bata damar juyowa ta dubeshi.
Ganin haka ya nufi firij yana k'ok'arin bud'ewa.
"Yaushe kika dawo?"
Ta yi kamar bata ji ba. Ya gama shan ruwansa sannan ya juyo gareta.
"Ban hanaki yawo babu d'ankwali bane?"
Tayi narai-narai da fuska.
"Wallahi Yaya d'ankwalin takura gareshi."
Ya dubeta duban da ace ba matarsa bace bai kamatu ba.
"Nikuma bazan d'auka ba a gidannan, sai ki wuce ki rufe kanki."
Kamar bazata ajiye aikin ba, dole ta ajiye ganin ba shi da niyyar barin wajen. Ta giftashi ta fita. Ya sauke ajiyar zuciya, bai bita da kallo ba, don ba shi da jarumtar nan. Saida ya tabbatar ta shige sannan ya fito ya koma d'akinsa.
Acan d'inma duniyar tunani kawai ya lula, saidai duk yanda zuciyarsa ta kai ga fahimtar da shi wani abu, sam ya k'i aminta balle kuma ya bata dama. Ya ja tsaki ya mik'e, bayason tunanin abinda bazai amfana da shi ba.
* * *
[7/20, 8:05 PM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)