← Book details Bintu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 33

Sashe 24

Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

<<35>>
A 6angaren Ma'aruf kuwa, yana shiga d'akin ya ajiye wayarsa k'arama marar tsada sosai k'irar Samsung, da ruwan shan da ya shigo da shi. Ya rage kayan jikinsa ya fad'a wanka. Bayan ya fito ne ya shirya cikin riga mai hannun singilet da wando iyaka gwuiwa na bacci. Alokacin ne kuma ya zare wayarsa daga chaji. Yayi mamakin ganin kira rututu na Lawisa. Kamar bazai kirata ba sai kuma ya kira, don baisan dalilin wannan yawan kiran ba duk da ba yau ta saba kiransa ba saidai muddin ta kira sau d'aya zuwa biyu bai d'auka ba bata matsawa kanta.
Bayan ta d'auka, yayi mata sallama, ta amsa. Kafin ya kai ga tambayar ko lafiya ta hau magana.
"Ka gargadi matarka ta kiyayeni, domin nafi k'arfin wulak'anci."
Yayi shiru kad'an, menene had'inta da Bintu kuma? Ya had'e gira.
"Idan zakiyi magana yanda zan fahimta kiyi, idan kuma bazakiyi ba, lokacina ba na shirme bane ok?"
Nan ta shiga zayyane mishi dukkan abinda ya had'asu. Kusan dariya ya so yi sakamakon kalaman da Bintu ta jefata da su. Har yakai ga murmushin mamaki. Wato har tasan wani wankan sunnah? Hum. Shi fa yana yi mata kallon wacce batasan komai ba.
"Kana jina kayi shiru!"
Ta fad'a ranta a 6ace.
"Duk abinda matata ta fad'a hakane anyi, kiyi hakuri banji dai dadin zagin da tayimiki ba, zan gargad'eta. Ya dace zuwa yanzu ki bar rayuwata Lawisa, ni na gayamiki bazan iya biyayya ga abinda kikeso ba, ba kuma zan iya aikatawa ba. Lokaci yayi da zaki kyaleni, daman ina kulaki ne ba don komai ba sai don girmemin da kikayi da kuma kaunar da kike nunawa d'ana kafin ki 6ullo da wannan batun naki marar kyawun ji. Kiyi hakuri Bintu bata kyauta ba da ta zageki wannan kuma zan gargad'eta."
Tayi shiru don takaici, kawai ta kashe wayar. Ya ta6e baki ya jona Samsung d'insa a chaji. Kamar ya je yanzun ya samu Bintu, saidai ya hak'ura zuwa gobe.
Haka ya kwana zuciyarsa babu ko d'igon damuwa.
Washegari tun tashin Bintu da asuba bata samu damar komawa ba adalilin Hanif, bataso ya tashi neman abincinsa. Tasan mai yiwuwa ya tashi cikin dare amma nauyin baccinta bai barta ta ji ba ballantana ta had'amishi abincinsa.
Tana farkawa ta had'a ta ajiye yanda zai d'an huce kafin ya farka.
Ta mik'e ta koma falon ta tsaftace har kicin, saida ta kammala komai misalin takwas da rabi ta d'ora abin kari. Kafin ta kammala Hanif ya tashi, ta koma gareshi, tana d'aukarshi tayi bandaki, daga zuwa cire famfas ta 6ige da yi mishi wanka, suna fitowa ta tuno da ruwan da ta dora. Da gudu ta direshi saman gado ta nufi kicin. Har ya k'one sauran kad'an, haka ta k'ara wani ruwan akai da Lipton. Ta fito tana jinjina kokarin mata. Haka suke fama ashe.
Ta koma dakin ta shirya Hanif cikin riga fara mai adon purple da bakin jeans bayan ta sanyamishi wando. Ta sanya mishi safa mai fari da purple itama. Ta d'ora mishi bif a wuyansa gudun kada ya 6ata jikinsa. Haka ta daukeshi suka fito falon. Anan k'asa ta zaunar da shi, ta koma ta dauko abincinsa da ta dama ta ajiye saman tebur sannan ta fad'a kicin ta kashe ruwan zafi ta juye a flask. Daman shi kadai ya rage mata tayi.
Ta jera komai saman faranti ta kawo ta ajiye saman tebur.
Sai lokacin ta samu nutsuwar dawowa ga Hanif ta shiga ba shi a baki. Ai kuwa ya hau sha da sauri. Ya bata tausayi, ta tallafi kumatunsa.
"Sorry bebina, na barka da yunwa."
Fatansa ta cigaba da ba shi. Saida ya shanye tas har yana gyatsa sannan ta bashi ruwa ta gyara mishi bakin ta cire bif din.
Bayan ta kammala ta mik'e. Saida ta gama gyara komai a kicin ta dawo ta daukeshi zuwa d'akinta, kayan wasanshi ta dauko ta dire mishi kayan wasa kala-kala. Nan kuwa ya rikice yayita iface-ifacensa yana wasa.
Ganin haka ta hau gyaran gado ta kwashe kayan wankinsu, saukinta akwai mai wanki. Ta ware na Hanif tunda kala d'aya ne bazai gagareta wankewa ba, ta hada nata a inda ta saba sati-sati ake wankewa.
"Bari na shiga wanka bebina, banda rigima." Baimasan tana yi ba, sai wasansa yakeyi yana jik'a kayan wasan da miyau.
Ganin su biyu ne kuma batason yayi rigima yasa ta bar band'akin a bud'e. Duk kuwa da cewar bata hangoshi, amma tafison ta dunga jinsa kada ya hau kuka.
Saida ta kammala wankan ta hau wanke mishi kayansa da ta cire.
Bangaren Ma'aruf kuwa, tara da mintuna ya tashi. Wanka ya soma yi ya zura jallabiya mai hula irinta 'yan Morocco sai dogon wando daga k'asa marar nauyi. Ayau kam koda zai fita baya tunanin fita da wuri.
Yana fitowa falon ya shak'i iska mai dadi, a 'yan zaman da sukayi ya tabbatar Bintu ba yanda ya d'auketa take ba, ba mai son jiki bace wajen kula da gida.
Ya hangi kayan kari a saman tebur, saidai kuma jin iface-ifacen yaronsa yana wasa ne ya sanyashi nufar d'akinta.
Anan tsakar d'akin ya tarar da shi yana wasa, ya k'arewa d'akin kallo, kafin ya sanya hannu ya dauki yaron ya cillashi sama yana dariya. K'arshe ya sakar mishi kiss a le66ansa. Yaron sai k'amshi yakeyi.
"Hey, ina Mamanka?"
Ya tambaya cikin kunnen yaron. Hanif sai dariya yayi kawai.
Jin dariyarsa yasa Bintu fitowa rik'e da rigarsa da ta matse, daga ita sai tawul, bai kai ga rufe cinyarta ba.
Ido hud'u sukayi da Ma'aruf, tayi azamar komawa ciki.
"Au Yaya kaine?"
Bai amsa ba don babu k'arfin amsawar, ya juya kawai ya fita daga d'akin zuwa falo.
Ya tsinci kansa cikin wani yanayi, lallai shi d'in bai zamo dutse ba, yana da buk'ata. Ganin Bintu a haka ya dagula lissafinsa, babu laifi yarinyar tana da abin gani a fad'a a jikinta.
Ya kai kusan mintuna biyar anan yana waya da Abba da Maminsa kafin ta fito, ajiye wayar kuma yayi daidai da fitowarta.
Kallonta ya jazamishi jin wani irin shock tun daga tsakar kansa har tafin k'afarsa.
Ya gaza d'auke idanunsa daga kanta. Wata shegiyar riga ce a jikinta wacce ta matseta. Hannun rigar d'aya irinta vest, d'ayar kuma hannun 3-quarter. Ruwan toka ce rigar, sai wando shima iyaka gwuiwarta bak'i mai kamar roba, hakan yasa ya kamata ya fiddo da zahirin halittarta. Sai hula da ta rufe kan da shi.
Ta sakarwa Hanif dake gefensa murmushi tayi kamar bata ga kallon da Ma'aruf ke binta da shi ba.
"Bebina, bari na shanya kayanka ko?"
A haka ta nufi hanyar waje. Sai lokacin ya dawo hayyacinsa.
"Baki da hankali zaki fita a haka?"
Ta tsaya, saida ta kammala murmushinta kafin ta juyo ta yi mishi wani irin narkakken kallo...
[7/21, 7:33 PM] ‪+249 99 842 9948‬: ¶°°BINTU°°¶

      ©Rufaida Omar 
         (July...2016)

<<36>>
  "Ya Ilahi."
Ya fad'a a ransa. Baisan lokacin da muryarsa ta sanyaya ba.
"Kada ki fita haka please."
"Please?" Ta maimaita a zuciyarta da mamaki. Yau kuma Ma'aruf ke bata oda harda rok'o. Sai kuma ta ji jikinta yayi sanyi.
"To a ina zan shanya?"
Ya kauda kai ga dubanta.
"Jeki zan sanya a shanya. Sannan please ki ringa suturta jikinki saboda aljanu."
   Ta yi murmushi kawai sannan ta koma d'akinta. Tsalle tayi ta fad'a saman gado kafin ta tuntsire da dariya. Yaya Ma'aruf kenan, yana wasa da ita. Ta yi kwafa. Zaiyi bayani ne. Ganin ta soma jin yunwa ne yasa ta mik'ewa dole ta chanja shiga zuwa doguwar riga ta shan iska, jallabiyar mata. Ta fito, baya falon saidai ya sauke Hanif daga saman kujera. Abin ya bata dariya, ta had'a tea abinta ta soma karyawa tana yiwa Hanif wasa. Ranta fari sol, ganin mazan sun soma russuna, ashe ma abin a baki ya tsaya?
   A d'aki kuwa, Ma'aruf ya shiga wani hali, dole saida ya had'a da fad'awa band'aki gami da sakarwa kansa ruwa. Kusan shekara kenan, shi d'in dai mutum ne kuma mai lafiya. Tunaninsa ya soma kuncewa akan Bintu. Ya soma jin wani abu a ranta yana tunani. Eh! Tunani kawai yakeyi, don ba shi da tabbas. Kawai ya dauki abinda yakeji da wani suna na daban wato sha'awa! Banda haka babu wani abu. Acewar Ma'aruf Abdullahi. Wannan ne silar share maganar Lawisa baiyiwa Bintu ba.
      Da daddare tana ji tana gani ya shirya maida Hanif wajen Mami, ranta bai so ba saidai jarabawa zasu soma a makaranta gashinan babu mai rik'o. Akan hakan yace Mami ta nemar musu yarinya da zata iya rik'eshi su je makarantar tare ko su zauna gida har Bintu ta dawo.
    Tun faruwar hakan sai ya zamana Ma'aruf ya rage zaman falon lura da yayi na zata fasa shigar kananun kaya ba. Ita kuwa wani sa'in ba da gayya takeyi ba, sai don hakan ya zame mata sabo. Tun bata rufe kanta har ta zo ta saba adalilin yawan tunasar da itan da yakeyi ta hanyar rankwashin kan.
    Watarana tana zaune a falo, fitowarta kenan bayan ta idar da sallah. Ranar ya kasance juma'a. Sai ga shi shima ya shigo dawowarsa daga masallaci kenan. Tayi mishi sannu da zuwa.
"Shirya zamu fita."
Wani sanyi ya mamayeta, daman zaman ya gundureta. Tayi shiga ta manyan kaya. Leshi ne light blue dinkin riga da siket ya zauna d'abas a jikinta. Ta k'ara gyara kwalliyar fuskarta sannan ta yafa mayafi dark blue hakanan takalminta mai d'an tsini shima dark.
    "Kina ina?"
Jin muryarsa yasa ta saurin d'aukar jakarta wacce ta yiwa ciko sai wayarta.
"Gani nan."
Tayi mishi kyau kwarai, to babu damar nunamata, ya soma tafiya.
"Muje."
Chapter 24 · 0% Book details