← Book details Bintu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 33

Sashe 4

Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

<<07>>
  Mami ranta ya 6aci, ga tsananin kunya da ta kamata. Ta rasa wa zata watsawa harara tsakanin Ma'aruf da Bintu wacce sam bata da wayo. Kunya ta sanyata mik'ewa bayan ta bar wayar anan ta bi bayan mijinta.
  Ma'aruf ya sanya hannu ya d'auki wayar, tuni Bintu ta ja baya a tsorace. Gaba d'aya fuskarsa ta sauya kwarai, farar fatarsa ta koma ja. Ya dubesu. Da sauri Aisha tayi magana.
"Na rantse da Allah bansan abinda tayi ba, tace dai na ara mata waya."
Gadan-gadan ya nufi Bintu, ya damk'eta kafin ya kwasheta da lafiyayyen mari. Ai tuni ta fasa k'ara.
"Wayyo na shiga uku Innata!"
"Ma'aruf!"
Ya ji muryar Abba cikin tsawa.
"Saketa!!"
Dolensa ya saketa.
"Zo inason magana dakai."
Daga haka Abba ya koma ciki, Ma'aruf a kunyace ya bi bayansa.
Rufa'i wanda wayar ta koma hannunsa ya goge hotunan gaba d'aya, shi kansa a yau Bintu ta k'ona ransa. Ya ja tsaki ya girgiza kai.
"Bintu baki da wayo sam, bakisan ya kamata ba." Ya mik'e tsaye gami da duban Aisha.
"Daga yau sai naga wanda zai k'ara baku waya tunda amfaninta kenan a hannunku. Banda abin Abba ma, ina ke ina rik'e waya a shekarunki. Mts." Ya fice bayan ya jefa wayar aljihun wandonsa.
A can kuwa Ma'aruf ya sha fad'a kwarai. Abba yace dole Ma'u ta tare a d'akinta babu wani sai ta kammala SS3 kuma. Ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, a k'arshe ya gargad'eshi kada ya kusa yace zai k'ara ta6a lafiyar Bintu, yarinya ce.
Wajejan tara na dare, Aisha d Bintu suna d'aki babu mai kula juna cikinsu. Aisha tana fushi da ita akan ta sanya Rufa'i kwace wayarta, daman sam baya so aka bata wayar, ayau gashinan Bintu ta janyomata. Itama Bintu gaba d'aya haushinsu take ji ganin babu wanda ya goyi bayanta. Ga fad'an da ta ci sosai a wajen Mami akan d'abi'ar da takeso ta mayar da ita jiki, wato la6e. Kuma ta k'ara jaddada mata Ma'u matar Ma'aruf ce. Daga haka ta fice, ko uffan basu cewa juna ba da Aisha har bacci yayi awon gaba da su.
Sai zuwa safiya Aisha ta sauko, daman bata kasance mai rik'o ba. Itama labari ta samo wajen Mami cewa za'ayi bikin Ma'aruf bayan sati biyu. Har sunyi magana da Hajiyar Ma'un, itama ta nuna jin dad'inta.
Bintu ta mik'e zaune.
"Wai da gaske ba'ayi musu fad'a ba?"
Aisha ta ja tsaki.
"Banza, ai bazaki ta6a ganewa ba. Bud'e kunne ki ji menene aure."
Nan ta dunga yi mata karatu dallah-dallah. Bintu tayi shiru tana sauraro. K'arshe ta saki baki da mamakin inda Aisha tasan duk wannan.
"A'i wai ina kikejin duk wadannan?"
Aisha ta d'aure fuska.
"Na gayamiki banason wata A'i."
"Yi hakuri, gayamin."
"Kinga ga Rai Dangin Goro. Kuma ga whatsapp na matan aure ina ciki. Maman Faruk sunana ma. Amma ko Mami batasani ba."
"Kin shiga uku wallahi."
Aisha tayi dariya.
"Kuma k'awata Safiya Bingel ta koyamin ba."
Sukayi dariya kafin alamun tsoro ya bayyana saman fuskar Aisha.
"Allah dai ya rufamin asiri na jima da ficewa ciki, da bansan me Yaya Rufa'i zaiyi min ba."
Tun bayan faruwar lamarin, ko kallon inda Bintu take Ma'aruf baya yi. Hakanan baya amsa gaisuwarta, a k'arshe ma ya gargad'eta akan kada ta k'ara gaisheshi baya buk'ata. Sannan koda wasa ya k'ara ganinta a sashensu sai ya kakkaryata.
Itama tun lokacin ta shareshi.
Bayan sati biyu akayi 'yar liyafa sai yini na gida, Ma'u ta tare a gidan mijinta wanda babu nisa sosai da gidansu Ma'aruf. Hatta Innar Bintu wacce kanwa ce ga Mami, ta halarci bikin. Ta ji dadin ganin da ta yiwa 'yarta gaba d'aya ta chanja ta k'ara girma. Matsalar da Bintu ta gayamata guda d'aya, wato karatu. Ita ta gaji da zuwa makaranta gashinan kwata kwata bata da wani basira, bata mayarda hankali. Inna tayita yi mata fad'a, a k'arshe ta rarrasheta da nunamata wataran zata ji dad'in karatun. Jinta kawai tayi, amma sam bata so haka ba, a sonta Inna ta cewa Mami a kyaleta kawai. Babanta ma yazo, shima sai washe baki yakeyi ganin yanda Bintunsu ta koma. Yayita shi wa Mami da Abba albarka yana binsu da addu'o'i na alheri.
* * *
Kuka sosai takeyi, ta fito daga cikin motar a guje ta rungume Mami.
"Dan Allah Mami kiyi hakuri wallahi zanyi karatu, kada a kaini bodin bana so."
Mami ta soma karaya, saidai tana so taga Bintu tayi karatun addini da boko. Shiyasa koda Ma'aruf ya kawo shawarar kaita Bodin batayi musu ba.
"Kiyi hakuri Bintu, zaki dunga ganinmu lokaci zuwa lokaci, ga 'yar uwarki nan kuna tare. Kada ki damu kinji ko?"
Aisha ta lek'o ta windo tana dariya.
"Mami ki kyaleta, seniors zasu jibgeta a banza dole ta nutsu."
Mami ta harareta. Dakyar ta rarrashi Bintu, ta shiga mota. Rufa'i ya ja suka tafi. Jss1 aka ajiye Bintu, zatayi repeating. Ita kuwa Aisha ta wuce Jss3.
* * *
BAYAN SHEKARU BIYAR...!

[7/20, 9:56 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶

      ©Rufaida Omar 
         (July...2016)

<<08>>
"Mamina!!"
Budurwa mai shekaru sha tara cif a duniya ta fad'a cikin d'aga murya alokacin da ta shigo falon a guje.
Mami itama da sauri ta fito daga kicin tana mai cike da murnar ganinta. Ai da sauri ta k'arasa gami da fad'awa jikinta tana dariya, Mami tayi mata kyakkyawar runguma tana murmushi mai bayyana hak'ora kafin ta d'agota.
"Bansan yaushe zaki ajiye shiriritar nan ba."
Budurwar ta turo baki.
"Kingani ko? Daman nasan yanzu za'a soma takuramin a gidannan. To dai babu inda zan k'ara tafiya, atoh."
"Inji wa? Sai mu turaki can k'auyen Rano kije can ki cigaba da haukanki."
Cewar Rufa'i wanda ya shigo mata da akwati, Aisha na biye da shi.
Sukayi dariya har Mami. Bintu ta dubeshi da fararen idanunta masu kyau manya da su. Ya harareta a wasance, ta dauke kai tana fad'in.
"Tab, ai dai dad'in abin bana gudun Innata. Kuma matarka ai itama a k'auyenmu ka kwasota."
"A'a malama, Hajara ta fiki kyau da wayewa. Kin manta da yanda kikayi karatun?"
Duk wannan maganar suna yinta ne a tsaye. Sai lokacin kuma suka zauna ana dariya. Idan da sabo, ya saba da tsokanar da Bintu ke yiwa Hajara matarsa. Kasancewar kusan sa'anni suke, kuma itama 'yar gida ce. A yanzu ta kusa haihuwa, har lokacin kuwa Ma'u ko 6ari bata yi ba. Allah bai kawo haihuwar ba.
Bayan shigarsu d'aki, Bintu ta dira saman gado ta saki k'aramin ihu.
"Home sweet home, shikenan babu k'ara kwana a makaranta, ba wani takura kai da karatu."
Aisha ta d'aka mata duka.
"Karatu yanzu kika soma, wa zai je miki jami'ar?"
Bintu tayi murmushi mai k'ara fiddo tsantsar kyawun fuskarta.
"Ai gwara jami'a tunda jeka ka dawo zanyi, ke nifa banason kwanan makaranta, wai da yaya na kammala? Ni abu d'aya ma nakejin haushi yanzu."
Ta yamutse fuska tana mai zame d'ankwalinta, hakan ya tona asirin gashinta wanda ko kusa bata shafawa relaxer, yana d'aure da ribon, ya cika taf saidai babu tsawo.
"Wannan yayan naki mai kama kwara."
Aisha ta zaro ido, "Au, iskancin naki har ya kai ki kirashi da kwara? Lallai ma, baruwana."
"Abinda yafi haka ma ai zan kirashi. Mutum babu walwala, sai wanda kakeso kad'ai ke ganin hak'oranka. Ji dan Allah idan yana gaban wannan siririyar matar tasa kamar a hure. Ke nan da kike ganina har na mutu bazan ta6a taka gidansa ba. Banje ba ina k'arama ba ballantana kuma yanzu da na k'ara sanin ciwon kaina? Hum um!"
Aisha tayi dariya.
"Kuma wallahi Anti Ma'u tana damuwa sosai akan rashin zuwanki. Amma tana tsoron rashin kunyarki ne shiyasa itama bata shiga harkarki."
Bintu ta yiwa Aisha wani kallo.
"Ita Ma'un ta gayamiki haka?"
"Kai Bintu, Ma'u babu Anti ma?"
Chapter 4 · 0% Book details