Sashe 23
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
<<34>>
Bintu fa ansamu abokin hira. Ai kuwa bata fito falon nan ba sai bayan sun gama wasa da Hanif. Tayi mishi wanka ta chanja mishi kaya bayan ta shafa mishi hoda a jikinsa da fuskarsa, sannan ta sanyamishi riga da wando jikin cotton, na baccinsa. Ta dubeshi tana dariya irin wacce ake yiwa yaro na wasa.
"Inye, kaga bebina yayi kyau. Zo muje falo muci abinci."
Ta d'aukeshi, yana rik'e da d'an ball sai ihu yakeyi yana sanya bakinsa a jiki. Tayi mamakin ganin Ma'aruf zaune saman carpet ga filet a gabansa har ya kammala cin abinci ma. Ya hard'e k'afa yana kallon The Dr's a Mbc4. Ganinsu ya sanyashi juyowa. Nan ya mik'awa yaronsa hannu yana murmushi.
"Come to me my boy."
Bintu ta dire mishi yaron sannan ta d'auki filet tayi kicin. Jimawa kad'an sai gatanan ta fito rik'e da faranti itama ta zubo tuwo. Ta ajiye ta koma ta d'auko ruwan roba saboda Hanif, marar sanyi. Itama ta d'aukowa kanta pure water mai d'an sanyi-sanyi.
Ta dawo ta zauna.
"Zo mu ci abinci." Ma'aruf ya tankwashe k'afafu.
"Juyo da abincin nan zan ba shi."
Ta dubeshi, kai har takan yi mamakin irin wannan so da yake yiwa d'ansa. Ba musu ta juyo da filet din. Tana ci a yangance ne saboda wai tana gaban miji, ta ji ance ba'ason yin loma babba. A gida ma bata fiye yi a gabansa ba saboda tsoron fad'ansa, da dai Rufa'i ne, to shi kam babu kalar lomarta da baisani ba.
Bayan ta kammala ta ja baya tana shan ruwa.
"D'aukomin tissue a d'aki." Ta mike zuwa d'akin. Ta k'ara k'arewa d'akin kallo tamkar bak'onta. Zata d'auko ne, ta hangi BlackBerry dinsa da ke jone a chaji tana faman (vibrating) alamun dai kira ya shigo. Ta nufi wayar ta duba.
"Lawisa" Shine sunan da ta gani kawai, babu wani sakaye. Ai kuwa bata manceta ba, k'awar Yaya Abida yayar Ma'u dake yawon zuwa gidansu neman soyayyar Ma'aruf tana fakewa da duba d'ansa. Ta rik'e k'ugu, yau zatayi maganin shegiya ashe. Ta d'aga.
"Hello." Bintu tayi shiru. Sa'a ta k'ara magana.
"Haba Ma'aruf, so fa ba hauka bane da zaka dunga wulakantani, don kayi aure shikenan sai kuma ka daina kulani gaba d'aya. Me zakayi da yarinya wacce batasan rayuwa ba?"
"Uwarki da ubanki zaiyi dani."
Cewar Bintu a zuciye. Lawisa tayi shiru kafin tace.
"Ni zaki yiwa rashin kunya? Ina mai wayar?"
Bintu ta dubi k'ofa babu alamun mutum, ta cigaba da magana a hankali.
"Ya shiga wankan sunnah. Ke wai bakyajin kunya ne Lawisa, don yau bazan kiraki antin ba. Babba dake, iskancinki ya rasa kan wa zai fad'a sai tatta6a kunnenki(cewar bintu, don Lawisa bazata fi talatin da wani abu, ta girmewa Ma'aruf). Toh wallahi kika k'ara kiran mijina sai na bazaki a duniya na kiraki karuwa. Ai ina sane cewar ba son Allah kikeyimai. Idan kuma don wannan ne, karki damu, mace mai karfin mata goma ce ni."
Ta katse kiran da sauri jin Ma'aruf ya kwalamata kira.
"Na'am!"
Ta amsa murya a d'age, a fili tace.
"Shima Yaya Ma'aruf, ya rasa wacce zai kula sai Lawisa. Ai wallahi ko ni mace banga abin burgewa awajenta. Idan Yaya dan iska ne ya k'are a Lawisa ya ci baya wallahi."
Ta zari tissue ta fito tana masifa a zuciya, a gefe d'aya kuwa, ta ji dad'in yanda ta ci mutuncinta, daman ba tun yau take dakonta ba.
Ya jefata da wani irin kallo.
"Me kika tsaya yi?"
Fuskarta a sake tace "Babu komai."
Kamar yayi magana, sai kawai ya fasa. Ya kar6a ya gogemishi inda ya 6ata a jikinsa da baki. Ta dauke filet d'in ta maida kicin sannan ta kawo ruwan wanke hannu. Bayan sun wanke ta kai kicin ta zubar.
Ta tsaya tana dubansu, babu alamun dai Hanif yana jin bacci. Ita kuwa Allah Allah takeyi ta shiga makwancinta kafin ta6argazar da tayi ya fito.
Ta zauna don tasan sai an kammala koda zai shiga d'aki. Hanif ya rarrafo wajenta, nan kuma tabar batun kallo ta k'ara shagaltuwa wajen yi mishi wasa. Ta dubi Yaya Ma'aruf wanda yake satar kallonsu.
"Yaya, wallahi yanzu na rasa da wanda Hanif ke kama, idan na hango kamanninka sai na hango na mamansa."
Ya lumshe ido ya bude da murmushi saman fuskarsa.
"Kamannin wa kika fi hangowa?" Yayi furucin hankalinsa na ga tv. Ta k'urawa Hanif ido, sai kuma ta dago tana yiwa Ma'aruf kallon k'urillah. Sannan ta maido dubanta ga Hanif.
"Kaga hancinku d'aya, bakinku ma haka, duk k'aramin baki gareki. Idanuwan ne dai kamar na Mamansa."
Ya kwantar da kai jikin kujera yana dubanta da murmushi, Ma'aruf bai fiye hayaniya ba sai akan Bintu wacce ke sanyashi dole don muddin bazata kiyaye abinda baya so ba, to fa za tayita wahala a hannunsa.
Ta kauda kanta ganin ba shi da niyyar magana.
"Ai dole yafi kama da ni don na fi sonshi akan mamansa dama."
Bintu ta amsa.
"Allah Yasa dai kada ya dauko halinkuuuu. Allah Yasa da halayen Annabinmu (s.a.w) zaiyi koyi."
Abinda ta fada a farko ya fusatashi saidai jin kalamanta na k'arshe yasa ta d'aureshi, babu abinda zai iya ce mata.
Ganin ta tsira yasa ta yi mishi saida safe. Zata shige ya dakatar da ita.
"Ki kula, nasan kalar baccinki, muddin na lek'o naga kin danneshi ni da ke ne."
Bata ce uffan ba ta fad'a dakinta. Bayan ta ajiye Hanif ta fita ta dauko jakarsa da ruwan zafi a flask wanda ta dafa saboda shan firisocrim dinsa.
Kulle k'ofarta tayi harda mukulli, tasan yau ya shiga d'aki ya dauki wayarsa to babu abinda zai hanashi kusan ci mata zarafi.
Acan kuwa Lawisa an k'ulu an kuma ci alwashi akan Ma'aruf ko babu aure! Daman kamar Bintu ta sani, abinda ta fi bukata kenan da shi bawai auren ba.
[7/21, 1:45 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Bintu fa ansamu abokin hira. Ai kuwa bata fito falon nan ba sai bayan sun gama wasa da Hanif. Tayi mishi wanka ta chanja mishi kaya bayan ta shafa mishi hoda a jikinsa da fuskarsa, sannan ta sanyamishi riga da wando jikin cotton, na baccinsa. Ta dubeshi tana dariya irin wacce ake yiwa yaro na wasa.
"Inye, kaga bebina yayi kyau. Zo muje falo muci abinci."
Ta d'aukeshi, yana rik'e da d'an ball sai ihu yakeyi yana sanya bakinsa a jiki. Tayi mamakin ganin Ma'aruf zaune saman carpet ga filet a gabansa har ya kammala cin abinci ma. Ya hard'e k'afa yana kallon The Dr's a Mbc4. Ganinsu ya sanyashi juyowa. Nan ya mik'awa yaronsa hannu yana murmushi.
"Come to me my boy."
Bintu ta dire mishi yaron sannan ta d'auki filet tayi kicin. Jimawa kad'an sai gatanan ta fito rik'e da faranti itama ta zubo tuwo. Ta ajiye ta koma ta d'auko ruwan roba saboda Hanif, marar sanyi. Itama ta d'aukowa kanta pure water mai d'an sanyi-sanyi.
Ta dawo ta zauna.
"Zo mu ci abinci." Ma'aruf ya tankwashe k'afafu.
"Juyo da abincin nan zan ba shi."
Ta dubeshi, kai har takan yi mamakin irin wannan so da yake yiwa d'ansa. Ba musu ta juyo da filet din. Tana ci a yangance ne saboda wai tana gaban miji, ta ji ance ba'ason yin loma babba. A gida ma bata fiye yi a gabansa ba saboda tsoron fad'ansa, da dai Rufa'i ne, to shi kam babu kalar lomarta da baisani ba.
Bayan ta kammala ta ja baya tana shan ruwa.
"D'aukomin tissue a d'aki." Ta mike zuwa d'akin. Ta k'ara k'arewa d'akin kallo tamkar bak'onta. Zata d'auko ne, ta hangi BlackBerry dinsa da ke jone a chaji tana faman (vibrating) alamun dai kira ya shigo. Ta nufi wayar ta duba.
"Lawisa" Shine sunan da ta gani kawai, babu wani sakaye. Ai kuwa bata manceta ba, k'awar Yaya Abida yayar Ma'u dake yawon zuwa gidansu neman soyayyar Ma'aruf tana fakewa da duba d'ansa. Ta rik'e k'ugu, yau zatayi maganin shegiya ashe. Ta d'aga.
"Hello." Bintu tayi shiru. Sa'a ta k'ara magana.
"Haba Ma'aruf, so fa ba hauka bane da zaka dunga wulakantani, don kayi aure shikenan sai kuma ka daina kulani gaba d'aya. Me zakayi da yarinya wacce batasan rayuwa ba?"
"Uwarki da ubanki zaiyi dani."
Cewar Bintu a zuciye. Lawisa tayi shiru kafin tace.
"Ni zaki yiwa rashin kunya? Ina mai wayar?"
Bintu ta dubi k'ofa babu alamun mutum, ta cigaba da magana a hankali.
"Ya shiga wankan sunnah. Ke wai bakyajin kunya ne Lawisa, don yau bazan kiraki antin ba. Babba dake, iskancinki ya rasa kan wa zai fad'a sai tatta6a kunnenki(cewar bintu, don Lawisa bazata fi talatin da wani abu, ta girmewa Ma'aruf). Toh wallahi kika k'ara kiran mijina sai na bazaki a duniya na kiraki karuwa. Ai ina sane cewar ba son Allah kikeyimai. Idan kuma don wannan ne, karki damu, mace mai karfin mata goma ce ni."
Ta katse kiran da sauri jin Ma'aruf ya kwalamata kira.
"Na'am!"
Ta amsa murya a d'age, a fili tace.
"Shima Yaya Ma'aruf, ya rasa wacce zai kula sai Lawisa. Ai wallahi ko ni mace banga abin burgewa awajenta. Idan Yaya dan iska ne ya k'are a Lawisa ya ci baya wallahi."
Ta zari tissue ta fito tana masifa a zuciya, a gefe d'aya kuwa, ta ji dad'in yanda ta ci mutuncinta, daman ba tun yau take dakonta ba.
Ya jefata da wani irin kallo.
"Me kika tsaya yi?"
Fuskarta a sake tace "Babu komai."
Kamar yayi magana, sai kawai ya fasa. Ya kar6a ya gogemishi inda ya 6ata a jikinsa da baki. Ta dauke filet d'in ta maida kicin sannan ta kawo ruwan wanke hannu. Bayan sun wanke ta kai kicin ta zubar.
Ta tsaya tana dubansu, babu alamun dai Hanif yana jin bacci. Ita kuwa Allah Allah takeyi ta shiga makwancinta kafin ta6argazar da tayi ya fito.
Ta zauna don tasan sai an kammala koda zai shiga d'aki. Hanif ya rarrafo wajenta, nan kuma tabar batun kallo ta k'ara shagaltuwa wajen yi mishi wasa. Ta dubi Yaya Ma'aruf wanda yake satar kallonsu.
"Yaya, wallahi yanzu na rasa da wanda Hanif ke kama, idan na hango kamanninka sai na hango na mamansa."
Ya lumshe ido ya bude da murmushi saman fuskarsa.
"Kamannin wa kika fi hangowa?" Yayi furucin hankalinsa na ga tv. Ta k'urawa Hanif ido, sai kuma ta dago tana yiwa Ma'aruf kallon k'urillah. Sannan ta maido dubanta ga Hanif.
"Kaga hancinku d'aya, bakinku ma haka, duk k'aramin baki gareki. Idanuwan ne dai kamar na Mamansa."
Ya kwantar da kai jikin kujera yana dubanta da murmushi, Ma'aruf bai fiye hayaniya ba sai akan Bintu wacce ke sanyashi dole don muddin bazata kiyaye abinda baya so ba, to fa za tayita wahala a hannunsa.
Ta kauda kanta ganin ba shi da niyyar magana.
"Ai dole yafi kama da ni don na fi sonshi akan mamansa dama."
Bintu ta amsa.
"Allah Yasa dai kada ya dauko halinkuuuu. Allah Yasa da halayen Annabinmu (s.a.w) zaiyi koyi."
Abinda ta fada a farko ya fusatashi saidai jin kalamanta na k'arshe yasa ta d'aureshi, babu abinda zai iya ce mata.
Ganin ta tsira yasa ta yi mishi saida safe. Zata shige ya dakatar da ita.
"Ki kula, nasan kalar baccinki, muddin na lek'o naga kin danneshi ni da ke ne."
Bata ce uffan ba ta fad'a dakinta. Bayan ta ajiye Hanif ta fita ta dauko jakarsa da ruwan zafi a flask wanda ta dafa saboda shan firisocrim dinsa.
Kulle k'ofarta tayi harda mukulli, tasan yau ya shiga d'aki ya dauki wayarsa to babu abinda zai hanashi kusan ci mata zarafi.
Acan kuwa Lawisa an k'ulu an kuma ci alwashi akan Ma'aruf ko babu aure! Daman kamar Bintu ta sani, abinda ta fi bukata kenan da shi bawai auren ba.
[7/21, 1:45 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)