Sashe 16
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
<<25>>
Ko da ta isa gidan babu wanda ya d'ago wani abu. Bayan ta idar da Azhar ta dawo falon. Mami ta dubeta, ta sakarwa Mami murmushi kafin ta kwanta saman cinyarta.
"Wash! Wallahi nagaji Mami."
Wani sanyi ya ratsa zuciyar Mamin ganin Bintu bata sanya komai a ranta ba. Ta dafa kanta.
"Sannu 'yar gidan Mami, amma yau baku jima ba."
Ta lumshe ido tana mai jin dad'in susar kan da Mamin keyi mata. A haka Aisha ta shigo gidan daga gidan amarya Hafsa. Ganin Bintu tayi turus.
"Har kin dawo?"
Ta harareta.
"Menene?"
Aisha na dariya ta zauna.
"A'a mamaki nayi dai. Haba Mami, kinason biyewa yarinyar nan wallahi. K'atuwa da ita sai shegen shagwa6a, wannan dai mijinki yana da aiki wallahi."
Ta ta6e baki ta muskuta.
"Wallahi A'i kin fiye sanye ido, dad'in abin ba ke zakiyi aikin ba. Mijina kuwa..."
Shaf, ta mance da wani batunta da Ma'aruf harma take batun miji. Sai kuma ta ji nauyi, ta maze ta share batun ta hanyar sanyo wata hirar.
"Ke ni bamu labarin gidan amarya."
Nan fa ta soma zuba, tuni Bintu ta ware ta mik'e zaune. Har Mami suka had'u akayita hira, a k'arshe suka shige d'akinsu sukayi la'asar.
Tana zaune saman darduma tana sauraron bayanin da Aisha ke faman zubawa yayinda take sauya kayan jikinta.
"Ke ni har na soma tunanin anya ba zan ce Ashir d'ina ya fito ba, irin wannan soyayyar da na tarar a gidan Hafsa da Bashir ai hum."
Ta yi shiru tana dariya. Bintu ta ja tsaki.
"Ke kuma babu soyayyar da ta burgeka sai ta wad'annan? Kwata kwata basu burgeni ba balle suyi abinda zai burgeni."
Hafsa ta zauna gefen gado da d'aura k'irji tana murmushi mai bayyana hak'ora.
"Bakisan so ba, amma zan d'agamiki k'afa wuyarta dai mu mik'a ki d'akin Yaya."
Ran Bintu ya 6aci ta danne saidai duk da hakan saida fa aikamata harara.
"Dad'in abin ni soyayyar ba damuna tayi ba, ina bawa lokutana muhimmanci. Da soyayyar gwara a siyomin rake nayita 6alla ina shan abina."
Hafsa ta kyalkyale da dariya, ta kai mata duka a kafad'a alokaci guda kuma ta mik'e.
"Lallai akwai aiki awajen mata."
Da haka ta shige band'aki, Bintu ta bita da kallon baki da matsala. Ta kwantar da kanta ta yi shiru. Wai daman damuwa tana kashe jiki har haka? Iko sai Allah, gashinan ayau sanadin wannan rikitaccen al'amari ta zama wata mai sanyi. Wayarta da tayi k'ara yasa ta d'aukowa, Innarta ce, bayan gaisuwa ta tambayeta ko sun isa lafiya. Ta tabbatar mata lafiya kalau. Ta k'ara binta da nasiha akan ta maida komai ga Allah, in sha Allah ta na ji a jikinta akwai alheri a aureta da d'an uwanta. Bintu tayi na'am da hakan kafin daga bisani suyi sallama.
Ma'aruf a 6angarensa yaso ya yiwa Bintu tambaya game da inda ta je saidai kuma zuwa yanzun bayason shiga dukkan lamuranta. Ai ya damu da ita kenan ma idan ya shiga.
Kwana ukun da Mami ta d'ibar mata na cika, Mami ta ji daddad'ar magana bayan ta kirayeta don jjn abinda ta yanke. Dad'i yasa Mami ta rugumeta a jiki.
"Alhamdulillah, Allah Yayi muku albarka."
Bintu ta lumshe ido kawai ranta na k'una. Ita fa tasan rayuwarta zata yi babu dad'i ne muddin ta auri Ma'aruf.
Abin ya bata mamaki ganin Mami har da 'yar kwallar farinciki. Lallai sai yanzu take k'ara gaskata maganar Innarta. Ta kuma hak'ik'ance Mami dagaske tana son wannan had'in.
Kafin sati biyu magana fa ta zagaya dangi. Tuni Abba da k'aninsa Mahaifin Ma'u wanda suke kira Alhaji, suka sun je har Rano sunga mahaifin Bintu an tsaida magana. Abun fa ya yiwa manyannan dadi. Nan suka yanke nan zuwa watanni biyu kacal.
Haka suka dawo cike da tsantsar farin ciki. Ai Bintu tun daga ranar bata k'ara bari koda wasa sun had'u da Ma'aruf ba, hakanan shima tunda ya fahimci ta sani ya rage shigowa falon Mami ya yi dogon zama. Saidai idan Mamin ce ta nemeshi game da shawarar wani abun na biki.
* * *
Wani yammaci ya kama lahadi, gaba d'aya gidan sun had'u a falon Mami suna hira har Rufa'i wanda ya zo da d'ansa, shima gogan yana zaune ya gama had'ewa cikin riga da wando farare tas, sunata hirar siyasa. Abba ne kawai bayanan sun fita taronsu na gida na manyan dattawa.(Family meeting). Alokacin Bintu ta fito sanye da riga da wando, rigar har gwuiwarta sai pencil jeans da ta sanya. Kanta kuwa ba'a ma batun d'ankwal, gashin ne dai ga shi nan an tufkeshi babu ko kitso. Biyun nan daman sam basa daga cikin tsarinta. Mami kad'ai ke tsawatar mata akan hakan. Kallo d'aya ta wurga musu gaba d'aya bata k'ara duban inda suke ba ta cigaba da tafiya.
"Yayarmu." Ta tsinci muryar Rufa'i, daman tasan shi da Aisha ke kiranta da hakan idan sun so tsokanarta.
Ta cigaba da tafiyarta ta shige kicin tamkar bata ji shi ba....
[7/19, 9:07 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Ko da ta isa gidan babu wanda ya d'ago wani abu. Bayan ta idar da Azhar ta dawo falon. Mami ta dubeta, ta sakarwa Mami murmushi kafin ta kwanta saman cinyarta.
"Wash! Wallahi nagaji Mami."
Wani sanyi ya ratsa zuciyar Mamin ganin Bintu bata sanya komai a ranta ba. Ta dafa kanta.
"Sannu 'yar gidan Mami, amma yau baku jima ba."
Ta lumshe ido tana mai jin dad'in susar kan da Mamin keyi mata. A haka Aisha ta shigo gidan daga gidan amarya Hafsa. Ganin Bintu tayi turus.
"Har kin dawo?"
Ta harareta.
"Menene?"
Aisha na dariya ta zauna.
"A'a mamaki nayi dai. Haba Mami, kinason biyewa yarinyar nan wallahi. K'atuwa da ita sai shegen shagwa6a, wannan dai mijinki yana da aiki wallahi."
Ta ta6e baki ta muskuta.
"Wallahi A'i kin fiye sanye ido, dad'in abin ba ke zakiyi aikin ba. Mijina kuwa..."
Shaf, ta mance da wani batunta da Ma'aruf harma take batun miji. Sai kuma ta ji nauyi, ta maze ta share batun ta hanyar sanyo wata hirar.
"Ke ni bamu labarin gidan amarya."
Nan fa ta soma zuba, tuni Bintu ta ware ta mik'e zaune. Har Mami suka had'u akayita hira, a k'arshe suka shige d'akinsu sukayi la'asar.
Tana zaune saman darduma tana sauraron bayanin da Aisha ke faman zubawa yayinda take sauya kayan jikinta.
"Ke ni har na soma tunanin anya ba zan ce Ashir d'ina ya fito ba, irin wannan soyayyar da na tarar a gidan Hafsa da Bashir ai hum."
Ta yi shiru tana dariya. Bintu ta ja tsaki.
"Ke kuma babu soyayyar da ta burgeka sai ta wad'annan? Kwata kwata basu burgeni ba balle suyi abinda zai burgeni."
Hafsa ta zauna gefen gado da d'aura k'irji tana murmushi mai bayyana hak'ora.
"Bakisan so ba, amma zan d'agamiki k'afa wuyarta dai mu mik'a ki d'akin Yaya."
Ran Bintu ya 6aci ta danne saidai duk da hakan saida fa aikamata harara.
"Dad'in abin ni soyayyar ba damuna tayi ba, ina bawa lokutana muhimmanci. Da soyayyar gwara a siyomin rake nayita 6alla ina shan abina."
Hafsa ta kyalkyale da dariya, ta kai mata duka a kafad'a alokaci guda kuma ta mik'e.
"Lallai akwai aiki awajen mata."
Da haka ta shige band'aki, Bintu ta bita da kallon baki da matsala. Ta kwantar da kanta ta yi shiru. Wai daman damuwa tana kashe jiki har haka? Iko sai Allah, gashinan ayau sanadin wannan rikitaccen al'amari ta zama wata mai sanyi. Wayarta da tayi k'ara yasa ta d'aukowa, Innarta ce, bayan gaisuwa ta tambayeta ko sun isa lafiya. Ta tabbatar mata lafiya kalau. Ta k'ara binta da nasiha akan ta maida komai ga Allah, in sha Allah ta na ji a jikinta akwai alheri a aureta da d'an uwanta. Bintu tayi na'am da hakan kafin daga bisani suyi sallama.
Ma'aruf a 6angarensa yaso ya yiwa Bintu tambaya game da inda ta je saidai kuma zuwa yanzun bayason shiga dukkan lamuranta. Ai ya damu da ita kenan ma idan ya shiga.
Kwana ukun da Mami ta d'ibar mata na cika, Mami ta ji daddad'ar magana bayan ta kirayeta don jjn abinda ta yanke. Dad'i yasa Mami ta rugumeta a jiki.
"Alhamdulillah, Allah Yayi muku albarka."
Bintu ta lumshe ido kawai ranta na k'una. Ita fa tasan rayuwarta zata yi babu dad'i ne muddin ta auri Ma'aruf.
Abin ya bata mamaki ganin Mami har da 'yar kwallar farinciki. Lallai sai yanzu take k'ara gaskata maganar Innarta. Ta kuma hak'ik'ance Mami dagaske tana son wannan had'in.
Kafin sati biyu magana fa ta zagaya dangi. Tuni Abba da k'aninsa Mahaifin Ma'u wanda suke kira Alhaji, suka sun je har Rano sunga mahaifin Bintu an tsaida magana. Abun fa ya yiwa manyannan dadi. Nan suka yanke nan zuwa watanni biyu kacal.
Haka suka dawo cike da tsantsar farin ciki. Ai Bintu tun daga ranar bata k'ara bari koda wasa sun had'u da Ma'aruf ba, hakanan shima tunda ya fahimci ta sani ya rage shigowa falon Mami ya yi dogon zama. Saidai idan Mamin ce ta nemeshi game da shawarar wani abun na biki.
* * *
Wani yammaci ya kama lahadi, gaba d'aya gidan sun had'u a falon Mami suna hira har Rufa'i wanda ya zo da d'ansa, shima gogan yana zaune ya gama had'ewa cikin riga da wando farare tas, sunata hirar siyasa. Abba ne kawai bayanan sun fita taronsu na gida na manyan dattawa.(Family meeting). Alokacin Bintu ta fito sanye da riga da wando, rigar har gwuiwarta sai pencil jeans da ta sanya. Kanta kuwa ba'a ma batun d'ankwal, gashin ne dai ga shi nan an tufkeshi babu ko kitso. Biyun nan daman sam basa daga cikin tsarinta. Mami kad'ai ke tsawatar mata akan hakan. Kallo d'aya ta wurga musu gaba d'aya bata k'ara duban inda suke ba ta cigaba da tafiya.
"Yayarmu." Ta tsinci muryar Rufa'i, daman tasan shi da Aisha ke kiranta da hakan idan sun so tsokanarta.
Ta cigaba da tafiyarta ta shige kicin tamkar bata ji shi ba....
[7/19, 9:07 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)