Sashe 13
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
<<22>>
Ya kwashi kusan rabin awa kafin yayi niyyar tafiya, a hakan ma budurwar wacce ya kira da Sa'a bata so ba, haka sukayi sallama tana rok'onsa da ya k'ara dawowa. Abin har ya bawa Bintu haushi, ta k'ulu iyakar k'uluwa, dubu yanda mace ba kunya take karya murya, shi kuwa sai shan k'amshi, haka kawai ta ji wata muguwar tsanar Sa'a ta dirar mata. Can kuma dai tayi tunanin me zai dameta?
Bayan tafiyarta ya juyo ya dubi Bintu wacce sai lokacin ne ta tunano inda suka nufa, ta turo baki ta 6ata rai. Murmushi kawai yayi baice komai ba, ai kwalliyar ta biya kud'in sabulu, yayi ribas maigadi ya bud'e mishi (gate) ya fita.
Sun kusa Afficent ya tsaida motar a gefen hanya. Ta dubeshi, hannu yasa ya bud'e mazaunin gefensa.
"Dawo gaba, don ba direba kika ajiye ba."
Ta yi jim kamar kada ta fito sai kuma ta bud'e ta dawo ta zauna ranta a 6ace. Tsaf ta fahimci manufar kaita wajen budurwarsa, wato dai ya nunamata lallai akwai mata 'yan gayu da suka damu da shi fiye da zatonta.
Ya dubeta ya maida kansa ga hanya lokacin da ya sha kwanar da zata kaishi d'akin taron.
Suna isa ya mik'a mata wayarta, a fusace ta fice daga motar. Saida ya kammala kunna wayoyinsa sannan ya kashe motar ya rufeta ya shiga.
Tun kafin ka k'arasa cikin hall d'in kana jiyo tashin kid'e-kid'e. Tana k'arasawa ciki kuwa ta daburce ganin taron jama'a. Mafi yawansu, dangin Abba ne. Ta dawo baya da zummar kiran Aisha a waya. Sai jin maganarsa tayi a dab da kunnenta sakamakon k'arar kid'an da bazai barta ta ji maganarsa ba.
"Illar 'yan k'auyen kenan, ko shekara nawa zasuyi a birni, wayewarsu, suna ce kawai."
Daga haka ya zarce ciki, kai tsaye 6angaren maza ya nufa. Ta bishi da kallon takaici. Ji tayi an dafa ta ta juya, ganin Aisha yasa ta sauke ajiyar zuciya, ta kasa magana kawai sai ta soma kuka. Ganin haka Aisha ta ja hannunta suka nufi waje.
"Ke ina kuka tsaya? Ga Mami can cikin damuwa. Me Yayan ya yi miki?"
Bintu tayi kwafa. Ta kwashe labarin komai ta bata, Aisha abin ya so bata dariya jin yanda take faman kushe Sa'a, ita kam tasan wacece Sa'a, d'iyar wani d'an majalisa ce, tun kafin ma ya auri Ma'u tana sonsa yanzu kuwa bazawara ce ma mijinta ya saketa adalilin shaye-shayen da takeyi ya zamar mata jiki. Tasan ko a mafarki, Ma'aruf bazai ta6a auren Sa'a ba ballantana kuma a farke. Saidai kuma jin abinda yace mata yanzun ne yasa jikin Aisha sanyi.
"Kiyi hakuri, kinsan halin Yaya Ma'aruf, ba yau ya soma ya6amiki magana don kawai ya k'ular dake ba. Ke kika nuna kina da saurin fushi shi kuma anan yake samun damar yi miki son ransa. Ni yanzu ba wannan ba, muje Mami ta ganki hankalinta ya kwanta."
Bintu ta share idanunta gami da yin kwafa kawai, Aisha ta gyara mata inda ya 6aci, tana janta da zolaya har Bintu ta saki ranta suka shiga ciki.
Mami ta yi murnar ganinta kafin ta hau fad'an meyasa bata hau adaidaita ba tunda Ma'aruf d'in ya biya hira. Bintu tayi shiru da mamaki, ko kusa Ma'aruf baisan yayi k'arya ba babu kwakkwarar dalili.
Har aka tashi taron bata sanyashi a ido ba. Tun kafin ma a tashin ashe ya tafi, haka ta ji a bakin Rufa'i sadda Mami ke cigiyarsa.
Washegari da yamma aka mik'a amarya Hafsa gidan mijinta. Babu inda Bintu ta je, saboda makaranta, ranar a gajiye ta dawo lik'is. Agaban idanunta Mami suka wuce, tana kwance saman doguwar kujera bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Dab da magrib, Ma'aruf ya shigo. Dawowarsa kenan daga ofis, tuni ya yi wanka ya chanja zuwa k'ananun kaya na shan iska.
Sam bai ko lura da ita a falon ba, duk a zatonsa, gaba d'aya gidan ne suka fice sai masu aiki ya rage da Atine da Hanif wadanda ya hanesu fita acewarsa, yaron ya gaji, kwana biyu kenan ana fita da shi.
Saida ya shiga kicin ya nemi Iya da ta d'oramishi ruwan shayi, sannan ya doshi falon. Alokacin ne idanunsa ya kai gareta.
Bacci takeyi, kallo d'aya zakayiwa fuskarta ka fahimci bata da wata matsala. Gashinta wanda ko kusa batason kitseshi ya mik'e tsaye kamar na mahaukaciya, ribon d'in kuwa tuni ya fad'i.
Daga ita sai vest da dogon wandon da bai matseta. Ya ja guntun tsaki kafin ya d'auki filon kujera a gefensa yayi jifa da shi saman fuskarta.
Bacci na Bintu fa, saida ya gwammace bai jefeta ba, juyin da ta yi yasa shi mik'ewa dole ya bar mata falon.
D'ayan falon ya koma ya jinginar da kanshi saman kujera yana mai lumshe idanunsa. Wani yanayi ne, wanda tunawa da Ma'unsa kad'ai kan janyo mishi.
Cikin k'arfin addu'a ya bagarar da tunanin ta hanyar buga game a wayarsa. Har Iya ta kawomishi ruwan shayin kamar yanda ya buk'ata.
"Ki tashi mai baccin nan, lokacin sallah ya kawo kai."
Ya fad'a yana duban Iya. Iya tayi 'yar dariya.
"Au, mutuniyarka? Bintu ko rigima, ai saida na hanata bata fasa ba."
Ta fice. Ta gabansa Bintu ta shige d'akinsu, bai ko dubeta ba. Bayan ta kimtsa ta k'ara fitowa cikin doguwar jallabiya da hula a kanta.
Tayi kamar bata ganshi ba zata fice.
"Ke bakisan ki gaida mutum ba?"
Har lokacin haushinsa takeji. A ciki ciki ta gaisheshi bayan ta d'an russuna. Bai amsa ba, itama ta shareshi ta fice daga falon.
Ya numfasa, har lokacin zuciyarsa ta kasa yanke tayashi yanke abinda ya dace. A gobe ne kuma zai bawa Abba amsa. Shi dai yasan Bintu ba ta daga cikin matan da yakeso, ina zai iya da shiriritarta? Ba k'aramin aikinsa bane wataran ya zaneta yayi mata raga-raga. Saidai kuma yanajin nauyin k'in amincewa aurenta. Da wane idon zai dubi Abba yace a'a? Mami kam, ya sani ba zata ji dad'i ba ko kad'an idan ya k'i jininta.
Da wannan tunanin ya kammala ya fito. Zai fice ya hangota daga d'akin Hanif, rik'e da shi a cinyarta tana kai lomar abinci tana d'an lasa mishi miyar a baki, sai kuma ta kyalkyale da dariya. Sun burgeshi burgewa, yasan tana son d'ansa, yana girmamata a wannan wajen.
Ya numfasa ya fice jin an soma kiraye-kirayen sallah.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Ya kwashi kusan rabin awa kafin yayi niyyar tafiya, a hakan ma budurwar wacce ya kira da Sa'a bata so ba, haka sukayi sallama tana rok'onsa da ya k'ara dawowa. Abin har ya bawa Bintu haushi, ta k'ulu iyakar k'uluwa, dubu yanda mace ba kunya take karya murya, shi kuwa sai shan k'amshi, haka kawai ta ji wata muguwar tsanar Sa'a ta dirar mata. Can kuma dai tayi tunanin me zai dameta?
Bayan tafiyarta ya juyo ya dubi Bintu wacce sai lokacin ne ta tunano inda suka nufa, ta turo baki ta 6ata rai. Murmushi kawai yayi baice komai ba, ai kwalliyar ta biya kud'in sabulu, yayi ribas maigadi ya bud'e mishi (gate) ya fita.
Sun kusa Afficent ya tsaida motar a gefen hanya. Ta dubeshi, hannu yasa ya bud'e mazaunin gefensa.
"Dawo gaba, don ba direba kika ajiye ba."
Ta yi jim kamar kada ta fito sai kuma ta bud'e ta dawo ta zauna ranta a 6ace. Tsaf ta fahimci manufar kaita wajen budurwarsa, wato dai ya nunamata lallai akwai mata 'yan gayu da suka damu da shi fiye da zatonta.
Ya dubeta ya maida kansa ga hanya lokacin da ya sha kwanar da zata kaishi d'akin taron.
Suna isa ya mik'a mata wayarta, a fusace ta fice daga motar. Saida ya kammala kunna wayoyinsa sannan ya kashe motar ya rufeta ya shiga.
Tun kafin ka k'arasa cikin hall d'in kana jiyo tashin kid'e-kid'e. Tana k'arasawa ciki kuwa ta daburce ganin taron jama'a. Mafi yawansu, dangin Abba ne. Ta dawo baya da zummar kiran Aisha a waya. Sai jin maganarsa tayi a dab da kunnenta sakamakon k'arar kid'an da bazai barta ta ji maganarsa ba.
"Illar 'yan k'auyen kenan, ko shekara nawa zasuyi a birni, wayewarsu, suna ce kawai."
Daga haka ya zarce ciki, kai tsaye 6angaren maza ya nufa. Ta bishi da kallon takaici. Ji tayi an dafa ta ta juya, ganin Aisha yasa ta sauke ajiyar zuciya, ta kasa magana kawai sai ta soma kuka. Ganin haka Aisha ta ja hannunta suka nufi waje.
"Ke ina kuka tsaya? Ga Mami can cikin damuwa. Me Yayan ya yi miki?"
Bintu tayi kwafa. Ta kwashe labarin komai ta bata, Aisha abin ya so bata dariya jin yanda take faman kushe Sa'a, ita kam tasan wacece Sa'a, d'iyar wani d'an majalisa ce, tun kafin ma ya auri Ma'u tana sonsa yanzu kuwa bazawara ce ma mijinta ya saketa adalilin shaye-shayen da takeyi ya zamar mata jiki. Tasan ko a mafarki, Ma'aruf bazai ta6a auren Sa'a ba ballantana kuma a farke. Saidai kuma jin abinda yace mata yanzun ne yasa jikin Aisha sanyi.
"Kiyi hakuri, kinsan halin Yaya Ma'aruf, ba yau ya soma ya6amiki magana don kawai ya k'ular dake ba. Ke kika nuna kina da saurin fushi shi kuma anan yake samun damar yi miki son ransa. Ni yanzu ba wannan ba, muje Mami ta ganki hankalinta ya kwanta."
Bintu ta share idanunta gami da yin kwafa kawai, Aisha ta gyara mata inda ya 6aci, tana janta da zolaya har Bintu ta saki ranta suka shiga ciki.
Mami ta yi murnar ganinta kafin ta hau fad'an meyasa bata hau adaidaita ba tunda Ma'aruf d'in ya biya hira. Bintu tayi shiru da mamaki, ko kusa Ma'aruf baisan yayi k'arya ba babu kwakkwarar dalili.
Har aka tashi taron bata sanyashi a ido ba. Tun kafin ma a tashin ashe ya tafi, haka ta ji a bakin Rufa'i sadda Mami ke cigiyarsa.
Washegari da yamma aka mik'a amarya Hafsa gidan mijinta. Babu inda Bintu ta je, saboda makaranta, ranar a gajiye ta dawo lik'is. Agaban idanunta Mami suka wuce, tana kwance saman doguwar kujera bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Dab da magrib, Ma'aruf ya shigo. Dawowarsa kenan daga ofis, tuni ya yi wanka ya chanja zuwa k'ananun kaya na shan iska.
Sam bai ko lura da ita a falon ba, duk a zatonsa, gaba d'aya gidan ne suka fice sai masu aiki ya rage da Atine da Hanif wadanda ya hanesu fita acewarsa, yaron ya gaji, kwana biyu kenan ana fita da shi.
Saida ya shiga kicin ya nemi Iya da ta d'oramishi ruwan shayi, sannan ya doshi falon. Alokacin ne idanunsa ya kai gareta.
Bacci takeyi, kallo d'aya zakayiwa fuskarta ka fahimci bata da wata matsala. Gashinta wanda ko kusa batason kitseshi ya mik'e tsaye kamar na mahaukaciya, ribon d'in kuwa tuni ya fad'i.
Daga ita sai vest da dogon wandon da bai matseta. Ya ja guntun tsaki kafin ya d'auki filon kujera a gefensa yayi jifa da shi saman fuskarta.
Bacci na Bintu fa, saida ya gwammace bai jefeta ba, juyin da ta yi yasa shi mik'ewa dole ya bar mata falon.
D'ayan falon ya koma ya jinginar da kanshi saman kujera yana mai lumshe idanunsa. Wani yanayi ne, wanda tunawa da Ma'unsa kad'ai kan janyo mishi.
Cikin k'arfin addu'a ya bagarar da tunanin ta hanyar buga game a wayarsa. Har Iya ta kawomishi ruwan shayin kamar yanda ya buk'ata.
"Ki tashi mai baccin nan, lokacin sallah ya kawo kai."
Ya fad'a yana duban Iya. Iya tayi 'yar dariya.
"Au, mutuniyarka? Bintu ko rigima, ai saida na hanata bata fasa ba."
Ta fice. Ta gabansa Bintu ta shige d'akinsu, bai ko dubeta ba. Bayan ta kimtsa ta k'ara fitowa cikin doguwar jallabiya da hula a kanta.
Tayi kamar bata ganshi ba zata fice.
"Ke bakisan ki gaida mutum ba?"
Har lokacin haushinsa takeji. A ciki ciki ta gaisheshi bayan ta d'an russuna. Bai amsa ba, itama ta shareshi ta fice daga falon.
Ya numfasa, har lokacin zuciyarsa ta kasa yanke tayashi yanke abinda ya dace. A gobe ne kuma zai bawa Abba amsa. Shi dai yasan Bintu ba ta daga cikin matan da yakeso, ina zai iya da shiriritarta? Ba k'aramin aikinsa bane wataran ya zaneta yayi mata raga-raga. Saidai kuma yanajin nauyin k'in amincewa aurenta. Da wane idon zai dubi Abba yace a'a? Mami kam, ya sani ba zata ji dad'i ba ko kad'an idan ya k'i jininta.
Da wannan tunanin ya kammala ya fito. Zai fice ya hangota daga d'akin Hanif, rik'e da shi a cinyarta tana kai lomar abinci tana d'an lasa mishi miyar a baki, sai kuma ta kyalkyale da dariya. Sun burgeshi burgewa, yasan tana son d'ansa, yana girmamata a wannan wajen.
Ya numfasa ya fice jin an soma kiraye-kirayen sallah.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)