← Book details Bintu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 33

Sashe 20

Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

<<30>>
  Zo kaga kuka da turjiya wajen Bintu. Ta rik'e Mami da Aisha gam! Har ta kusa sanya Mami kuka, Aisha kuwa ai ba'a magana. Abokiyar hirarta zata tafi ta barta. Dakyar Mami ta ja ta ta sanyata a mota bayan ta k'ara mata da nasiharta akan ta Abba da mahaifinta.
    Har aka isa gidan kuka kawai takeyi. Haka Bintu tana ji tana gani kowa ya watse ya barta, ko k'awayen amaryar wadanda rabinsu 'yan uwana babu wanda aka bari bisa fad'in Mami.
  Jin shiru yasa ta bud'e idanunta. D'akin Asma'u a baya kenan wanda ya yau yake mallakinta. Anyi fenti mai kyau, kayanta masu tsada. Ta numfasa, jin tsayuwar mota yasa ta mik'ewa da azama ta rufe k'ofar da muk'ulli. A fili ta furta. 
"Naga abokan da zaka tattaro min su cikamin kunne da hayaniya."
  To shima Ma'aruf d'in babu wanda ya janyo rakiya sai Hashim wanda shi ya tilasta masa suka biya siyo KAZAR AMARCI da sauran kayan sha.
  Da sallama suka sanyo kai falon. Daman basu tsammaci ganin kowa ba a falon, don haka Hashim ya nemi wuri ya zauna. Ma'aruf ya harareshi ganin hakan.
"To me kuma kake nema?" Hashim ya sanya dariya.
"Ikon Allah, ka manta bisa al'ada abokan ango ke rakiya suma su tofa nasu addu'ar?"
  Ma'aruf wanda shima ya nemi wajen zama, ya cire hularsa ya yamutse fuska.
  "Look, ka tilastamin mun siyomata tarkace, ba kuma zan d'auki wani sabon abu ba bayan wannan kaji ko? Baruwana da wata al'ada. Malam ka tashi ka je Sally tana jiranka."
   Hashim tun yana d'aukar abin wasa don kuwa a auren Ma'aruf na farko, har Ma'un ya kawo falon idanunta a rufe ya yi musu 'yar nasiha. Ganin haka ya watsar, ya bishi da nasiha daga nan kuma ya mik'e.
  "To ai shikenan, mai yiwuwa kishi ke damunka. Bari na tafi, Allah Ya sanya alheri. A kuma ji tsoron Allah dai. Atoh."
  Wani kallo kawai ya bishi da shi baice uffan ba. Ya mik'e yayi mishi rakiya har wajen motarsa.
  Bintu tana jin dukkan abinda suke fad'a, ta ta6e baki, wai ma? Shi kansa bai isheta kallo ba yanzun balle kuma abokinsa.
   Ta cire laffayarta ta wurga saman gadon. Wani riga da siket na farin leshi d'inkin ya kamata kwarai hakan ya k'ara fiddo zahirin zubin halittarta.
   Ta fisge d'ankwalin, tana k'ok'arin zuge zip din rigar ne ta ji an murd'a k'ofar. Jin ta a k'ulle ya sanyashi soma bugawa a sannu.
  Ta harari k'ofar ta cigaba da abinda ta soma. Shima daga bugu uku bai k'ara ba ya bar wajen, daman ledar zai mik'a mata, haka ya sanyata a firij ya fice zuwa d'akinsa bayan ya kashe fitilu.
  Ita kuwa Bintu ta chanja kayanta zuwa riga da dogon wando ta nemi makwanci. A gajiye take sosai, hakan yasa ko mintuna uku bata ci ba bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
   Asuba nayi kuwa ta farka, wannan kuma sabon su ne, Mami ta sabar musu da tashi sallar asuba. Tana idarwa kuma ta lafke anan saman dardumar sai bacci, abinda ta kasa horuwa da shi kenan, hak'uri har fitowar rana.
   Cikin baccin ne ta ji ana bugun k'ofarta tamkar za'a 6alla. Bintu ba dai nauyin bacci ba. Ta mik'e a firgice. Ga rana har ta fito kyal. Ba shiri ta bud'e k'ofar.
  Ma'aruf ta gani sanye cikin farar jallabiya sai faman huci yakeyi.
  "Wane irin wulak'anci ne haka ina bugun k'ofa bazaki bud'e ba, banda wannan ma, wanene ya baki damar rufe k'ofa?"
Ta turo baki.
"Gani nayi d'akina ne."
Ya watsa mata mugun kallo.
"D'akinki, ni kuma gidana ne. Ki ka k'ara gangancin rufe k'ofa sai na hukuntaki. Ba ki da abinda zan nema."
   Ta dubeshi kawai cike da tsananin 6acin rai dangane da furucinsa. Ta kauda kanta tana mai tunanin abinda ya kamata tayi domin ramuwa. Ya katsemata tunani.
  "Ki kunna wayarki, Mami na son magana da ke. Ki kuma yi sallah, don banga alamun kinyi ba."
  Ya juya ya fice ya barta tsaye kamar an dasa ta. Ta ci alwashin Yaya Ma'aruf sai yayi dana sanin munanan kalamansa gareta. Tayi murmushi mai fassarori.
  "Bintu ce fa." Cewar wani sashe na zuciyarta.
Ta juya ta koma ciki ta rufe d'akinta, saidai bata sanya muk'ulli ba.
Wayarta ta nufa kai tsaye ta kunnata. Kira ta dannawa Mami. Mami tana d'auka kawai sai ta fashemata da kuka.
"Haba Bintu, kukan na menene kuma? Meyafaru?"
Ta ja ajiyar zuciya.
"Mamina kewarku nakeyi wallahi." Ta fad'a a shagwa6ance. Mami tayi murmushi mai sauti.
"Muma munyi kewar Bintuna, saidai dole zamuyi hakuri saboda gidan mijinki shine babban gata da rufin asirinki. Shi kuma kad'ai ne wanda zai nunamiki so tamkar mu ko ince fiye da mu. Kinji ko?"
Bintu ta share hawayenta, lallai ma Mami, batasan abinda ya yi mata ba yanzun. Amma ai bakomai, Inna ta haneta kai k'ara kasafai. Itama ai ba kanwar lasa bace. Shine abinda ta barwa zuciyarta. A fili kuwa ta nunawa Mami ta gamsu, ta hau rok'on a kawomata hanif amma Mami tace ba yanzu ba sai an kwana biyu. Dole ta hak'ura.
Gama wayarsu, ta mik'e ta fad'a wanka. Bayan ta fito ta nufi akwatin da Aisha ta had'omata. Tsaki tayi, Aisha sai a barta, duk ta had'ata da manyan kaya bayan ta sani ko a gida ba damunta sukayi ba. Tayi ta d'age-d'agenta, can dai ta hak'ura ta d'auko wani atamfa ja mai adon fararen fulawoyi manya. Simple d'inki akayi masa na riga da siket saidai ya zauna sosai a jikinta. Ta k'ara fesa turare. Ta dubi kan gadon, kayan da ta cire babu linki, haka ta tattara komai ta linke ta gyara gadon gami da adana kayan sallarta.
Har zata fita falo ta tuno da batun d'ankwali, ba k'aramin aikin Ma'aruf bane ya zubamata rankwashi a kanta, ba don ta so ba ta d'auka, saidai koda ta tashi yin d'aurin batayi na kirki ba, sai wani da ake kira da Ture Kaga Tsiya. D'ankunne kawai ta sanya sai zobunanta, babu sark'a da abin hannu. Fuskar fayau babu kwalliyar kirki, acewarta wa zata yiwa?
Batayi tsammanin ganinsa a falon ba, saidai ga mamakinta yana zaune saman carpet yana karyawa abinsa. Mamaki tayi kwarai, ta shaida kulolin, daga gidan Mami suka fito. Ya dubeta duba na wacce bata isa ba ya kauda kansa fuskarnan tamkar wanda aka aikowa sak'on mutuwa. Shi fa ba'a kyauta mishi ba, ina shi ina Bintu ne? Wannan ta gama ganinsa ai ta cuceshi. Gwara suyita zaman doya da manja.
Ganin irin kallon da yayi mata ne yasa tayi murmushin mugunta. Kicin ta shiga ta d'auko kofi da cokali bayan ta d'aurayesu ta dawo.
Ta zauna d'an nesa da shi ta janyo flask na ruwan shayi fuskarta a sake.
"Wane irin d'an iskan d'auri ne haka kamar wata ka..."
Bai kai ga k'arasawa ba wayarsa ta d'auki k'ara. Saida ta kusan yankewa sannan ya d'aga tare da sanyawa a loudspeaker.
"Hello."
Bintu ta yagi kwai ta tura a baki batare da ta kalleshi ba.
Daga can ita kuma wacce ke akan layi ta fashe da kuka. Kukan da ya sanya Bintu kusan sakin dariya sakamakon wata k'atuwar murya da ta ji marar dad'in sauraro tamkar ba muryar mace ba saidai ta cije.
Shi kansa yayi mamakin jin ta da babbar murya haka, ashe kenan idan zasuyi magana da shi ne kawai take ragewa. Yau kam gayun murya babu shi.
"Prince ka cuceni, ka ci amanar k'auna. Ashe daman aure za'ayi maka da 'yar uwarka shine baka sanardani ba? Na shiga uku."
Sai lokacin Bintu ta gane ko wacece, itace dai wacce ta yi mishi rakiyar dole zance wajenta.
Ma'aruf ya d'an rarrasheta ta kasa shiru har ya gaji, ganin zai kashe wayar dole ta sauko. Yace ta kwantar da hankalinta, shi aure ai nufin Allah ne. A k'arshe kuma tayita rok'onsa akan ya shigo tayi mishi kallon k'arshe don itama zata koma Kaduna wajen yayarta.
Ya tabbatar mata zai shigo. Bayan sunyi sallama ya kwantar da kansa saman kujera ya lumshe ido kawai. Can ya tsinci muryar Bintu.
"Yaya, wallahi wannan matar 'yar yaudara ce. Bakaji muryarta ba? Allah Ya kamata, ranar da na raka ka zance tana ta faman k'ank'ance murya, yanzu kuma dubi yanda ta bud'e murya tana zuba kuka tamkar ana ruwan sama."
Yayi cak, ya kuma gaza bud'e idanunsa, gaba d'aya tunaninsa ya tafi ga matakin da yafi cancanta ya d'auka akanta. Ita kuwa wani sanyin dad'i ne ya dirar mata ganin ta kashe bakinsa. Ta kammala ciye-ciyenta a tsanake ta kora da ruwan shayi kafin ta mik'e ta kai kayan kicin.
Kafin ta kai ga juyowa, ta ji an cakumi gashinta da k'arfi. Ai tuni ta soma ihu.
[7/20, 1:55 PM] ‪+249 99 842 9948‬: ¶°°BINTU°°¶

      ©Rufaida Omar 
         (July...2016)

<<31>>
Tuni d'aurinta ya kunce.
"Wacece mai k'atuwar murya?"
  Ta sanya hannu ta rik'o hannunsa amma k'arfin ba d'aya ba, ko gezau yatsunsa basu motsa ba.
  "Zan mutu! Don Allah kayi hak'uri Yaya."
   "Daga yau kika k'ara kiranta mai k'aton murya ni da ke ne. Ke meye a muryarki?"
  "Wallahi muryata tafi... Wayyo!"
Ta kasa k'arasawa adalilin k'ara jan gashin da ya yi.
  "Au, ashe bakinki bazai mutu ba? Lallai idan zaman da kika za6a kenan muyi zaki d'and'ana kudarki."
Chapter 20 · 0% Book details