Sashe 7
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
<<12>>
Gida Saif yaso su soma nufa, saidai Bintu tace ita kam asibiti ya kamata su je su ga lafiyar baby da mamansa. Inna ta goyi bayanta. Bintu ta bud'e wayarta a lokacin da motarsu ta shigo harabar asibitin. Layin Aisha ta soma nema. Saidai yana ta k'ara ba'a d'aga ba. Ta kira lambar Mami, cikin sa'a ringing uku ana hud'un Mami ta d'aga.
"Mami gamunan a asibitin, a wane 6angare kuke?"
Ta ji shiru kafin ta ji muryar Mami a sanyaye.
"Ku dawo gida mu ma gamunan a hanyar gidan."
Kafin Bintu tayi magana Mami ta katse. Ta dubi wayar da mamaki.
"Ya akayi ne?" Cewar Inna da ke tsaye tana jiran shigarsu. Bintu gaba d'aya jikinta yayi sanyi.
"Bansani ba, wai an sallamesu, tace muje gidan. Mamin ce ta sanyayarmin da jiki, duk muryarta ta chanja."
Inna tayi shiru tana ambaton innalillahi a zuci, tasan ba k'aramin abu ke sanya yayarta shiga wani hali ba. Ta soma kokarin shiga mota.
"Ai sai mu k'arasa."
Suka hau sai gida.
Cikin fad'uwar gaba, suke duban k'ofar gidan ganin motoci fin uku.
"Wannan motocin duk na barkan ne?"
Cewar Bintu.
"Ina tunanin haka."
Baba maigadi ya bud'emusu kyauren suka shiga, anan ta ga su Abba tsaye tare da mahaifin Ma'u wanda ya kasance k'anin Abban, sai sauran 'yan uwansu.
Suka gaisa sannan suka k'arasa ciki, Saifu ya bisu da akwatin Bintu. Gaba d'ayansu jikinsu a sanyaye. Kuka kawai kakeji daga falon Mami. Ai da gudu Bintu ta k'arasa, duk taron jama'ar dake a falon, bata kasa hango Aisha ba. Itama a guje ta k'araso ta rungumeta.
"Munyi rashi Bintu, Anti Ma'u ta rasu."
Ai ji tayi kamar an bugamata guduma a k'irji sakamakon wani bugawa da yayi.
"Ke kina da hankali kuwa? Haka mutuwar take?!!"
Ta fisge jikinta da gudu ta nufi wata 'yar uwar Ma'u da suke uwa d'aya uba d'aya.
"Anti Zainab, ina Anti Ma'u?"
Cikin kuka Zainab ta k'ara jaddada mata lallai babu Asma'u, Asma'u ta rasu."
Kai Bintu ta ga tashin hankali. Da wayonta, batasan mutuwa ba. Kuka takeyi tana tambaya.
"Haka mutuwar take? Innalillahi."
Suna ji suna gani aka tafi da Ma'u makwancinta na gaskiya. Ko ta kan jaririn bata bi ba ballantana ta sanyashi a ido.
Har magrib bata saki ranta ba, babu abinda take tunanowa sai yanda Ma'u ke hak'uri da dukkan abinda take fad'amata duk furucin da ya zo bakinta akan mijinta.
"Allah Sarki, halinki na gari ya biki. Allah Yayi miki rahma. Aisha, ina Yaya Ma'aruf?"
Aisha ta ja majina.
"Yaya Ma'aruf yana asibiti, amma naji Mami tace sunyi waya da Rufa'i, yanzu zasu taho. Shi fa yana ganin an fito da ita bayan an shiryata ya suma. Har zuwa yanzu, bai k'ara sanin inda kansa yake ba sai yanzun. Yaya Ma'aruf ya ji mutuwa Bintu, yana son Anti Ma'u kamar ransa."
Bintu hawayenta suka k'ara zubowa. Ta tunano baya, ta jinjina kai. Ita tasan yana k'aunar Ma'u.
"Ina Bebin?"
"Yana wajen Anti Amina. Ta amince zata shayar da shi, mijinta bai hanata ba."
Tausayinsa ya mamaye Bintu. Ta mik'e ta fito zuwa wajen da Anti Amina take. Saidai ta tabbatar mata yana d'akin Mami yana bacci. Batayi k'as a gwuiwa ba ta nufi d'akin Mami. Can ta hangoshi cikin gadon jarirai yana baccinsa lafiya lau.
Ta bud'e (net) d'in ta rik'o yatsunsa. Yaron sak mahaifinsa, babu abinda ya bari. Hawaye kawai take shatatarwa na tausayinsa. Shikenan ya zama mara uwa. Abin akwai tausayi. K'aunar yaron ya shigeta kwarai. Nan ta kwanta tana dubansa har bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita itama. Don jiya batayi baccin kirki ba sakamakon d'oki da son ganin Ma'u da bebinta da takeyi.
A haka Mami ta shigo ta iskesu.
"Wani abun sai Bintu, kya bud'ewa yaro (net) sauro ya cijeshi?"
Bintu batasan ma tana yi ba. Mami ta gyara mishi rufin net din ta fita.
* * *
Washegari da asuba Bintu ta farka babu yaro a gefenta. Inna ke sanarmata yana can wajen Amina a d'ayan d'akin. Suna cikin haka Mami ta shigo.
"Mami don Allah kada a d'auke baby daga gidannan."
Mami ta sauke ajiyar zuciya jin k'orafin Bintu.
"Shi kansa uban yaron bai amince ba, yace a samo mai shayarwa ko nawa ne zai biyata da dai yaron yayi nisa da shi."
"Haka ma yafi wallahi Mami. Idan ya koma gidan Anti Amina ba zamu k'ara ganinsa ba fa. Kema nasan bazaki so ya bar nan ba."
Mami ta d'auki hijabin sallarta wanda shi ya maidota d'akin daga d'akin Abba.
"Bani da iko, sai abinda Abbanku ya fad'a. Bari dai muga yanda za'ayi."
Daga haka ta fice. Bintu ta fad'a bandaki tana fad'a a fili.
"Banda mutuwa ma, me zai raba d'a da uwarsa? Kai, Allah Ya bamu kyakkyawan k'arshe."
Inna daga saman darduma ta amsa da amin.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<13>>
Bintu bata samu yiwa Yayan nasu gaisuwa ba sai wajejan sha d'aya na safe. Shi d'inma, aikenta Mami tayi akan yazo Abba yanason ganinsa, don gaba d'aya wayoyinsa a kashe suke.
Da sallamarta ta tura k'ofar, ba'a amsa ba. Kansa kawai take iya hangowa kasancewar ya juyawa k'ofar baya, ta tako sannu kad'an yanda take iya hangen fuskarsa. Fuskarsa ruwan hawaye ne kwance yayinda ya zubawa k'aton enlargement na hotonsa da Ma'u tun ma na lokacin da aka d'aura musu aure yana duba. Ta dubi hoton, ma'auratan sun dace matuk'a da juna. A dai fari da kyau, babu na yar wa. Allah Ya basu, kodayake jini d'aya ne.
Tunda take a rayuwa, bata ta6a jin tausayin Yaya Ma'aruf ba sai a wannan karon da Anti Ma'u ta tafi ta barshi. Ga duk wanda ya zauna da Ma'aruf da Asma'u, zai gane irin tsantsar so da kaunar da sukeyiwa juna. A yau ga mutuwa ta yi musu YANKAR K'AUNA. Ta zauna a gefensa, ina ruwan Bintu, maimakon ta rarrashe shi sai kawai ta had'a kai da gwuiwa ta fashe da kukan itama.
Sai a lokacin yayi niyyar motsawa. Ya ji shigowar mutum, saidai bai san ko wanene ba. A yanzu kuwa da ya ji muryarta, ya ganeta.
"Nayi rashin madubi abin dubawa. Na rasa wani 6angare na jikina. Asma'u ta kasance wata fitila mai haskaka rayuwata, har abada bazan daina jin ciwon rashinta ba. Bani da tamkarta, a yanzu kuma bani da tamkar abinda ta haifamin."
Yayi shiru sakamakon hawayen da ya haneshi k'ara magana.
Bintu ta tsaida kukanta ta dubeshi cike da tausayawa.
Kawai sai ta k'ara rushewa da ihun kuka. Ya tsayar da hawayensa ya dubeta a mamakince. Wai daman tana da tausayi har haka? Ikon Allah.
Sallamar Mami da Abba ta katsesu. Itama jin shirun yayi yawa ne ya sanyasu biyo sahu don Abba har ya fito da zummar ganin abokansa da sukazo musu ta'aziyya.
"A'a, menene kuma haka? Ke ba kiranshi nace kiyi ba?"
Bintu ta mik'e tana sharar majina.
"Kuyi hakuri, kuka ya sanyani."
Abba ya girgiza kai sannan ya nufi wajensa ya zauna. Bintu ta fice daga d'akin. Nasiha mai ratsa jiki Abba yayi mishi. A k'arshe Mami ta d'ora sannan Abba ya umarceshi da yin wanka ya kimtsa ya fito amsar gaisuwa. Ya amsa da toh.
Ita kuwa Bintu kan gadonsu ta nufa kai tsaye bayan shigarta d'aki. Ta kwanta ta soma rusa ihun kuka.
"Allah mun tuba, Allah ka ji k'anmu ba don halinmu ba."
Aisha ta amsa da amin.
"Haba ke kuwa, ya dace kibar wannan kukan, duk masoyin Ma'u na hakika kamata yayi ya bita da addu'a koyaushe. Wannan kukan ba abinda zai rage mata."
Bintu ta zauna sannan ta share hawayenta.
"Hakane, Allah Ya jik'an Anti Ma'u."
To a k'arshe dai bayan anyi sadakar bakwai kowa ya watse, lokacin itama Inna ta wuce Rano. Gidan ya zama daga su sai su, sai ko Ma'aruf wanda Abba ya k'i amincewa da komawarsa gidansa adalilinsa na tsoron halin da zai jefa kansa saboda damuwa. Sai kuma Malama Atine wacce ita ke shayar da Hanif, yaron Ma'u.
Babu wanda ba ya ji da Hanif, daidai da 'yan uwan mahaifiyarsa sukan lek'oshi. Da wuya ayi sati batare da wani cikinsu yazo ganinsa ba. Bintu da Aisha kuwa, d'akin da yake nan ne wajen hirarsu tare da Atine muddin basu da karatu.
Tsakanin Bintu da Ma'aruf kuwa, raina mishi wayon da ta saba yi, ta rage sosai ganin yanda shi kansa ya sanyaya.
Saidai bayan watanni biyu ta fahimci ashe lam6o yayi ba wai ya chanja bane. Abinda ya had'asu kuwa shine.
Tana bacci gefen Hanif yaro mai watanni biyu, wanda saboda gata da kulawar da yake samu sai ka rantse d'an watanni hud'u ne. Cikin magagin baccinta ta d'ora mishi hannu a wajen hanci, ai kuwa yaro ya hau numfarfashi, Allah Ya taimaka Ma'aruf yayi sallama ya shigo wanda sam Bintu bata ji ba, Allah Ya yi ta mai nauyin bacci. Atine suna falo suna hira da 'yan aiki. Lokacin k'arfe uku na rana. Babu zato ya kai mata wawan duka a k'afa. Ta mik'e a gigice tana sosawa.
"Tsabar iskanci kashemin yaron zakiyi?! Atine! Atine!!"
Ai da sauri ta yo d'akin. Nan yayita bud'emata wuta. Ya kuma gargad'eta koda wasa kada ta k'ara yarda Bintu tayi bacci a gefen d'ansa.
Bintu ta turo baki tana dubansa. Ya danna mata harara.
"Sai na yanke wannan bakin mai kama da na tsuntsaye. Tashi ki fita kafin na karyaki!"
Ta mik'e cikin fushi ta bar d'akin.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Gida Saif yaso su soma nufa, saidai Bintu tace ita kam asibiti ya kamata su je su ga lafiyar baby da mamansa. Inna ta goyi bayanta. Bintu ta bud'e wayarta a lokacin da motarsu ta shigo harabar asibitin. Layin Aisha ta soma nema. Saidai yana ta k'ara ba'a d'aga ba. Ta kira lambar Mami, cikin sa'a ringing uku ana hud'un Mami ta d'aga.
"Mami gamunan a asibitin, a wane 6angare kuke?"
Ta ji shiru kafin ta ji muryar Mami a sanyaye.
"Ku dawo gida mu ma gamunan a hanyar gidan."
Kafin Bintu tayi magana Mami ta katse. Ta dubi wayar da mamaki.
"Ya akayi ne?" Cewar Inna da ke tsaye tana jiran shigarsu. Bintu gaba d'aya jikinta yayi sanyi.
"Bansani ba, wai an sallamesu, tace muje gidan. Mamin ce ta sanyayarmin da jiki, duk muryarta ta chanja."
Inna tayi shiru tana ambaton innalillahi a zuci, tasan ba k'aramin abu ke sanya yayarta shiga wani hali ba. Ta soma kokarin shiga mota.
"Ai sai mu k'arasa."
Suka hau sai gida.
Cikin fad'uwar gaba, suke duban k'ofar gidan ganin motoci fin uku.
"Wannan motocin duk na barkan ne?"
Cewar Bintu.
"Ina tunanin haka."
Baba maigadi ya bud'emusu kyauren suka shiga, anan ta ga su Abba tsaye tare da mahaifin Ma'u wanda ya kasance k'anin Abban, sai sauran 'yan uwansu.
Suka gaisa sannan suka k'arasa ciki, Saifu ya bisu da akwatin Bintu. Gaba d'ayansu jikinsu a sanyaye. Kuka kawai kakeji daga falon Mami. Ai da gudu Bintu ta k'arasa, duk taron jama'ar dake a falon, bata kasa hango Aisha ba. Itama a guje ta k'araso ta rungumeta.
"Munyi rashi Bintu, Anti Ma'u ta rasu."
Ai ji tayi kamar an bugamata guduma a k'irji sakamakon wani bugawa da yayi.
"Ke kina da hankali kuwa? Haka mutuwar take?!!"
Ta fisge jikinta da gudu ta nufi wata 'yar uwar Ma'u da suke uwa d'aya uba d'aya.
"Anti Zainab, ina Anti Ma'u?"
Cikin kuka Zainab ta k'ara jaddada mata lallai babu Asma'u, Asma'u ta rasu."
Kai Bintu ta ga tashin hankali. Da wayonta, batasan mutuwa ba. Kuka takeyi tana tambaya.
"Haka mutuwar take? Innalillahi."
Suna ji suna gani aka tafi da Ma'u makwancinta na gaskiya. Ko ta kan jaririn bata bi ba ballantana ta sanyashi a ido.
Har magrib bata saki ranta ba, babu abinda take tunanowa sai yanda Ma'u ke hak'uri da dukkan abinda take fad'amata duk furucin da ya zo bakinta akan mijinta.
"Allah Sarki, halinki na gari ya biki. Allah Yayi miki rahma. Aisha, ina Yaya Ma'aruf?"
Aisha ta ja majina.
"Yaya Ma'aruf yana asibiti, amma naji Mami tace sunyi waya da Rufa'i, yanzu zasu taho. Shi fa yana ganin an fito da ita bayan an shiryata ya suma. Har zuwa yanzu, bai k'ara sanin inda kansa yake ba sai yanzun. Yaya Ma'aruf ya ji mutuwa Bintu, yana son Anti Ma'u kamar ransa."
Bintu hawayenta suka k'ara zubowa. Ta tunano baya, ta jinjina kai. Ita tasan yana k'aunar Ma'u.
"Ina Bebin?"
"Yana wajen Anti Amina. Ta amince zata shayar da shi, mijinta bai hanata ba."
Tausayinsa ya mamaye Bintu. Ta mik'e ta fito zuwa wajen da Anti Amina take. Saidai ta tabbatar mata yana d'akin Mami yana bacci. Batayi k'as a gwuiwa ba ta nufi d'akin Mami. Can ta hangoshi cikin gadon jarirai yana baccinsa lafiya lau.
Ta bud'e (net) d'in ta rik'o yatsunsa. Yaron sak mahaifinsa, babu abinda ya bari. Hawaye kawai take shatatarwa na tausayinsa. Shikenan ya zama mara uwa. Abin akwai tausayi. K'aunar yaron ya shigeta kwarai. Nan ta kwanta tana dubansa har bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita itama. Don jiya batayi baccin kirki ba sakamakon d'oki da son ganin Ma'u da bebinta da takeyi.
A haka Mami ta shigo ta iskesu.
"Wani abun sai Bintu, kya bud'ewa yaro (net) sauro ya cijeshi?"
Bintu batasan ma tana yi ba. Mami ta gyara mishi rufin net din ta fita.
* * *
Washegari da asuba Bintu ta farka babu yaro a gefenta. Inna ke sanarmata yana can wajen Amina a d'ayan d'akin. Suna cikin haka Mami ta shigo.
"Mami don Allah kada a d'auke baby daga gidannan."
Mami ta sauke ajiyar zuciya jin k'orafin Bintu.
"Shi kansa uban yaron bai amince ba, yace a samo mai shayarwa ko nawa ne zai biyata da dai yaron yayi nisa da shi."
"Haka ma yafi wallahi Mami. Idan ya koma gidan Anti Amina ba zamu k'ara ganinsa ba fa. Kema nasan bazaki so ya bar nan ba."
Mami ta d'auki hijabin sallarta wanda shi ya maidota d'akin daga d'akin Abba.
"Bani da iko, sai abinda Abbanku ya fad'a. Bari dai muga yanda za'ayi."
Daga haka ta fice. Bintu ta fad'a bandaki tana fad'a a fili.
"Banda mutuwa ma, me zai raba d'a da uwarsa? Kai, Allah Ya bamu kyakkyawan k'arshe."
Inna daga saman darduma ta amsa da amin.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<13>>
Bintu bata samu yiwa Yayan nasu gaisuwa ba sai wajejan sha d'aya na safe. Shi d'inma, aikenta Mami tayi akan yazo Abba yanason ganinsa, don gaba d'aya wayoyinsa a kashe suke.
Da sallamarta ta tura k'ofar, ba'a amsa ba. Kansa kawai take iya hangowa kasancewar ya juyawa k'ofar baya, ta tako sannu kad'an yanda take iya hangen fuskarsa. Fuskarsa ruwan hawaye ne kwance yayinda ya zubawa k'aton enlargement na hotonsa da Ma'u tun ma na lokacin da aka d'aura musu aure yana duba. Ta dubi hoton, ma'auratan sun dace matuk'a da juna. A dai fari da kyau, babu na yar wa. Allah Ya basu, kodayake jini d'aya ne.
Tunda take a rayuwa, bata ta6a jin tausayin Yaya Ma'aruf ba sai a wannan karon da Anti Ma'u ta tafi ta barshi. Ga duk wanda ya zauna da Ma'aruf da Asma'u, zai gane irin tsantsar so da kaunar da sukeyiwa juna. A yau ga mutuwa ta yi musu YANKAR K'AUNA. Ta zauna a gefensa, ina ruwan Bintu, maimakon ta rarrashe shi sai kawai ta had'a kai da gwuiwa ta fashe da kukan itama.
Sai a lokacin yayi niyyar motsawa. Ya ji shigowar mutum, saidai bai san ko wanene ba. A yanzu kuwa da ya ji muryarta, ya ganeta.
"Nayi rashin madubi abin dubawa. Na rasa wani 6angare na jikina. Asma'u ta kasance wata fitila mai haskaka rayuwata, har abada bazan daina jin ciwon rashinta ba. Bani da tamkarta, a yanzu kuma bani da tamkar abinda ta haifamin."
Yayi shiru sakamakon hawayen da ya haneshi k'ara magana.
Bintu ta tsaida kukanta ta dubeshi cike da tausayawa.
Kawai sai ta k'ara rushewa da ihun kuka. Ya tsayar da hawayensa ya dubeta a mamakince. Wai daman tana da tausayi har haka? Ikon Allah.
Sallamar Mami da Abba ta katsesu. Itama jin shirun yayi yawa ne ya sanyasu biyo sahu don Abba har ya fito da zummar ganin abokansa da sukazo musu ta'aziyya.
"A'a, menene kuma haka? Ke ba kiranshi nace kiyi ba?"
Bintu ta mik'e tana sharar majina.
"Kuyi hakuri, kuka ya sanyani."
Abba ya girgiza kai sannan ya nufi wajensa ya zauna. Bintu ta fice daga d'akin. Nasiha mai ratsa jiki Abba yayi mishi. A k'arshe Mami ta d'ora sannan Abba ya umarceshi da yin wanka ya kimtsa ya fito amsar gaisuwa. Ya amsa da toh.
Ita kuwa Bintu kan gadonsu ta nufa kai tsaye bayan shigarta d'aki. Ta kwanta ta soma rusa ihun kuka.
"Allah mun tuba, Allah ka ji k'anmu ba don halinmu ba."
Aisha ta amsa da amin.
"Haba ke kuwa, ya dace kibar wannan kukan, duk masoyin Ma'u na hakika kamata yayi ya bita da addu'a koyaushe. Wannan kukan ba abinda zai rage mata."
Bintu ta zauna sannan ta share hawayenta.
"Hakane, Allah Ya jik'an Anti Ma'u."
To a k'arshe dai bayan anyi sadakar bakwai kowa ya watse, lokacin itama Inna ta wuce Rano. Gidan ya zama daga su sai su, sai ko Ma'aruf wanda Abba ya k'i amincewa da komawarsa gidansa adalilinsa na tsoron halin da zai jefa kansa saboda damuwa. Sai kuma Malama Atine wacce ita ke shayar da Hanif, yaron Ma'u.
Babu wanda ba ya ji da Hanif, daidai da 'yan uwan mahaifiyarsa sukan lek'oshi. Da wuya ayi sati batare da wani cikinsu yazo ganinsa ba. Bintu da Aisha kuwa, d'akin da yake nan ne wajen hirarsu tare da Atine muddin basu da karatu.
Tsakanin Bintu da Ma'aruf kuwa, raina mishi wayon da ta saba yi, ta rage sosai ganin yanda shi kansa ya sanyaya.
Saidai bayan watanni biyu ta fahimci ashe lam6o yayi ba wai ya chanja bane. Abinda ya had'asu kuwa shine.
Tana bacci gefen Hanif yaro mai watanni biyu, wanda saboda gata da kulawar da yake samu sai ka rantse d'an watanni hud'u ne. Cikin magagin baccinta ta d'ora mishi hannu a wajen hanci, ai kuwa yaro ya hau numfarfashi, Allah Ya taimaka Ma'aruf yayi sallama ya shigo wanda sam Bintu bata ji ba, Allah Ya yi ta mai nauyin bacci. Atine suna falo suna hira da 'yan aiki. Lokacin k'arfe uku na rana. Babu zato ya kai mata wawan duka a k'afa. Ta mik'e a gigice tana sosawa.
"Tsabar iskanci kashemin yaron zakiyi?! Atine! Atine!!"
Ai da sauri ta yo d'akin. Nan yayita bud'emata wuta. Ya kuma gargad'eta koda wasa kada ta k'ara yarda Bintu tayi bacci a gefen d'ansa.
Bintu ta turo baki tana dubansa. Ya danna mata harara.
"Sai na yanke wannan bakin mai kama da na tsuntsaye. Tashi ki fita kafin na karyaki!"
Ta mik'e cikin fushi ta bar d'akin.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)