Sashe 22
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
<<32>>
Ta kammala tsaf ta zubo nata a filet bayan ta bar mishi nashi cikin flask. Kasancewar ba sallar takeyi ba, yasa ta zaman cin abincinta.
Ta soma ci kenan tana kallon wata tasha da ke hasko wrestling. A haka ya fito da zummar tafiya masallaci. Yayi mata kallo d'aya ya cigaba da tafiyarsa baice uffan ba. Ta bishi da kallo, wataran rashin son yawan magana irin na Ma'aruf yakan bata mamaki matuk'a. Kodayake daman bashi da hayaniya, bar shi dai da son girma. D'an hayaniya sai mutuminta, Yaya Rufa'i.
Bayan ya dawo ya zauna a falon alokacin ta kusa kammala cin abincin. Ya dubi abinda take kallo sannan ya dubeta.
"Bani remote."
Ta narke fuska.
"Yaya don Allah ka bari na gama kallo."
Ya yamutse fuska batare da ya dubeta ba don baya buk'atar cigaba da dubannata saboda dalilai.
"A matan ma bansan sunan da zan baki ba, me mace zatayi da wrestling idan na rashin abin yi ba? Malama bani na kalli abinda zai fissheni."
Ta mik'a mishi remote d'in ta d'auki filet tayi hanyar kicin ganin ya kamo Aljazeera. Daman ai ba yau suka soma fad'a akan tashar kallo ba.
"Ina abincina?" Bata ko juyo ba ballantana ta dubeshi ta amsa.
"Yana kicin."
"Kawomin."
Ta had'o mishi komai ta ajiye, zama tayi gami da janyo wayarta.
"Malama tashi ki suturta jikinki kafin zuciyata ta tashi."
Wani gululun bakinciki ya turnuk'eta, kai bafa zata amince da wannan cin fuskar ba. Dole ne tayi maganin Yayan nan.
Ta fasa zaman falon ta koma d'aki. Batasan sadda ta soma hawaye ba, kewar Maminta da Aisharta suka mamayeta. Yanzu da ace tana gaban Mami da duk wani abu da zai mata ba dai yayi a gabanta ba. Gashi kuma babu damar kai k'ara, to tace me? Alhalin ta riga ta nunawa Aisha komai lafiya ke tafiya tsakani. Ganin zata sanyawa ranta damuwar babu gaira babu dalili ne yasa ta janyo wayarta. Whatsapp ta soma k'ok'arin downloading, a baya sam bata chatting, tana ganin yanda Aisha ke haukar karanta books da kutsawa groups na matan aure amma ita ko a jikinta. Wannan karon kam, tayi niyyar somawa don ya d'ebemata kewa.
Bayan ta gama downloading, ya kammala updating contacts dinta da komai. Bata d'ora hotonta ba, tabar wajen fayau.
Dad'i ya cikata ganin Aisha online, hakanan da yawa daga cikin 'yan uwansu na Rano da 'yan uwan Abban Aisha ma duk sunayi. Kai tsaye ta yiwa Aisha magana. Aisha harda 'yar rawarta na murnar ganinta. Nan ta sanyata a groups, na matan auren ma ta sanya (Admin) ta sanyata ciki.
Nan ta soma ganin abubuwa, saidai tafi maida hankali a na 'yanuwansu na Rano. Suka isheta da shewa suna tambayar ya amarci. Ta biyemusu da dariya, koda suka tambayi mijin, sai cewa tayi gashinan yana mata tausa. Nan aka dauki dariya har da masu turo Audio. Kai Bintu ta rasa inda zata sanya ranta don dad'i. Ashe dai wataran zata ga amfanin chatting? Haka tayi ta biyemusu tana darawa.
Shima Ma'aruf bai k'ara bi ta kanta ba. Misalin tara ta ajiye wayar ta fito. Fitilun a kashe, sai hasken tv saidai waya yakeyi. Ta fahimci da abokin aikinsa yake yinta, ta wuce zuwa kicin domin d'aukar ruwa. Bayan ta fito ne yayi mata nuni da hannu wato ta kwashe kayan abinci. Kamar bazata tsaya ba, sai kuma dai ta dawo da baya. Yana wayan yana binta da kallo sakamakon hasken tv da ya hasketa. Ita kuwa kamar tasan yana kallonta ta wuce tana wata rausaya wacce da gayya ta yi ta.
Ai kuwa har da d'an mik'ewa zaune. Tuni kuma ya soma mance bayanin da sukeyi ta wayar. Ta gabansa ta shige da robar ruwa a hannunta.
Ajiyar zuciya yayi, ya runtse ido. Dole ya yiwa abokin aikinsa sallama ya tattara ya kashe kayan kallo ya fad'a d'akinsa. Yarinyar nan zai gargad'eta, don bazai lamunci ta dunga yi mishi yawo da duk suturun da ta so ba acikin gidannan.
* * *
Ita kuwa shigarta d'aki ta chanja zuwa kayan bacci doguwar riga mai d'an kauri saidai da kad'an ta wuce gwuiwarta, bata da nauyi. Daga haka ta kashe fitila ta kunna (gwamna ya gaza..lol)ta hau whatsapp bayan tayi male-male asaman gadonta. Kai tsaye group na matan aure ta lek'a, nan ta soma cin karo da sirrika kala-kala da akeson duk mace ta iya ta kuma sansu. Ta soma karantawa tiryan-tiryan. Ajiyar zuciya kawai ta saki, wai ana nufin itama zata iya yiwa Ma'aruf? Ta runtse ido ta bud'e, kai bata fatan har mutuwar aurensu wani abin ma ya had'asu. Ta yarda akwai sha'awa a rayuwa, soyayya ce dai ta kasa gaskatawa yana faruwa domin acewarta ita bai ta6a kamata ba.
"Toh idan kuma kika soma son Yaya Ma'aruf fa?"
Cewar wata zuciyarta. Ta ja wani iri. Kai Allah ma bazai jarabceta da wannan ba in sha Allah. Me zata so a wajen mutumin da baya sonta?
"Ni mugani ma ko yana online."
Ta fad'a a fili sannan ta hau lalube contacts. Baya online, hotonsa ta gani a dp hakan yasa ta bud'owa. Saida ta furta "Wow" a fili tun bata kai ga k'arewa hoton kallo ba.
[7/20, 10:42 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<33>>
Ta bud'o hoton tana kalla. Yana zaune cikin motarsa a mazaunin direba. Ya juyo har da wani tankwashe k'afafu, hannunsa na dama dafe da ha6arsa yana murmushi har da wani k'ank'ance idanu. Ya gama had'ewa cikin lemon-green na shadda ta sha aiki. Farar hula ce mai adon lemon-green a saman kansa. Ta bishi da kallon tsaf, tasan yanada kyau, bayan wannan ma, yana da wasu nagarta na mutunci da yake nunawa jama'a da dukkan wad'anda yakeso kad'ai, amma idan bai k'aunar mutum, to fa anan ka shiga uku. (Atunanin Bintu kenan).
Sai kuma ta tsinci kanta da fad'awa kogin tunanin wanda ya d'aukeshi hoton. Ta k'urawa hoton ido, anan ta gane alokacin Ma'aruf da k'ibarsa wuyansa a cike ba kamar yanzun da ya rame ba. Hoton zai dan kwana biyu da alamu. To kodai Hashim ya d'aukeshi? Sai kuma ta girgiza kai, ba zai kashewa Hashim idanu haka ba. Ta yi jim, sai kuma ta ja tsaki ta kashe wayarta. Me zai sanya ta damu kanta da tunanin abinda bai dameta ba. Ta lumshe ido a haka bacci yayi awon gaba da ita.
Abinda ya bata mamaki bai wuce yanda tayi mafarkin Yaya Ma'aruf ba, wai gashinan ta tsareshi da tambayar wacce ta daukeshi hoto har ya kawo mata duka.
Koda ta farka, sai mafarkin ma ya bata dariya da haushi. Lallai jiya ta ci ta k'oshi.
Washegari ya kama asabar babu makaranta, wannan yasa dukkansu babu wanda ya taka waje. Lokacin k'arfe sha biyu na rana ta kusa saidai Ma'aruf ko falon bai lek'o ba, haka itama Bintu, tana kammala gyare-gyaranta ta koma d'aki abinta ganin bai tashi ba ballantana ta gyara.
Sai wajejan sha biyu da rabi ta ji fitowarsa falon. Anan kuma ta ji yana kwala mata kira. Ta ajiye wayar da take dannawa ta fito.
Yana zaune ya hard'e kafafunsa a saman tebur, yayi wankansa yana sanye cikin riga ja da wando fari na jeans. Kallo d'aya yayi mata ya had'e rai. "Wai ban hanaki yin shiga anyhow a gidannan bane?"
Ta dubeshi sannan ta dubi abinda ke a jikinta. Doguwar riga ce 'yar kanti saidai tana da fiddo halitta kwarai. Ta turo baki kad'an sannan ta zauna tana dubansa kad'an.
"Wallahi Yaya kaima kasan manyan kaya suna takuramin a rayuwa. Ko a gida bana sanyawa."
Ya furzar da iska kawai, bazai iya fitowa ya sanarmata dalilinsa ba. Shi kansa yana jin ma kunyar tuna wai surar yarinyar da ya raina ke d'an hargitsa shi ba.
"Kawomin breakfast."
Ta saci kallonsa tayi murmushi lokacin da ta mik'e. Ai tasan manufarsa ta hanata sanyawa. Ita fa ba yarinya bace. Tana shiga kicin tayi kwafa.
"Lallai zakayi ka bari." Ta ayyana a ranta. Ta k'udurta a ranta ba zata bar shiga irin yanda ta so ba don ko a can gida ma bata fasa ba.
Ta had'omishi kayan kari ta fito. Ya sauke k'afarsa saman teburin ta ajiye sannan ta koma ta zauna. Ya d'an dubeta kawai ya basar, ya soma k'ok'arin had'a tea.
"Yaya, baka kewar Hanif? Don Allah ka rok'i Mami su dawo nan."
Ya d'an ji sanyi a ransa. Kamar bazai amsa ba sai kuma yayi magana.
"Munyi magana da ita jiya, zan iya tahowa da shi a yau."
Haba Bintu ta hau murna har tana washe hak'ora.
Yana lura da yanda tayita faman shige da fice, daga d'akin da Ma'aruf ya tanada don d'anshi kad'ai wanda aka k'awata da kwalliya da ya kamatu a d'akin yaro. Can kuma sai ta nufi kicin ta d'auko duster ta goge. Kallonta kawai yakeyi, hakanan kuma ya ji ta burgeshi. Yana so yaga ana son d'ansa Hanif. D'an soyayya kenan. Bintu kuwa, a wannan 6angaren ya tabbatar ba shi da matsala ko kad'an da ita. Tana son d'anshi.
Yana kammalawa ya fice gidan. Sai wajejan biyar na yamma Aisha ke tabbatar mata yazo ya taho da Hanif, zuwa lokacin ya sallami Atine da goma ta arziki, Atine har kuka tayi saboda murna.
Ai kuwa nan Bintu na jin sun taho ta mik'e ta fad'a kicin, har ta kammala tuk'a tuwon semovita miyar ku6ewa babu labarinsu.
Can kuma sai ta ji k'arar bud'e gate wanda ya bata tabbacin shine.
Ta bud'e k'ofar, bayan yayi fakin ya fito yana rik'e da Hanif a hannu. Yaron ya k'ara narka uban k'iba, ya k'ara wayo. Ga shi fari k'al da shi kamar mahaifinsa. A kammani kuwa, zuwa yanzu sai ka kasa bambance kamannin wanda yafi rinjaye, tsakanin babansa da mamarsa.
Sunayin sallama ta amsa da saurinta ta kar6i Hanif ta cillashi sama ta cafe tana dariya. Shima Hanif d'in ganin haka ya kyalkyale da dariya. Tuni ta juya ciki tana fad'in.
"Oyoyo d'an Mami."
Ya shigo da 'yar jakar Hanif ya rufe k'ofar. Kallonsu yakeyi domin kuwa alal hakika sun burgeshi. Yana zama ta dauki jakar yaron sukayi d'aki. Ya shafi sumarsa yana murmushi, lallai Bintu ba k'aramin so take yiwa Hanif ba
[7/21, 9:23 AM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Ta kammala tsaf ta zubo nata a filet bayan ta bar mishi nashi cikin flask. Kasancewar ba sallar takeyi ba, yasa ta zaman cin abincinta.
Ta soma ci kenan tana kallon wata tasha da ke hasko wrestling. A haka ya fito da zummar tafiya masallaci. Yayi mata kallo d'aya ya cigaba da tafiyarsa baice uffan ba. Ta bishi da kallo, wataran rashin son yawan magana irin na Ma'aruf yakan bata mamaki matuk'a. Kodayake daman bashi da hayaniya, bar shi dai da son girma. D'an hayaniya sai mutuminta, Yaya Rufa'i.
Bayan ya dawo ya zauna a falon alokacin ta kusa kammala cin abincin. Ya dubi abinda take kallo sannan ya dubeta.
"Bani remote."
Ta narke fuska.
"Yaya don Allah ka bari na gama kallo."
Ya yamutse fuska batare da ya dubeta ba don baya buk'atar cigaba da dubannata saboda dalilai.
"A matan ma bansan sunan da zan baki ba, me mace zatayi da wrestling idan na rashin abin yi ba? Malama bani na kalli abinda zai fissheni."
Ta mik'a mishi remote d'in ta d'auki filet tayi hanyar kicin ganin ya kamo Aljazeera. Daman ai ba yau suka soma fad'a akan tashar kallo ba.
"Ina abincina?" Bata ko juyo ba ballantana ta dubeshi ta amsa.
"Yana kicin."
"Kawomin."
Ta had'o mishi komai ta ajiye, zama tayi gami da janyo wayarta.
"Malama tashi ki suturta jikinki kafin zuciyata ta tashi."
Wani gululun bakinciki ya turnuk'eta, kai bafa zata amince da wannan cin fuskar ba. Dole ne tayi maganin Yayan nan.
Ta fasa zaman falon ta koma d'aki. Batasan sadda ta soma hawaye ba, kewar Maminta da Aisharta suka mamayeta. Yanzu da ace tana gaban Mami da duk wani abu da zai mata ba dai yayi a gabanta ba. Gashi kuma babu damar kai k'ara, to tace me? Alhalin ta riga ta nunawa Aisha komai lafiya ke tafiya tsakani. Ganin zata sanyawa ranta damuwar babu gaira babu dalili ne yasa ta janyo wayarta. Whatsapp ta soma k'ok'arin downloading, a baya sam bata chatting, tana ganin yanda Aisha ke haukar karanta books da kutsawa groups na matan aure amma ita ko a jikinta. Wannan karon kam, tayi niyyar somawa don ya d'ebemata kewa.
Bayan ta gama downloading, ya kammala updating contacts dinta da komai. Bata d'ora hotonta ba, tabar wajen fayau.
Dad'i ya cikata ganin Aisha online, hakanan da yawa daga cikin 'yan uwansu na Rano da 'yan uwan Abban Aisha ma duk sunayi. Kai tsaye ta yiwa Aisha magana. Aisha harda 'yar rawarta na murnar ganinta. Nan ta sanyata a groups, na matan auren ma ta sanya (Admin) ta sanyata ciki.
Nan ta soma ganin abubuwa, saidai tafi maida hankali a na 'yanuwansu na Rano. Suka isheta da shewa suna tambayar ya amarci. Ta biyemusu da dariya, koda suka tambayi mijin, sai cewa tayi gashinan yana mata tausa. Nan aka dauki dariya har da masu turo Audio. Kai Bintu ta rasa inda zata sanya ranta don dad'i. Ashe dai wataran zata ga amfanin chatting? Haka tayi ta biyemusu tana darawa.
Shima Ma'aruf bai k'ara bi ta kanta ba. Misalin tara ta ajiye wayar ta fito. Fitilun a kashe, sai hasken tv saidai waya yakeyi. Ta fahimci da abokin aikinsa yake yinta, ta wuce zuwa kicin domin d'aukar ruwa. Bayan ta fito ne yayi mata nuni da hannu wato ta kwashe kayan abinci. Kamar bazata tsaya ba, sai kuma dai ta dawo da baya. Yana wayan yana binta da kallo sakamakon hasken tv da ya hasketa. Ita kuwa kamar tasan yana kallonta ta wuce tana wata rausaya wacce da gayya ta yi ta.
Ai kuwa har da d'an mik'ewa zaune. Tuni kuma ya soma mance bayanin da sukeyi ta wayar. Ta gabansa ta shige da robar ruwa a hannunta.
Ajiyar zuciya yayi, ya runtse ido. Dole ya yiwa abokin aikinsa sallama ya tattara ya kashe kayan kallo ya fad'a d'akinsa. Yarinyar nan zai gargad'eta, don bazai lamunci ta dunga yi mishi yawo da duk suturun da ta so ba acikin gidannan.
* * *
Ita kuwa shigarta d'aki ta chanja zuwa kayan bacci doguwar riga mai d'an kauri saidai da kad'an ta wuce gwuiwarta, bata da nauyi. Daga haka ta kashe fitila ta kunna (gwamna ya gaza..lol)ta hau whatsapp bayan tayi male-male asaman gadonta. Kai tsaye group na matan aure ta lek'a, nan ta soma cin karo da sirrika kala-kala da akeson duk mace ta iya ta kuma sansu. Ta soma karantawa tiryan-tiryan. Ajiyar zuciya kawai ta saki, wai ana nufin itama zata iya yiwa Ma'aruf? Ta runtse ido ta bud'e, kai bata fatan har mutuwar aurensu wani abin ma ya had'asu. Ta yarda akwai sha'awa a rayuwa, soyayya ce dai ta kasa gaskatawa yana faruwa domin acewarta ita bai ta6a kamata ba.
"Toh idan kuma kika soma son Yaya Ma'aruf fa?"
Cewar wata zuciyarta. Ta ja wani iri. Kai Allah ma bazai jarabceta da wannan ba in sha Allah. Me zata so a wajen mutumin da baya sonta?
"Ni mugani ma ko yana online."
Ta fad'a a fili sannan ta hau lalube contacts. Baya online, hotonsa ta gani a dp hakan yasa ta bud'owa. Saida ta furta "Wow" a fili tun bata kai ga k'arewa hoton kallo ba.
[7/20, 10:42 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<33>>
Ta bud'o hoton tana kalla. Yana zaune cikin motarsa a mazaunin direba. Ya juyo har da wani tankwashe k'afafu, hannunsa na dama dafe da ha6arsa yana murmushi har da wani k'ank'ance idanu. Ya gama had'ewa cikin lemon-green na shadda ta sha aiki. Farar hula ce mai adon lemon-green a saman kansa. Ta bishi da kallon tsaf, tasan yanada kyau, bayan wannan ma, yana da wasu nagarta na mutunci da yake nunawa jama'a da dukkan wad'anda yakeso kad'ai, amma idan bai k'aunar mutum, to fa anan ka shiga uku. (Atunanin Bintu kenan).
Sai kuma ta tsinci kanta da fad'awa kogin tunanin wanda ya d'aukeshi hoton. Ta k'urawa hoton ido, anan ta gane alokacin Ma'aruf da k'ibarsa wuyansa a cike ba kamar yanzun da ya rame ba. Hoton zai dan kwana biyu da alamu. To kodai Hashim ya d'aukeshi? Sai kuma ta girgiza kai, ba zai kashewa Hashim idanu haka ba. Ta yi jim, sai kuma ta ja tsaki ta kashe wayarta. Me zai sanya ta damu kanta da tunanin abinda bai dameta ba. Ta lumshe ido a haka bacci yayi awon gaba da ita.
Abinda ya bata mamaki bai wuce yanda tayi mafarkin Yaya Ma'aruf ba, wai gashinan ta tsareshi da tambayar wacce ta daukeshi hoto har ya kawo mata duka.
Koda ta farka, sai mafarkin ma ya bata dariya da haushi. Lallai jiya ta ci ta k'oshi.
Washegari ya kama asabar babu makaranta, wannan yasa dukkansu babu wanda ya taka waje. Lokacin k'arfe sha biyu na rana ta kusa saidai Ma'aruf ko falon bai lek'o ba, haka itama Bintu, tana kammala gyare-gyaranta ta koma d'aki abinta ganin bai tashi ba ballantana ta gyara.
Sai wajejan sha biyu da rabi ta ji fitowarsa falon. Anan kuma ta ji yana kwala mata kira. Ta ajiye wayar da take dannawa ta fito.
Yana zaune ya hard'e kafafunsa a saman tebur, yayi wankansa yana sanye cikin riga ja da wando fari na jeans. Kallo d'aya yayi mata ya had'e rai. "Wai ban hanaki yin shiga anyhow a gidannan bane?"
Ta dubeshi sannan ta dubi abinda ke a jikinta. Doguwar riga ce 'yar kanti saidai tana da fiddo halitta kwarai. Ta turo baki kad'an sannan ta zauna tana dubansa kad'an.
"Wallahi Yaya kaima kasan manyan kaya suna takuramin a rayuwa. Ko a gida bana sanyawa."
Ya furzar da iska kawai, bazai iya fitowa ya sanarmata dalilinsa ba. Shi kansa yana jin ma kunyar tuna wai surar yarinyar da ya raina ke d'an hargitsa shi ba.
"Kawomin breakfast."
Ta saci kallonsa tayi murmushi lokacin da ta mik'e. Ai tasan manufarsa ta hanata sanyawa. Ita fa ba yarinya bace. Tana shiga kicin tayi kwafa.
"Lallai zakayi ka bari." Ta ayyana a ranta. Ta k'udurta a ranta ba zata bar shiga irin yanda ta so ba don ko a can gida ma bata fasa ba.
Ta had'omishi kayan kari ta fito. Ya sauke k'afarsa saman teburin ta ajiye sannan ta koma ta zauna. Ya d'an dubeta kawai ya basar, ya soma k'ok'arin had'a tea.
"Yaya, baka kewar Hanif? Don Allah ka rok'i Mami su dawo nan."
Ya d'an ji sanyi a ransa. Kamar bazai amsa ba sai kuma yayi magana.
"Munyi magana da ita jiya, zan iya tahowa da shi a yau."
Haba Bintu ta hau murna har tana washe hak'ora.
Yana lura da yanda tayita faman shige da fice, daga d'akin da Ma'aruf ya tanada don d'anshi kad'ai wanda aka k'awata da kwalliya da ya kamatu a d'akin yaro. Can kuma sai ta nufi kicin ta d'auko duster ta goge. Kallonta kawai yakeyi, hakanan kuma ya ji ta burgeshi. Yana so yaga ana son d'ansa Hanif. D'an soyayya kenan. Bintu kuwa, a wannan 6angaren ya tabbatar ba shi da matsala ko kad'an da ita. Tana son d'anshi.
Yana kammalawa ya fice gidan. Sai wajejan biyar na yamma Aisha ke tabbatar mata yazo ya taho da Hanif, zuwa lokacin ya sallami Atine da goma ta arziki, Atine har kuka tayi saboda murna.
Ai kuwa nan Bintu na jin sun taho ta mik'e ta fad'a kicin, har ta kammala tuk'a tuwon semovita miyar ku6ewa babu labarinsu.
Can kuma sai ta ji k'arar bud'e gate wanda ya bata tabbacin shine.
Ta bud'e k'ofar, bayan yayi fakin ya fito yana rik'e da Hanif a hannu. Yaron ya k'ara narka uban k'iba, ya k'ara wayo. Ga shi fari k'al da shi kamar mahaifinsa. A kammani kuwa, zuwa yanzu sai ka kasa bambance kamannin wanda yafi rinjaye, tsakanin babansa da mamarsa.
Sunayin sallama ta amsa da saurinta ta kar6i Hanif ta cillashi sama ta cafe tana dariya. Shima Hanif d'in ganin haka ya kyalkyale da dariya. Tuni ta juya ciki tana fad'in.
"Oyoyo d'an Mami."
Ya shigo da 'yar jakar Hanif ya rufe k'ofar. Kallonsu yakeyi domin kuwa alal hakika sun burgeshi. Yana zama ta dauki jakar yaron sukayi d'aki. Ya shafi sumarsa yana murmushi, lallai Bintu ba k'aramin so take yiwa Hanif ba
[7/21, 9:23 AM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)