Sashe 8
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
<<14>>
Gadonsu ta fad'a, wani wawan bacci ya kwasheta tuni ta mance da haushin Ma'aruf da takeji. Ba ita ta farka ba saida Mami ta tasheta don gabatar da sallar isha'i.
"Kwanakin nan kin zama wata kasa, baki da aiki muddin baku da makaranta sai bacci. Kina bani mamaki, wannan bansan me zaki tsinana a gidan aure ba."
Tana jin Mami na faman maganganu har ta fice. Ganin da tayi wani sabon baccin na neman kwasarta ne ya sanyata mik'ewa da k'arfinta. Ta fad'a band'aki.
Bayan ta gama uzurinta ta d'ora alwala ta fito. Saida ta idar da sallah sannan ta fad'a ta k'ara wani wankan sakamakon zafin da ya addabeta.
Ta shirya cikin brown tshirt da siket bak'i. Bata bi ta kan d'ankwali ba, ita kam basa jituwa da d'ankwali. Gashinta tufke da ribbon ta nufi falon.
Tayi mamakin ganin Sadauki tare da babansa. Gaba d'aya suke zaune har Ma'aruf da Aisha wacce bata jima da shigowa gidan ba itama.
Da gudu-gudu yaron ya nufota da tafiyarsa wacce batayi kwari sosai ba. Yana son Bintu, har ya ganeta, ita d'inma kasancewar tana mishi wasa sosai ne. Yaron yana da kwuiwuya idan yaso. Ganinta ne ya sanyashi warewa amma a farko yana nannad'e jikin mahaifinsa.
Da sauri ta d'aukeshi ta cilla sama tana dariya.
"Oyoyo my lovely son. Ummuah!" Ta sakar mishi sumba a le66ansa. Ya kyalkyale da dariya. Mami tace
"Oh, kiga yaro, tun d'azu ya k'i sakewa amma ganin mutuniyarsa har da kyakyacewa."
Rufa'i da Aisha suka dara. Bintun ma tana dariya ta k'araso zata zauna.
"A'a, ban hanaki zama babu d'ankwali ba? Oya, koma ki d'auko." Cewar Mami.
Dolenta ta koma tana d'auke da Sadauki har d'aki, bayan ta d'auko suka fito.
Ko kallon sashen da Ma'aruf yake bata yi, ballantana ya saka ran samun gaisuwarta. Ta gaida Yayanta Rufa'i. Ya amsa cikin nuna jin dad'in ganinta.
"Kamar kuwa kinsan inada magana da ke kanwata."
Ta bar yiwa Sadauki wasa ta dubeshi fuska a sake.
"Magana wace iri Yayan?"
"Kema kinsani, maganarmu ta rannan har yau bakice uffan ba."
Sai lokacin ta tunano, ashe fa ya sanarmata abokinsa Ukasha ya nuna yana sonta. Ta dubi gefen Mami, idanunsu yana kanta. Jikinta ya bata Ma'aruf ma kallonsu yakeyi. Ta yamutse fuska.
"Ai don kada na fad'a kaga kamar na wulak'anta abokinka ne wallahi."
Mami da Aisha har Rufa'in suka dara. Mami tayi kwafa, kafin ma Rufa'i ya sanarwa Bintun ita ta soma ji, daman tasan za'a rina.
"A'aha, saidai idan ba Fatima Bintun da na sani bace. A komai sai ta kwa6a shiriritarta."
Bintu ta dubeta da murmushi.
"Allah Mami ba zancen shiririta ba, ni ban fiyeson mutum mai sirantaka ba. Ka ba shi hakuri, Allah kuwa bana sonshi. Ai karatu ma nakeyi ko Mami?"
Mami da Aisha suka tuntsire da dariya, hatta Ma'aruf wanda rabin hankalinsa ke a waya saida ya murmusa jin abinda ya fito daga bakinta. Rufa'i ya d'an d'aure fuska kad'an.
"Wulak'ancin da zaki yiwa abokina kenan? Kinsan kusancinmu kuwa?"
Kafin tayi magana, Mami ta rigata.
"Wai ana so dole ne Rufa'i? Tunda yarinya ta nunamaka bata sonsa ai sai ka rabu da ita. Nifa banason takurawa mutum."
Rufa'i yana jijjiga muk'ullin motarsa yace "Allah kuwa Mami kuna sangarta yarannan da yawa. Kamar wannan k'atuwar ace har yanzu wulak'anta maza takeyi, wataran sai kin nemi mashinshini kin rasa. Ukashat yafi k'arfin ajinki, don ma dai kawai so baruwansa."
Ganin ya fusata, ya sanyasu dariya. Sai lokacin Ma'aruf ya tofa,
"Toh kai menene na fusatar? Ni ai sun burgeni, idan karatun karatu, idan auren to ayi auren. Babu amfanin kula samari barkatai. A zamanin nan na yanzu sai ana kaffa-kaffa. Kodayake naga ita waccan boss ta kanta ce."
Ya basu labarin sunayen da ya ta6a gani ta sanyawa samarinta. Rufa'i kansa saida ya dara. Ita kuwa ko a jikinta don bata huce da abinda Ma'aruf yayi mata ba, sai ma ta mayarda hankalinta ga yiwa Sadauki wasa. Ba zato ta ji an mako mata filo.
Mami ce, cikin dariya take fad'in.
"Jimin ja'irar yarinya, ashe abinda kuke aikatawa kenan? Eh lallai zan kwace wayoyinku."
Bintu sai lokacin tayi dariya. Atine ta fito rik'e da Hanif wanda ta chanjawa kaya. Bintu ta bishi da kallo, taji wani sanyi, tun d'azun tunaninta yana kansa saidai batason shiga d'akin ganin Ma'aruf a wajen. Ga Ma'aruf kuwa, ya lura da fushin da takeyi da shi, abin mamaki, sai ya ji ya damu. Yana rik'e da Hanif, saidai jefi-jefi yakan dubeta, sai wasa takeyi da Sadauki tana hira da Rufa'i wanda dolensa ya saki ransa ganin Bintu bazata bar shi ba. Sunata hirar har Mami, can kuma Hanif ya soma kuka. Tayi saurin dubansa, ganin ta had'a ido da ubansa ta basar gami da d'auke kanta.
Ita kam ko kukan yaron bata so. Tana gani uban ya mik'e ya sa6ashi a kafad'a yayi waje yana raino, ta bi fuskar yaron da kallo da murmushi kafin ta maido dubanta ga Sadauki.
"Yayan, wai yaushe zaka kawomana Sadauki kwana? Mami ku lura bai ta6a kawoshi ba."
Mami ta ta6e baki
"Yaron yanzu kenan, son 'ya'yansu Bintu. Baki ganin ko yini zai kawoshi, saidai su yinin tare?"
Rufa'i ya rufe fuska yana dariya.
"Yaron nan fa ba'a yayeshi ba."
"Mami rannan fa agabanmu yayita fad'a wai meyasa Anti Hajara ke bari ana fita da shi makwafta? Bayaso." Cewar Aisha.
"Ai shikenan, yanzun ma ya tashi ya wuce da shi."
Bintu tana dariya ta amsa.
"Madara yafi sha kuma. Kawai dai Yayan bayason nesa da yaronsa."
Mami bata k'ara magana ba, k'arshe ma ta mik'e ta bar falon. Hirar batayi tsawo ba, Rufa'i ya fice ganin hadari a garin.
Bintu ta dawo ciki ta dubi Aisha.
"Wai yayanki baisan ba'ason fita da yaro idan ana iska ba haka, don Allah jeki kice ya maidoshi ciki, kallesu can a harabar gidan."
Aisha ta harareta.
"Tsawon baki na fiki ne? Jimin ke d'innan ma. Banda haka, mutum da d'ansa."
Bintu ta ja tsaki.
"Banza mai fuskar buzaye." Daga haka ta fito Aisha na mata dariya.
Ta lek'osu ta windon falon, suna tsaye ya rufe mishi kai da shawul, har lokacin ana iska, ganin da tayi iskar ta soma k'arfi yasa ta kasa hak'ura da saurinta ta nufi k'ofa. Shima a lokacin ganin iskar na yawa ya sanyashi yo hanyar falon. A fili take masifa.
"Ya fita da yaro cikin wannan iskar kamar..."
Sauran maganarta ta mak'ale a fatar bakinta ganinsa a gabanta. Ya zubamata idanu, haka kawai ta ji kallon ya sanyaya jikinta. Ta juya da sauri, ya dakatar da ita da fad'in.
"Kar6eshi." Dolenta ta juyo tana wani cin magani.
"Me d'in?"
Yayi d'an murmushi a ranta tace "Ba saban ba."
"Ina tunanin shi kikazo kar6a."
Ta tsuke baki, idanunta suka kai ga shanyarta. Ta nuna da yatsa.
"Shanyata..shanyata na zo kwashewa."
Ya dubi kayan.
"Daman ke kika saba kwasa?"
"Ai d'an dolon bayanan."
Bai bi ta kanta ba ya gota ya shige ciki ganin idan baiyi da gaske ba ruwan zai iya zubowa batare da ya koma d'akinsa ba.
Ta rik'e k'ugu ta bi bayansa da kallo. Dolenta ta kwaso kayan gudun kada ya k'aryatata. Tana kallonsa da sauri sauri ya nufi d'akinsa. Itama da sauri tayi ciki don tuni ruwa ya soma sauka.
A falo ta yasar da kayan ta nufi d'akin Hanif. D'aukar yaron tayi tana mishi wasa. Tana son yaron, kusan tare suke rainonsa da Atine. Haka ta wuni a d'akin har akayi kiran sallah.
* * *
<<15>>
Haka rayuwar ta gidan ke tafiya cikin jin dad'i da kwanciyar hankali. Idan an d'auke mage da 6eran gidan wad'anda basu fiye jituwa ba.(Ma'aruf da Bintu).
Sun bararraje a falo da k'anwar Ma'u, Hafsa wacce bikinta ya k'arato suna duban ankonta.
"Kai, wallahi yayi kyau. Bari na kaiwa Mami ta gani." Cewar Aisha.
Bayan tashin Aisha, Bintu ta muskuta kusa da Hafsa.
"Wai wa zaki aura?"
Hafsa tayi farr da ido.
"Ina da wanda yafi Bash?"
Bintu ta kya6e baki.
Yayi daidai da tahowar Ma'aruf, zaiyi sallama ya tsaya cak jin furucin da Bintu tayi wanda ya girgizashi. Ga abinda tace.
"Kema dai Hafsa, ke bakiga yanda akeyi ba. Idan yayata ta rasu, sai a bawa k'anwarta mijin? Saboda yaranta su samu gata. Wai Bash? Mts."
Hafsa ta d'aure fuska, daman wata kakarta ta ta6a yi mata wannan maganar. Nan take haushin Bintu ya kamata. Ta mik'e ta d'auki jakarta.
"Ni bana wannan ra'ayin, bana sonsa. Kuma aurena da Bash, in sha Allah babu abinda zai hana. Idan kinga damar zuwa ki zo, idan kuwa bakiga dama ba kada ki zo."
Daga haka ta nufi falon Mami na biyu. A fili Bintu ta rik'e baki tayi magana.
"Oh, ina laifin Yayanmu, Bash d'in da bai fi a dunk'ule a jefa aljihu ba tsabar gajarta?"
Daidai lokacin Ma'aruf ya fita baranda, saida ya kammala cin dariyar furucinta na k'arshe kafin ya shiga.
Ta mik'e da zummar barin falon itama da zummar k'ara fesawa Mami hangen da tayi sukayi kici6us da Ma'aruf. Ta amsa sallamarsa a tsorace. Bata so zuwansa yanzu ba Hafsa na nan, tsoranta kada ta sanarmishi kato6arar da tayi mishi. Ganin babu walwala a saman fuskarsa yasa ta azamar gaisheshi.
Ya amsa kafin yace.
"Ki zo ina nemanki."
Daga haka ya juya ya fita. Ta had'iyi miyau, to fa, yau kuma da wacce yazo? Hankalinta ya kasu gida biyu, tana son k'arasawa wajensu Hafsa, ga kuma kiran Yaya Ma'aruf.
"To idan dukana zaiyi fa?" Ta tambayi zuciyarta. Dabara ta fad'o mata. Bari ta tafi da Hanif, tasan yanda yake son d'ansa bazai iya yi mata komai ba. Da sauri ta nufi wajen Atine ta kar6eshi ta goya.
K'ofar a bude, ta shiga da sallamarta.
Yana tsaye gaban firij yana fiddo gwangwanin Maltina. Ya dubeta, murmushi ya saki har hak'oransa na bayyana. Ta k'araso ta zauna.
"Yaya gani"
Ya maida firjin ya rufe ya zauna yana fuskantarta. Itama shi take kallo, ta dauke idanunta. Ita kam tafi sabawa da hararar da yake danna mata akan kallon salama d'innan.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<16>>
Gadonsu ta fad'a, wani wawan bacci ya kwasheta tuni ta mance da haushin Ma'aruf da takeji. Ba ita ta farka ba saida Mami ta tasheta don gabatar da sallar isha'i.
"Kwanakin nan kin zama wata kasa, baki da aiki muddin baku da makaranta sai bacci. Kina bani mamaki, wannan bansan me zaki tsinana a gidan aure ba."
Tana jin Mami na faman maganganu har ta fice. Ganin da tayi wani sabon baccin na neman kwasarta ne ya sanyata mik'ewa da k'arfinta. Ta fad'a band'aki.
Bayan ta gama uzurinta ta d'ora alwala ta fito. Saida ta idar da sallah sannan ta fad'a ta k'ara wani wankan sakamakon zafin da ya addabeta.
Ta shirya cikin brown tshirt da siket bak'i. Bata bi ta kan d'ankwali ba, ita kam basa jituwa da d'ankwali. Gashinta tufke da ribbon ta nufi falon.
Tayi mamakin ganin Sadauki tare da babansa. Gaba d'aya suke zaune har Ma'aruf da Aisha wacce bata jima da shigowa gidan ba itama.
Da gudu-gudu yaron ya nufota da tafiyarsa wacce batayi kwari sosai ba. Yana son Bintu, har ya ganeta, ita d'inma kasancewar tana mishi wasa sosai ne. Yaron yana da kwuiwuya idan yaso. Ganinta ne ya sanyashi warewa amma a farko yana nannad'e jikin mahaifinsa.
Da sauri ta d'aukeshi ta cilla sama tana dariya.
"Oyoyo my lovely son. Ummuah!" Ta sakar mishi sumba a le66ansa. Ya kyalkyale da dariya. Mami tace
"Oh, kiga yaro, tun d'azu ya k'i sakewa amma ganin mutuniyarsa har da kyakyacewa."
Rufa'i da Aisha suka dara. Bintun ma tana dariya ta k'araso zata zauna.
"A'a, ban hanaki zama babu d'ankwali ba? Oya, koma ki d'auko." Cewar Mami.
Dolenta ta koma tana d'auke da Sadauki har d'aki, bayan ta d'auko suka fito.
Ko kallon sashen da Ma'aruf yake bata yi, ballantana ya saka ran samun gaisuwarta. Ta gaida Yayanta Rufa'i. Ya amsa cikin nuna jin dad'in ganinta.
"Kamar kuwa kinsan inada magana da ke kanwata."
Ta bar yiwa Sadauki wasa ta dubeshi fuska a sake.
"Magana wace iri Yayan?"
"Kema kinsani, maganarmu ta rannan har yau bakice uffan ba."
Sai lokacin ta tunano, ashe fa ya sanarmata abokinsa Ukasha ya nuna yana sonta. Ta dubi gefen Mami, idanunsu yana kanta. Jikinta ya bata Ma'aruf ma kallonsu yakeyi. Ta yamutse fuska.
"Ai don kada na fad'a kaga kamar na wulak'anta abokinka ne wallahi."
Mami da Aisha har Rufa'in suka dara. Mami tayi kwafa, kafin ma Rufa'i ya sanarwa Bintun ita ta soma ji, daman tasan za'a rina.
"A'aha, saidai idan ba Fatima Bintun da na sani bace. A komai sai ta kwa6a shiriritarta."
Bintu ta dubeta da murmushi.
"Allah Mami ba zancen shiririta ba, ni ban fiyeson mutum mai sirantaka ba. Ka ba shi hakuri, Allah kuwa bana sonshi. Ai karatu ma nakeyi ko Mami?"
Mami da Aisha suka tuntsire da dariya, hatta Ma'aruf wanda rabin hankalinsa ke a waya saida ya murmusa jin abinda ya fito daga bakinta. Rufa'i ya d'an d'aure fuska kad'an.
"Wulak'ancin da zaki yiwa abokina kenan? Kinsan kusancinmu kuwa?"
Kafin tayi magana, Mami ta rigata.
"Wai ana so dole ne Rufa'i? Tunda yarinya ta nunamaka bata sonsa ai sai ka rabu da ita. Nifa banason takurawa mutum."
Rufa'i yana jijjiga muk'ullin motarsa yace "Allah kuwa Mami kuna sangarta yarannan da yawa. Kamar wannan k'atuwar ace har yanzu wulak'anta maza takeyi, wataran sai kin nemi mashinshini kin rasa. Ukashat yafi k'arfin ajinki, don ma dai kawai so baruwansa."
Ganin ya fusata, ya sanyasu dariya. Sai lokacin Ma'aruf ya tofa,
"Toh kai menene na fusatar? Ni ai sun burgeni, idan karatun karatu, idan auren to ayi auren. Babu amfanin kula samari barkatai. A zamanin nan na yanzu sai ana kaffa-kaffa. Kodayake naga ita waccan boss ta kanta ce."
Ya basu labarin sunayen da ya ta6a gani ta sanyawa samarinta. Rufa'i kansa saida ya dara. Ita kuwa ko a jikinta don bata huce da abinda Ma'aruf yayi mata ba, sai ma ta mayarda hankalinta ga yiwa Sadauki wasa. Ba zato ta ji an mako mata filo.
Mami ce, cikin dariya take fad'in.
"Jimin ja'irar yarinya, ashe abinda kuke aikatawa kenan? Eh lallai zan kwace wayoyinku."
Bintu sai lokacin tayi dariya. Atine ta fito rik'e da Hanif wanda ta chanjawa kaya. Bintu ta bishi da kallo, taji wani sanyi, tun d'azun tunaninta yana kansa saidai batason shiga d'akin ganin Ma'aruf a wajen. Ga Ma'aruf kuwa, ya lura da fushin da takeyi da shi, abin mamaki, sai ya ji ya damu. Yana rik'e da Hanif, saidai jefi-jefi yakan dubeta, sai wasa takeyi da Sadauki tana hira da Rufa'i wanda dolensa ya saki ransa ganin Bintu bazata bar shi ba. Sunata hirar har Mami, can kuma Hanif ya soma kuka. Tayi saurin dubansa, ganin ta had'a ido da ubansa ta basar gami da d'auke kanta.
Ita kam ko kukan yaron bata so. Tana gani uban ya mik'e ya sa6ashi a kafad'a yayi waje yana raino, ta bi fuskar yaron da kallo da murmushi kafin ta maido dubanta ga Sadauki.
"Yayan, wai yaushe zaka kawomana Sadauki kwana? Mami ku lura bai ta6a kawoshi ba."
Mami ta ta6e baki
"Yaron yanzu kenan, son 'ya'yansu Bintu. Baki ganin ko yini zai kawoshi, saidai su yinin tare?"
Rufa'i ya rufe fuska yana dariya.
"Yaron nan fa ba'a yayeshi ba."
"Mami rannan fa agabanmu yayita fad'a wai meyasa Anti Hajara ke bari ana fita da shi makwafta? Bayaso." Cewar Aisha.
"Ai shikenan, yanzun ma ya tashi ya wuce da shi."
Bintu tana dariya ta amsa.
"Madara yafi sha kuma. Kawai dai Yayan bayason nesa da yaronsa."
Mami bata k'ara magana ba, k'arshe ma ta mik'e ta bar falon. Hirar batayi tsawo ba, Rufa'i ya fice ganin hadari a garin.
Bintu ta dawo ciki ta dubi Aisha.
"Wai yayanki baisan ba'ason fita da yaro idan ana iska ba haka, don Allah jeki kice ya maidoshi ciki, kallesu can a harabar gidan."
Aisha ta harareta.
"Tsawon baki na fiki ne? Jimin ke d'innan ma. Banda haka, mutum da d'ansa."
Bintu ta ja tsaki.
"Banza mai fuskar buzaye." Daga haka ta fito Aisha na mata dariya.
Ta lek'osu ta windon falon, suna tsaye ya rufe mishi kai da shawul, har lokacin ana iska, ganin da tayi iskar ta soma k'arfi yasa ta kasa hak'ura da saurinta ta nufi k'ofa. Shima a lokacin ganin iskar na yawa ya sanyashi yo hanyar falon. A fili take masifa.
"Ya fita da yaro cikin wannan iskar kamar..."
Sauran maganarta ta mak'ale a fatar bakinta ganinsa a gabanta. Ya zubamata idanu, haka kawai ta ji kallon ya sanyaya jikinta. Ta juya da sauri, ya dakatar da ita da fad'in.
"Kar6eshi." Dolenta ta juyo tana wani cin magani.
"Me d'in?"
Yayi d'an murmushi a ranta tace "Ba saban ba."
"Ina tunanin shi kikazo kar6a."
Ta tsuke baki, idanunta suka kai ga shanyarta. Ta nuna da yatsa.
"Shanyata..shanyata na zo kwashewa."
Ya dubi kayan.
"Daman ke kika saba kwasa?"
"Ai d'an dolon bayanan."
Bai bi ta kanta ba ya gota ya shige ciki ganin idan baiyi da gaske ba ruwan zai iya zubowa batare da ya koma d'akinsa ba.
Ta rik'e k'ugu ta bi bayansa da kallo. Dolenta ta kwaso kayan gudun kada ya k'aryatata. Tana kallonsa da sauri sauri ya nufi d'akinsa. Itama da sauri tayi ciki don tuni ruwa ya soma sauka.
A falo ta yasar da kayan ta nufi d'akin Hanif. D'aukar yaron tayi tana mishi wasa. Tana son yaron, kusan tare suke rainonsa da Atine. Haka ta wuni a d'akin har akayi kiran sallah.
* * *
<<15>>
Haka rayuwar ta gidan ke tafiya cikin jin dad'i da kwanciyar hankali. Idan an d'auke mage da 6eran gidan wad'anda basu fiye jituwa ba.(Ma'aruf da Bintu).
Sun bararraje a falo da k'anwar Ma'u, Hafsa wacce bikinta ya k'arato suna duban ankonta.
"Kai, wallahi yayi kyau. Bari na kaiwa Mami ta gani." Cewar Aisha.
Bayan tashin Aisha, Bintu ta muskuta kusa da Hafsa.
"Wai wa zaki aura?"
Hafsa tayi farr da ido.
"Ina da wanda yafi Bash?"
Bintu ta kya6e baki.
Yayi daidai da tahowar Ma'aruf, zaiyi sallama ya tsaya cak jin furucin da Bintu tayi wanda ya girgizashi. Ga abinda tace.
"Kema dai Hafsa, ke bakiga yanda akeyi ba. Idan yayata ta rasu, sai a bawa k'anwarta mijin? Saboda yaranta su samu gata. Wai Bash? Mts."
Hafsa ta d'aure fuska, daman wata kakarta ta ta6a yi mata wannan maganar. Nan take haushin Bintu ya kamata. Ta mik'e ta d'auki jakarta.
"Ni bana wannan ra'ayin, bana sonsa. Kuma aurena da Bash, in sha Allah babu abinda zai hana. Idan kinga damar zuwa ki zo, idan kuwa bakiga dama ba kada ki zo."
Daga haka ta nufi falon Mami na biyu. A fili Bintu ta rik'e baki tayi magana.
"Oh, ina laifin Yayanmu, Bash d'in da bai fi a dunk'ule a jefa aljihu ba tsabar gajarta?"
Daidai lokacin Ma'aruf ya fita baranda, saida ya kammala cin dariyar furucinta na k'arshe kafin ya shiga.
Ta mik'e da zummar barin falon itama da zummar k'ara fesawa Mami hangen da tayi sukayi kici6us da Ma'aruf. Ta amsa sallamarsa a tsorace. Bata so zuwansa yanzu ba Hafsa na nan, tsoranta kada ta sanarmishi kato6arar da tayi mishi. Ganin babu walwala a saman fuskarsa yasa ta azamar gaisheshi.
Ya amsa kafin yace.
"Ki zo ina nemanki."
Daga haka ya juya ya fita. Ta had'iyi miyau, to fa, yau kuma da wacce yazo? Hankalinta ya kasu gida biyu, tana son k'arasawa wajensu Hafsa, ga kuma kiran Yaya Ma'aruf.
"To idan dukana zaiyi fa?" Ta tambayi zuciyarta. Dabara ta fad'o mata. Bari ta tafi da Hanif, tasan yanda yake son d'ansa bazai iya yi mata komai ba. Da sauri ta nufi wajen Atine ta kar6eshi ta goya.
K'ofar a bude, ta shiga da sallamarta.
Yana tsaye gaban firij yana fiddo gwangwanin Maltina. Ya dubeta, murmushi ya saki har hak'oransa na bayyana. Ta k'araso ta zauna.
"Yaya gani"
Ya maida firjin ya rufe ya zauna yana fuskantarta. Itama shi take kallo, ta dauke idanunta. Ita kam tafi sabawa da hararar da yake danna mata akan kallon salama d'innan.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<16>>