Sashe 18
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
<<27>>
Biki fa ya kankama, sai shirye-shirye kawai mutanen gidan keyi. Mami babu zama, itace can itace nan. Bintu kallon kowa kawai takeyi da ido, gaba d'aya ta rame saboda bata ta6a kawowa a ranta zatayi aure nan kusa ba. Tuni aka kammala had'a lefe da kayan kunshi da komai da aka sani na al'ada aka rankaya Rano. To abu na gida, babu wanda bai taya Fatima Bintu murna ba, a k'arshe Inna da kanta tace a mayar can Kano, Mami ai itace uwar amarya ita kam ango ne na wajenta. Haka da dariya da komai 'yan uwan junan suka rabu. Ga ango da amaryar kuwa babu wanda zai saurin d'ago wani abu tsakaninsu. Aisha dai tuni ta harbo Bintu, saidai ta san komai zai wuce bayan aure. Babu abinda yafi k'ular da Bintu kamar yanda Ma'aruf ya soma nunawa lallai dagaske sonta yakeyi agaban 'yan uwa. Ta k'ulu iyakar k'uluwa ta tabbatar sabon salo ne ya d'auko domin k'untata mata ga shi a wannan ga6ar ta rasa abin da zai zame mata ramuwar gayya. Ganin bata da mafita yasa ta ke k'auracewa duk wajen da yake. Ta yankewa kanta shiga d'akin Hanif, hakanan ta rage zama falon Mami saidai ta shige k'uryar d'akinta tayi zamanta.
Ana sauran sati bikin ne, aka soma yiwa Bintu gyaran jiki, Mami ta tilasta ta sanya hijab da nik'ab idan zataje makaranta har ma da safa saboda kada rana ta 6ata gyaran da akeyi. Ana sauran kwana uku ne kuma ta daina zuwa makarantar acewar Mami ta bari a mik'ata d'akinta tunda ba jarabawa sukeyi ba.
Ana gobe za'a soma biki, suna zaune a d'akinsu ita da Aisha, da Hajara harma da Jalila da Atika(yanuwansu wadanda suke sa'anni, suna zama a Rano). Amarya Bintu ansha lalle da kitso siri-siri.
Hajara ta kama baki.
"Kai nifa nafi mamakin ramar da yarinyar nan keyi, daman akwai abinda zai ladabtar da Bintu haka? Kamar ba wannan shak'iyiyar ba."
Bintu ta kallera kawai saidai batace uffan ba. Su Aisha suka kwashe da dariya. Atika dake cin meatpie ta dubeta.
"Wallahi ni kunsan me yafi burgeni? Bai wuce yanda naga Yaya Ma'aruf ke nan nan da ita ba. Ku duba kugani, yana ganinta zakuga ya soma zolayarta da amaryata amaryata. Hum, wannan a gidansu akwai kallo."
Bintu ta harareta, me zasuyi ba dariya ba. Ta ja tsaki, kamar tayi magana, sai kuma ta fasa.
"Yi maganarki, yar duniyar k'arya kinaso kina kaiwa kasuwa. Kodayake kin gama ciki bakin ke bakya soyayya." Cewar Jalila.
Tsam ta mik'e ta koma wajensu Mami da iyayensu Atika wadanda suka kasance, 'ya'ya ga kishiyar uwar su Mamin. Nan kuwa babu mai tsokanarta saima hirarsu da sukeyi.
Washegari aka soma shagalin biki. Can na hango masu aikin abinci, ciki har da Fauza ga Ummu Abdool a gefenta suna ta juya farar shinkafa a k'atin warmer. A gefe ga dangin Taskira suna ta wanke kwanukan rabo. Can kuwa, Su hanne da Batool kai harma da Sholingaye ke faman kula da miya. Can na hango Bingel da Faharty na fad'a akan k'ashi ganin Bayarabiya Asal mai d'aukar bidiyo ta nufo wajensu ne ya sanyasu nutsuwa.
Kai group na matan aure suma sunyi gefe suna hirar yanda zata kaya a gidan amarya Bintu wacce suka gama had'ata suka suburbud'a mata lakcoci acan falon Mami.
Bintu ta sha kuka yanda manyan nan suka sanyata a tsaka suna faman yi mata maganganun da suka girmi kunnuwanta.
"Nidai gaskiya banason aure." Su Aisha suka kyalkyale da dariyar jin abinda ya fito daga bakinta.
Ango kuwa a yanzu ya share komai, ya lura a hakan da yake nunawa Bintu son k'arya idan sun ke6e kuma ya guma mata rashin mutunci.
Washegari misalin k'arfe goma na safe aka d'aura auren Fatima Bintu Muhammad da Ma'aruf Abdullahi...!!!
[7/19, 9:07 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<28>>
Idan kaga Bintu, ba zaka ce itace amaryar ba domin kuwa tun safe take kwance saman gadon Mami, daga ita sai Sadauki don su Aisha sun hanata zaman d'akin da zolayarsu, wannan yasa Mami ta lalla6ata zuwa d'akinta.
Har kuwa aka d'aura auren bata da niyyar motsawa daga saman gadon. Su Aisha sunason zuwa yi mata bud'i saidai Mami ta yi musu jan ido akan shiga inda take.
Kuka sosai takeyi, saida Mami ta yi da gaske kafin ta shawo kan Bintu. Babban abinda kuwa yasa jikin Bintun sanyi bai wuce tambayar da Mamin ta jefomata ba na cewa.
"Bintuna kodai bakyason yaron nan tilastawa zuciyarki kikayi?"
Wannan ne silar daina zubar hawayenta kafin ta nunawa Mami ba haka bane tana kaunarsa.
Bayan ta yi wankanta a d'akin Mami. Mami ta turo Hajara da Aisha domin taimakawa wajen shiryata kafin ango da abokansa su shigo bayan ta gargad'esu akan koda wasa kada su tsokaneta.
Aisha ta fente mata fuskarta. Yayinda Hajara ta fiddo mata abin buk'ata. Bintu ta fito tayi kyau fiye da zato, ta had'e cikin shadda fara mai golden surfani.
"Masha Allah!" Shine kad'ai abinda ke fitowa daga bakin Aisha da Hajara. Bintu dai ta bisu da ido kawai, ita kanta tasan ta had'u k'arshe. Fatarta ta k'ara murjewa tayi haske sakamakon gyaran da ta sha a kwanakin nan.
"Wai ina amaryar ne?" Cewar wata gwaggonsu ta Rano lokacin da ta sanyo kai d'akin tare da sauran tsoffin. Har tsakar kan Bintu ta iso ta sakar mata bud'a.
"Ayuiririii!"
Haka sukayi mata ca, banda haushinsu babu abinda takeji. Suka ja ta har tsakar falon Mami aka zaunar da ita saman kujera, tuni ta soma ruwan hawaye Aisha ta taimakawa wajen sharemata har itama tana tayata hawayen. Bata ta6a jin tausayin 'yar uwartata ba akan lamarin auren sai yanzu, da kuma tunanin rabuwar da zasuyi, daga yau shikenan bazata k'ara kwana tare da ita ba. Babu abinda ta tunano sai shak'uwarsu da yanda take rayamusu gidan da wasa da dariyarta. Allah Sarki rayuwa.
Can kuma sukaji shewar ta juya baya. Ana fad'in ga ango! Ga ango!
Har da abokansa kuwa. Yana sanye cikin dakakkiyar shadda fara k'al, sai shek'i yakeyi. Lallausan sajensa ya kwanta luf-luf. Ya had'u har ya gaji, kallo d'aya zakayi kwayar idanunsa ka fahimci lallai ya yi kuka sakamakon kad'awar da sukayi, ba kuwa don komai ba sai don tunano matarsa wacce k'aunarta ko kad'an bai ta6a raguwa ba a zuciyarsa. A yau da aka d'aura aurensa da Fatima Bintu, sai ya ji zuciyarsa tamkar anyi mishi fami. Haka suka kammala gaisawa da dangi, yana shirin ficewa wata abokiyar wasanshi ta janyoshi.
"A'a ango ya zakayi mana haka. Zo nan ka zauna sai fa anyi muku hoton tarihi."
Wajen akayi dariya. Bintu zata mik'e sai kuma wata ta maidata ta zaunar.
"Zauna, ina zaki gudu? Ke kuma matsa kin zauna kina taya 6era 6ari, kema muna dab da aurar da ke."
Aisha ta matsa tana k'unk'uni. Daidai lokacin kuma aka zaunar da Ma'aruf a gefenta. Kusan lokaci guda gabansu ya fad'i, k'amshin turaren kowannensu ya bugi hancinsu. Ta muskuta ta ja gefe cike da jin haushin wad'annan matan.
Abin haushi suka bud'emata lullu6i wai za'ayi hoto. Dakyar ta bari akayi d'aya duk ranta a k'untace kafin da gudunta ta kutsa ta fad'a d'akin Hanif kasancewar yafi kusa da inda take. Ma'aruf ko murmushi kawai yayi wanda shi kad'ai yasan ma'anarsa.
Haka akayita hotuna da ango da abokansa. K'arshe akayimai da d'ansa fin kala biyar.
Bayan Magrib kuwa aka soma shirin tafiya Dinner party wanda Mami ta shirya.
Anan kuwa Bintu bata bayar da matsala ba, sosai ta ji fad'an Maminta. Ta gama had'ewa cikin gown lace ne mai adon golden da fari. Ta d'ora golden head sai 'yar jaka had'e da takalminsa da na mayafi.
Su Aisha da sauran abokan karatunsu na sakandire da jami'a sai 'yan uwa sun yi ankonsu suma sun fito d'as cikin golden lace, yayinda mazan sukayi ankon farin boyel.
Mami ta shigo ta d'ago ha6ar Bintu tana dubanta. Murmushi ta saki.
"Masha Allah, Allah Ya kauda idanun mak'iya akanki my daughter. Kinyi kyau, sai ki k'ara kame kanki banason rawa kinji ko?"
Bintu ta amsa kawai da to. Ina ta ga wani dama ta yin rawa a auren da ba wani so da d'aukinsa take ba?
Aisha ce tayi mata rakiya har motar angon. Ta saci kallon motar. Baka ganin wanda ke ciki, hakan yasa ta maida kanta k'asa. Kafin su k'arasa Bintu ta ja tsaki.
"Wallahi taraku nakeyi daga ke har su Anti Hajaran, zan rama d'aya bayan d'aya."
Jin abinda ta furta yasa Aisha darawa.
"Ashe fa d'an iska d'an iska ne ko? Oho dai, kafin kiyi mana ke muka soma yiwa."
Bintu ta yi kwafa.
"Lokaci."
Daga haka bata k'ara cewa uffan ba tana jin dariyar Aisha.
Aisha ta bud'e mata k'ofar ta shiga, wani sanyi ya ratsata had'e da k'amshi. Ta dubi gefenta, ajiyar zuciya ta saki ta kauda fuskarta. Ai 6ata lokaci ne ma idan tace yayi kyau, daman kyakkyawan ne. Saidai a yau kowa ya ganshi zai k'ara son ya k'ara kalla banda ita Bintun. Acewar zuciyarta kenan.
Muryar Hashim dake zaune wajen direba ya katse tunaninta.
"Ina gaisuwa amarsu."
Ta daure ta gaisheshi cikin sassanyar muryar da ya ba shi mamaki, ya saba jin Bintu da karad'i, bata da wani sanyi. Ya dai basar ta hanyar dariya kafin ya amsa ya had'a da fatan alheri. Bata amsa ba, alokacin kuma ya ja motar.
Shiru ya biyo baya. Can kuma ta ji wayarta ta d'auki k'ara. Ta ciro ta duba. Text message ne daga unknown number. Ta bud'o ta karanta.
"Kin ci nasarar zama matata, ina tayaki murna, fatan baki mance dukkan maganganun da na yi miki a baya ba?"
Ta dubeshi kad'an bayan ta kammala, wani shu'umin murmushi ya sakarmata mai k'ara sanya yanmata matowa a kansa. Ta kauda kanta, abin da ya ba shi mamaki ganin batayi niyyar ba shi amsa ba, k'arshe ma ta kashe wayar gaba d'aya ta jefa jaka.
Hashim ya danna rediyo nan kuma kid'a ya soma tashi jin da yayi shirun na motar ya isa. Haka har suka isa babu wanda ya k'ara cewa wani uffan sai shi da Hashim da ke d'an ta6a hira.
[7/19, 9:07 PM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<29>>
Biki fa ya kankama, sai shirye-shirye kawai mutanen gidan keyi. Mami babu zama, itace can itace nan. Bintu kallon kowa kawai takeyi da ido, gaba d'aya ta rame saboda bata ta6a kawowa a ranta zatayi aure nan kusa ba. Tuni aka kammala had'a lefe da kayan kunshi da komai da aka sani na al'ada aka rankaya Rano. To abu na gida, babu wanda bai taya Fatima Bintu murna ba, a k'arshe Inna da kanta tace a mayar can Kano, Mami ai itace uwar amarya ita kam ango ne na wajenta. Haka da dariya da komai 'yan uwan junan suka rabu. Ga ango da amaryar kuwa babu wanda zai saurin d'ago wani abu tsakaninsu. Aisha dai tuni ta harbo Bintu, saidai ta san komai zai wuce bayan aure. Babu abinda yafi k'ular da Bintu kamar yanda Ma'aruf ya soma nunawa lallai dagaske sonta yakeyi agaban 'yan uwa. Ta k'ulu iyakar k'uluwa ta tabbatar sabon salo ne ya d'auko domin k'untata mata ga shi a wannan ga6ar ta rasa abin da zai zame mata ramuwar gayya. Ganin bata da mafita yasa ta ke k'auracewa duk wajen da yake. Ta yankewa kanta shiga d'akin Hanif, hakanan ta rage zama falon Mami saidai ta shige k'uryar d'akinta tayi zamanta.
Ana sauran sati bikin ne, aka soma yiwa Bintu gyaran jiki, Mami ta tilasta ta sanya hijab da nik'ab idan zataje makaranta har ma da safa saboda kada rana ta 6ata gyaran da akeyi. Ana sauran kwana uku ne kuma ta daina zuwa makarantar acewar Mami ta bari a mik'ata d'akinta tunda ba jarabawa sukeyi ba.
Ana gobe za'a soma biki, suna zaune a d'akinsu ita da Aisha, da Hajara harma da Jalila da Atika(yanuwansu wadanda suke sa'anni, suna zama a Rano). Amarya Bintu ansha lalle da kitso siri-siri.
Hajara ta kama baki.
"Kai nifa nafi mamakin ramar da yarinyar nan keyi, daman akwai abinda zai ladabtar da Bintu haka? Kamar ba wannan shak'iyiyar ba."
Bintu ta kallera kawai saidai batace uffan ba. Su Aisha suka kwashe da dariya. Atika dake cin meatpie ta dubeta.
"Wallahi ni kunsan me yafi burgeni? Bai wuce yanda naga Yaya Ma'aruf ke nan nan da ita ba. Ku duba kugani, yana ganinta zakuga ya soma zolayarta da amaryata amaryata. Hum, wannan a gidansu akwai kallo."
Bintu ta harareta, me zasuyi ba dariya ba. Ta ja tsaki, kamar tayi magana, sai kuma ta fasa.
"Yi maganarki, yar duniyar k'arya kinaso kina kaiwa kasuwa. Kodayake kin gama ciki bakin ke bakya soyayya." Cewar Jalila.
Tsam ta mik'e ta koma wajensu Mami da iyayensu Atika wadanda suka kasance, 'ya'ya ga kishiyar uwar su Mamin. Nan kuwa babu mai tsokanarta saima hirarsu da sukeyi.
Washegari aka soma shagalin biki. Can na hango masu aikin abinci, ciki har da Fauza ga Ummu Abdool a gefenta suna ta juya farar shinkafa a k'atin warmer. A gefe ga dangin Taskira suna ta wanke kwanukan rabo. Can kuwa, Su hanne da Batool kai harma da Sholingaye ke faman kula da miya. Can na hango Bingel da Faharty na fad'a akan k'ashi ganin Bayarabiya Asal mai d'aukar bidiyo ta nufo wajensu ne ya sanyasu nutsuwa.
Kai group na matan aure suma sunyi gefe suna hirar yanda zata kaya a gidan amarya Bintu wacce suka gama had'ata suka suburbud'a mata lakcoci acan falon Mami.
Bintu ta sha kuka yanda manyan nan suka sanyata a tsaka suna faman yi mata maganganun da suka girmi kunnuwanta.
"Nidai gaskiya banason aure." Su Aisha suka kyalkyale da dariyar jin abinda ya fito daga bakinta.
Ango kuwa a yanzu ya share komai, ya lura a hakan da yake nunawa Bintu son k'arya idan sun ke6e kuma ya guma mata rashin mutunci.
Washegari misalin k'arfe goma na safe aka d'aura auren Fatima Bintu Muhammad da Ma'aruf Abdullahi...!!!
[7/19, 9:07 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<28>>
Idan kaga Bintu, ba zaka ce itace amaryar ba domin kuwa tun safe take kwance saman gadon Mami, daga ita sai Sadauki don su Aisha sun hanata zaman d'akin da zolayarsu, wannan yasa Mami ta lalla6ata zuwa d'akinta.
Har kuwa aka d'aura auren bata da niyyar motsawa daga saman gadon. Su Aisha sunason zuwa yi mata bud'i saidai Mami ta yi musu jan ido akan shiga inda take.
Kuka sosai takeyi, saida Mami ta yi da gaske kafin ta shawo kan Bintu. Babban abinda kuwa yasa jikin Bintun sanyi bai wuce tambayar da Mamin ta jefomata ba na cewa.
"Bintuna kodai bakyason yaron nan tilastawa zuciyarki kikayi?"
Wannan ne silar daina zubar hawayenta kafin ta nunawa Mami ba haka bane tana kaunarsa.
Bayan ta yi wankanta a d'akin Mami. Mami ta turo Hajara da Aisha domin taimakawa wajen shiryata kafin ango da abokansa su shigo bayan ta gargad'esu akan koda wasa kada su tsokaneta.
Aisha ta fente mata fuskarta. Yayinda Hajara ta fiddo mata abin buk'ata. Bintu ta fito tayi kyau fiye da zato, ta had'e cikin shadda fara mai golden surfani.
"Masha Allah!" Shine kad'ai abinda ke fitowa daga bakin Aisha da Hajara. Bintu dai ta bisu da ido kawai, ita kanta tasan ta had'u k'arshe. Fatarta ta k'ara murjewa tayi haske sakamakon gyaran da ta sha a kwanakin nan.
"Wai ina amaryar ne?" Cewar wata gwaggonsu ta Rano lokacin da ta sanyo kai d'akin tare da sauran tsoffin. Har tsakar kan Bintu ta iso ta sakar mata bud'a.
"Ayuiririii!"
Haka sukayi mata ca, banda haushinsu babu abinda takeji. Suka ja ta har tsakar falon Mami aka zaunar da ita saman kujera, tuni ta soma ruwan hawaye Aisha ta taimakawa wajen sharemata har itama tana tayata hawayen. Bata ta6a jin tausayin 'yar uwartata ba akan lamarin auren sai yanzu, da kuma tunanin rabuwar da zasuyi, daga yau shikenan bazata k'ara kwana tare da ita ba. Babu abinda ta tunano sai shak'uwarsu da yanda take rayamusu gidan da wasa da dariyarta. Allah Sarki rayuwa.
Can kuma sukaji shewar ta juya baya. Ana fad'in ga ango! Ga ango!
Har da abokansa kuwa. Yana sanye cikin dakakkiyar shadda fara k'al, sai shek'i yakeyi. Lallausan sajensa ya kwanta luf-luf. Ya had'u har ya gaji, kallo d'aya zakayi kwayar idanunsa ka fahimci lallai ya yi kuka sakamakon kad'awar da sukayi, ba kuwa don komai ba sai don tunano matarsa wacce k'aunarta ko kad'an bai ta6a raguwa ba a zuciyarsa. A yau da aka d'aura aurensa da Fatima Bintu, sai ya ji zuciyarsa tamkar anyi mishi fami. Haka suka kammala gaisawa da dangi, yana shirin ficewa wata abokiyar wasanshi ta janyoshi.
"A'a ango ya zakayi mana haka. Zo nan ka zauna sai fa anyi muku hoton tarihi."
Wajen akayi dariya. Bintu zata mik'e sai kuma wata ta maidata ta zaunar.
"Zauna, ina zaki gudu? Ke kuma matsa kin zauna kina taya 6era 6ari, kema muna dab da aurar da ke."
Aisha ta matsa tana k'unk'uni. Daidai lokacin kuma aka zaunar da Ma'aruf a gefenta. Kusan lokaci guda gabansu ya fad'i, k'amshin turaren kowannensu ya bugi hancinsu. Ta muskuta ta ja gefe cike da jin haushin wad'annan matan.
Abin haushi suka bud'emata lullu6i wai za'ayi hoto. Dakyar ta bari akayi d'aya duk ranta a k'untace kafin da gudunta ta kutsa ta fad'a d'akin Hanif kasancewar yafi kusa da inda take. Ma'aruf ko murmushi kawai yayi wanda shi kad'ai yasan ma'anarsa.
Haka akayita hotuna da ango da abokansa. K'arshe akayimai da d'ansa fin kala biyar.
Bayan Magrib kuwa aka soma shirin tafiya Dinner party wanda Mami ta shirya.
Anan kuwa Bintu bata bayar da matsala ba, sosai ta ji fad'an Maminta. Ta gama had'ewa cikin gown lace ne mai adon golden da fari. Ta d'ora golden head sai 'yar jaka had'e da takalminsa da na mayafi.
Su Aisha da sauran abokan karatunsu na sakandire da jami'a sai 'yan uwa sun yi ankonsu suma sun fito d'as cikin golden lace, yayinda mazan sukayi ankon farin boyel.
Mami ta shigo ta d'ago ha6ar Bintu tana dubanta. Murmushi ta saki.
"Masha Allah, Allah Ya kauda idanun mak'iya akanki my daughter. Kinyi kyau, sai ki k'ara kame kanki banason rawa kinji ko?"
Bintu ta amsa kawai da to. Ina ta ga wani dama ta yin rawa a auren da ba wani so da d'aukinsa take ba?
Aisha ce tayi mata rakiya har motar angon. Ta saci kallon motar. Baka ganin wanda ke ciki, hakan yasa ta maida kanta k'asa. Kafin su k'arasa Bintu ta ja tsaki.
"Wallahi taraku nakeyi daga ke har su Anti Hajaran, zan rama d'aya bayan d'aya."
Jin abinda ta furta yasa Aisha darawa.
"Ashe fa d'an iska d'an iska ne ko? Oho dai, kafin kiyi mana ke muka soma yiwa."
Bintu ta yi kwafa.
"Lokaci."
Daga haka bata k'ara cewa uffan ba tana jin dariyar Aisha.
Aisha ta bud'e mata k'ofar ta shiga, wani sanyi ya ratsata had'e da k'amshi. Ta dubi gefenta, ajiyar zuciya ta saki ta kauda fuskarta. Ai 6ata lokaci ne ma idan tace yayi kyau, daman kyakkyawan ne. Saidai a yau kowa ya ganshi zai k'ara son ya k'ara kalla banda ita Bintun. Acewar zuciyarta kenan.
Muryar Hashim dake zaune wajen direba ya katse tunaninta.
"Ina gaisuwa amarsu."
Ta daure ta gaisheshi cikin sassanyar muryar da ya ba shi mamaki, ya saba jin Bintu da karad'i, bata da wani sanyi. Ya dai basar ta hanyar dariya kafin ya amsa ya had'a da fatan alheri. Bata amsa ba, alokacin kuma ya ja motar.
Shiru ya biyo baya. Can kuma ta ji wayarta ta d'auki k'ara. Ta ciro ta duba. Text message ne daga unknown number. Ta bud'o ta karanta.
"Kin ci nasarar zama matata, ina tayaki murna, fatan baki mance dukkan maganganun da na yi miki a baya ba?"
Ta dubeshi kad'an bayan ta kammala, wani shu'umin murmushi ya sakarmata mai k'ara sanya yanmata matowa a kansa. Ta kauda kanta, abin da ya ba shi mamaki ganin batayi niyyar ba shi amsa ba, k'arshe ma ta kashe wayar gaba d'aya ta jefa jaka.
Hashim ya danna rediyo nan kuma kid'a ya soma tashi jin da yayi shirun na motar ya isa. Haka har suka isa babu wanda ya k'ara cewa wani uffan sai shi da Hashim da ke d'an ta6a hira.
[7/19, 9:07 PM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<29>>