Sashe 32
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"A baya, nayi zaton mace d'aya ce ta dace da ni, mace d'aya ta dace na mallakawa komai nawa. Nayi zaton yanda nake, ni d'in MIJIN MACE D'AYA ne, banyi aune ba, mutuwa tayi min YANKAR KAUNA da matar da na so na kuma fi sonta fiye da kowace mace a duniya."
Ya d'an tsagaita kafin ya cigaba da magana.
"Na zo nayi biyayya bayan da na jajircewa zuciyata na yarda da KADDARA, na aureki."
Ya k'ara matse yatsunta yana dubanta duk kuwa da cewar idanunta baya gareshi.
"Bintun Mami, Bintun Ma'aruf. Kinsan me yafi had'ani dake?"
Sai lokacin ta dubeshi ta girgiza kai gami da turo baki. Yayi 'yar dariya.
"Bakya ji, na lura kina da fitina da tsokanar fad'a. Ba kuma sai na fad'amaki wanene Ma'aruf ba. Wannan shine ya kawo rashin jituwarmu. Kafin kuma na zo na had'u da jarabta ta sonki. Ban k'ara sanin ina sonki ba, sai bayan da na nisanta gareki har na kwanaki talatin da d'aya, zuwana Lagos kenan. Bayan na dawo nayi kokarin soma janyoki a jikina domin nuna miki irin so da kaunar da nakeyi miki a aikace batare da na furta ba."
Ya d'anyi shiru yana mai cigaba da murza yatsunta, ta sauke ajiyar zuciyar tana kar6ar sak'on a sannu-sannu.
"My Queen."
Yayi furucin da wata muryar da ta ji kamar ba ta shi ba.
"Ina sonki, ina kaunar na kasance tare da ke har abada. Kin shirya kar6ata matsayin miji kuma uba ga 'ya'yanki?"
Ta sunkuyar da kanta k'asa. Gaskiya ne, da ba'ason zurfafa k'iyayya a addini, bakasan sadda zaka soma son abinda kake k'i ba.
Ya d'ago ha6anta.
"A'a my queen, you have to answer me."
Ta lumshe idanunta. Murya na rawa ta furta a hankali.
"Na amince, ina sonka."
Haka yayita aika sak'o kafin ya barta yana murmushi ya soma da bud'e kofofin.
"Nagode my queen."
Daga haka suka shiga ciki, ran kowannensu k'al.
Ranar ma basu raba shimfid'a ba.
Washegari kuwa da Magriba, yana shigowa ya risketa tana sallah a d'akinta. Ai baisan sadda ya washe hak'ora ba don farinciko sannan ya juya zuwa d'akinsa.
Abincin daren nan dakyar ya ci. Ita kuwa gaba d'aya ta tsorata da yanda ya soma nunamata. Haka dai ta daurewa zuciyarta ganin ya riga ya gama matowa.
A daren bayan sunyi sallar nuna godiya ga Mahaliccinsu yayi musu dogon adduoi.
DAREN ALKHAIRI KENAN...!
* * *
Kuka takeyi sosai, yana rarrashinta, dole tayi shiru ganin yanda duk ya bi ya damu kansa da kukannata.
Da kansa ya taimaka mata ta tsarkake jikinta kafin ya barta ta k'arasa.
Ranar ya tsinci kansa da wani irin farinciki marar misaltuwa. Lallai Allah Ya mishi babbar kyauta, a yau gashinan ga madadin Asma'u. Yau shi ya taimakawa Sauda da d'awainiyar gidan, ita kuwa kunya ce ta hanata fitowa ma.
Tana jin shigowarsa d'akin tayi saurin ture kanta k'ark'ashin filo. Ya k'arasa yana dariya ya hau yi mata cakulkuli, babu shiri ta hau dariya gami da ture filon.
Ya sumbaci goshinta, ta lura yanason yin hakan kafin ya kwanta ya soma yi mata wasu nauyayyun zantuttuka acikin kunnenta. Zata mik'e cikin zafin nama ya janyota, tayi narai-narai da ido, kwalla suka cikamata idon.
"Don Allah kayi hakuri."
Ya kwaikwayi muryarta.
"Don Allah ki nunamin karfinki na mata goma."
Ai sai ta tura kanta jikinsa tana dariya. Yayi mata kyakkyawan runguma.
* * *
Acikin wannan satin, ba'a cewa komai. Da ka gansu kasan suna cike da more rayuwa babu wata matsala a gabansu. Sai gashi wata muguwar shakuwa ta daban ta shiga tsakanin Bintu da Ma'aruf wanda ta bawa kowa mamaki.
Akwai sadda da yamma suna zaune gaba d'aya a falon Mami ana hira har Hashim da Sally wadanda suka kawowa Mamin ziyara, lokacin sauran kwanaki biyar ya rage bikin Aisha.
'Yar kwarewa Ma'aruf yayi, nan da nan Bintu ta rikice ta mance a inda suke ta hau shafa bayansa tana mai mik'a mishi ruwa. Cike sa tausayawa tace. "Sorry my king."
Ya amsa, gyaran muryar da Rufa'i yayi ta farkar da su. Mami dai kauda kanta tayi kawai tana murmushi, yayinda Rufa'i da su Hajara suka sanya dariya. Ma'aruf ko a jikinsa sai ma ita Bintun ce ta dan ji nauyi.
"Oh, Allah Hakim, yau 'yar Mami ce ke wannan rikicewar akan abin gudunta? Soyayya lallai tana dadi
"
Mami ta mike don sai alokacin ta ji kunya. Daman ita Bintu ke kunyar, ai kuwa tana bada baya ta dubi Yaya Rufa'i.
"To meye? Wasu ma suyi mana."
"Lah, ni kike gayawa haka? Eh lallai, kinmanta sadda yake bulale ki nake yare miki? Aisha kinga halin d'an adam."
Bintu na dariya ta zauna gefen mijinta wanda ke sauraronsu da murmushi dauke saman fuskarsa.
"To ai bulala ce ta soyayya, yanzu ba gashinan tayi rana ba, ai hakane ko my king?"
Suka tuntsire da dariya har Ma'aruf din.
"Yes my queen, ashe kingane. Ku dai ku rike girmanku ba'a shiga tsakaninmu da queen, ko harshe da hak'ori ma haka suka ganmu suka kyale. Ato."
Dariyar aka k'ara. Hashim ya d'ora da fad'in.
"To d'an iska, dadin abin dai..."
"Ya isa." Ma'aruf ya dakatar da shi ta hanyar mik'ewa yana dariya gudun kada yayi mishi iskanci.
"Malam tashi muje ku gaisa da Abba."
Haka suka wuni cike da jin wani irin annashuwa.
* * *
BIKI BUDURI....!
((SAIRAN POST DAYA KO BIYU IN SHA ALLAH..!)
[7/28, 7:00 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<48>>
A yau ake bikin sanya Aisha a lalle. Wannan yasa gidan nasu yake a cike da 'yan uwa, cikinsu kuwa har da mutanen Rano. Wannan karon har Umma abokiyar zaman Inna itama ba'a barta a baya ba wajen halartar bikin autar Mami.
Bintu babu zama, sune wancan babban shagon na kayan kicin, sune acan shagon gyaran gashi.
Ya zamana ta dawo gidan da zama, duk yanda Ma'aruf yaso hanawa bai samu hakan ba kasancewar ta samu daurin gindi wajen Mami.
A daren da akayi kamun Aisha, suna zaune a can d'akinsu tare da su Atika harma da Hafsa kanwar Ma'u wacce itama takanas ta zo kwana adalilin mijinta yayi tafiya, kasancewar gidansu basu da sa ido ballantana har abin ya zama wani babban al'amarin da zai shafi ZUMUNCI A YAU.
Sai hira sukeyi suna kyalkyala dariya. Rabin hirar kuwa Atika ke basu akan matar saurayinta. Yanda yake bala'in shakkar daukar koda wayarta a gaban matar.
Wayar Bintu da tayi k'ara ya sanyasu dubanta suna tsokana.
"Toh sarakan soyayya."
Ta murgud'a baki tana dariya kafin tace suyi shiru ta d'aga da sallamarta.
"My king, fatan dai ka bar fushin?"
"Idan kinaso na daina, zo ki sameni anan d'akina. Ta zaro ido.
"Lah, baka tafi gida ba? Karfe goma fa " Yayi 'yar dariya.
Ya d'an tsagaita kafin ya cigaba da magana.
"Na zo nayi biyayya bayan da na jajircewa zuciyata na yarda da KADDARA, na aureki."
Ya k'ara matse yatsunta yana dubanta duk kuwa da cewar idanunta baya gareshi.
"Bintun Mami, Bintun Ma'aruf. Kinsan me yafi had'ani dake?"
Sai lokacin ta dubeshi ta girgiza kai gami da turo baki. Yayi 'yar dariya.
"Bakya ji, na lura kina da fitina da tsokanar fad'a. Ba kuma sai na fad'amaki wanene Ma'aruf ba. Wannan shine ya kawo rashin jituwarmu. Kafin kuma na zo na had'u da jarabta ta sonki. Ban k'ara sanin ina sonki ba, sai bayan da na nisanta gareki har na kwanaki talatin da d'aya, zuwana Lagos kenan. Bayan na dawo nayi kokarin soma janyoki a jikina domin nuna miki irin so da kaunar da nakeyi miki a aikace batare da na furta ba."
Ya d'anyi shiru yana mai cigaba da murza yatsunta, ta sauke ajiyar zuciyar tana kar6ar sak'on a sannu-sannu.
"My Queen."
Yayi furucin da wata muryar da ta ji kamar ba ta shi ba.
"Ina sonki, ina kaunar na kasance tare da ke har abada. Kin shirya kar6ata matsayin miji kuma uba ga 'ya'yanki?"
Ta sunkuyar da kanta k'asa. Gaskiya ne, da ba'ason zurfafa k'iyayya a addini, bakasan sadda zaka soma son abinda kake k'i ba.
Ya d'ago ha6anta.
"A'a my queen, you have to answer me."
Ta lumshe idanunta. Murya na rawa ta furta a hankali.
"Na amince, ina sonka."
Haka yayita aika sak'o kafin ya barta yana murmushi ya soma da bud'e kofofin.
"Nagode my queen."
Daga haka suka shiga ciki, ran kowannensu k'al.
Ranar ma basu raba shimfid'a ba.
Washegari kuwa da Magriba, yana shigowa ya risketa tana sallah a d'akinta. Ai baisan sadda ya washe hak'ora ba don farinciko sannan ya juya zuwa d'akinsa.
Abincin daren nan dakyar ya ci. Ita kuwa gaba d'aya ta tsorata da yanda ya soma nunamata. Haka dai ta daurewa zuciyarta ganin ya riga ya gama matowa.
A daren bayan sunyi sallar nuna godiya ga Mahaliccinsu yayi musu dogon adduoi.
DAREN ALKHAIRI KENAN...!
* * *
Kuka takeyi sosai, yana rarrashinta, dole tayi shiru ganin yanda duk ya bi ya damu kansa da kukannata.
Da kansa ya taimaka mata ta tsarkake jikinta kafin ya barta ta k'arasa.
Ranar ya tsinci kansa da wani irin farinciki marar misaltuwa. Lallai Allah Ya mishi babbar kyauta, a yau gashinan ga madadin Asma'u. Yau shi ya taimakawa Sauda da d'awainiyar gidan, ita kuwa kunya ce ta hanata fitowa ma.
Tana jin shigowarsa d'akin tayi saurin ture kanta k'ark'ashin filo. Ya k'arasa yana dariya ya hau yi mata cakulkuli, babu shiri ta hau dariya gami da ture filon.
Ya sumbaci goshinta, ta lura yanason yin hakan kafin ya kwanta ya soma yi mata wasu nauyayyun zantuttuka acikin kunnenta. Zata mik'e cikin zafin nama ya janyota, tayi narai-narai da ido, kwalla suka cikamata idon.
"Don Allah kayi hakuri."
Ya kwaikwayi muryarta.
"Don Allah ki nunamin karfinki na mata goma."
Ai sai ta tura kanta jikinsa tana dariya. Yayi mata kyakkyawan runguma.
* * *
Acikin wannan satin, ba'a cewa komai. Da ka gansu kasan suna cike da more rayuwa babu wata matsala a gabansu. Sai gashi wata muguwar shakuwa ta daban ta shiga tsakanin Bintu da Ma'aruf wanda ta bawa kowa mamaki.
Akwai sadda da yamma suna zaune gaba d'aya a falon Mami ana hira har Hashim da Sally wadanda suka kawowa Mamin ziyara, lokacin sauran kwanaki biyar ya rage bikin Aisha.
'Yar kwarewa Ma'aruf yayi, nan da nan Bintu ta rikice ta mance a inda suke ta hau shafa bayansa tana mai mik'a mishi ruwa. Cike sa tausayawa tace. "Sorry my king."
Ya amsa, gyaran muryar da Rufa'i yayi ta farkar da su. Mami dai kauda kanta tayi kawai tana murmushi, yayinda Rufa'i da su Hajara suka sanya dariya. Ma'aruf ko a jikinsa sai ma ita Bintun ce ta dan ji nauyi.
"Oh, Allah Hakim, yau 'yar Mami ce ke wannan rikicewar akan abin gudunta? Soyayya lallai tana dadi
"
Mami ta mike don sai alokacin ta ji kunya. Daman ita Bintu ke kunyar, ai kuwa tana bada baya ta dubi Yaya Rufa'i.
"To meye? Wasu ma suyi mana."
"Lah, ni kike gayawa haka? Eh lallai, kinmanta sadda yake bulale ki nake yare miki? Aisha kinga halin d'an adam."
Bintu na dariya ta zauna gefen mijinta wanda ke sauraronsu da murmushi dauke saman fuskarsa.
"To ai bulala ce ta soyayya, yanzu ba gashinan tayi rana ba, ai hakane ko my king?"
Suka tuntsire da dariya har Ma'aruf din.
"Yes my queen, ashe kingane. Ku dai ku rike girmanku ba'a shiga tsakaninmu da queen, ko harshe da hak'ori ma haka suka ganmu suka kyale. Ato."
Dariyar aka k'ara. Hashim ya d'ora da fad'in.
"To d'an iska, dadin abin dai..."
"Ya isa." Ma'aruf ya dakatar da shi ta hanyar mik'ewa yana dariya gudun kada yayi mishi iskanci.
"Malam tashi muje ku gaisa da Abba."
Haka suka wuni cike da jin wani irin annashuwa.
* * *
BIKI BUDURI....!
((SAIRAN POST DAYA KO BIYU IN SHA ALLAH..!)
[7/28, 7:00 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<48>>
A yau ake bikin sanya Aisha a lalle. Wannan yasa gidan nasu yake a cike da 'yan uwa, cikinsu kuwa har da mutanen Rano. Wannan karon har Umma abokiyar zaman Inna itama ba'a barta a baya ba wajen halartar bikin autar Mami.
Bintu babu zama, sune wancan babban shagon na kayan kicin, sune acan shagon gyaran gashi.
Ya zamana ta dawo gidan da zama, duk yanda Ma'aruf yaso hanawa bai samu hakan ba kasancewar ta samu daurin gindi wajen Mami.
A daren da akayi kamun Aisha, suna zaune a can d'akinsu tare da su Atika harma da Hafsa kanwar Ma'u wacce itama takanas ta zo kwana adalilin mijinta yayi tafiya, kasancewar gidansu basu da sa ido ballantana har abin ya zama wani babban al'amarin da zai shafi ZUMUNCI A YAU.
Sai hira sukeyi suna kyalkyala dariya. Rabin hirar kuwa Atika ke basu akan matar saurayinta. Yanda yake bala'in shakkar daukar koda wayarta a gaban matar.
Wayar Bintu da tayi k'ara ya sanyasu dubanta suna tsokana.
"Toh sarakan soyayya."
Ta murgud'a baki tana dariya kafin tace suyi shiru ta d'aga da sallamarta.
"My king, fatan dai ka bar fushin?"
"Idan kinaso na daina, zo ki sameni anan d'akina. Ta zaro ido.
"Lah, baka tafi gida ba? Karfe goma fa " Yayi 'yar dariya.