Sashe 26
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
<<38>>
A hankali ta zauna a k'asa ta jingina da gado yayinda ta takure k'afafunta da hannuwanta wuri d'aya. Har lokacin jikinta yana kyarma. Ta k'ara kai hannu ta share bakinta. Sai kuma ta fashe da kuka marar dalili. To ita kanta batasan abinda ya janyomata zubar hawayen ba, tasan dai ta tsorata sosai da irin abinda ya wanzu tsakaninsu. Can kuma ta mik'e ta koma kan gado gami da goge fuskarta. Lumshe ido tayi tana maida numfashi sannu-sannu. Abin mamaki sai kuma ta tsinci kanta da yin wani murmushi. Yaya Ma'aruf ya had'u, shine kawai abinda ta ayyana a ranta. Abubuwa da yawa sun tsaya mata a rai a d'an wannan rik'on da yayi mata da sak'on da ya isar.
"Ban hanaki yimin shiga haka ba?"
Abinda ya fad'o ranta kenan, ta mik'e tsaye da saurinta ta nufi gaban madubi tana k'arewa jikinta kallo.
Rigar kam babu laifi, da a gidan Mami takeyi ba zata barta ta sanya ba duk da cewar ita bata ga aibunta ba, amma ba laifi tayi shara-shara.
Ta dauki top d'inta ta d'ora akai gami da zama a gefen gadon ta rik'e cikinta da ke wani irin kuwwa sakamakon yunwar da ta ji ta motsa mata. Saidai kuma batajin zata iya fita yana a falon, wai Bintu ce da jin kunyar Ma'aruf yau? Abin da ya bata mamaki kenan har yasa ta murmusawa.
Haka ta zauna tana sak'e-sak'en zuci. Ta rasa yanda zata fassara hakikanin matsayin da ta ajiye Ma'aruf. D'an uwan ne ko Mijin? To ai kuwa tuni a matsayin mijin yake ko ta k'i kuwa. Saidai fa bata sonshi, shine babbar hujjar da ta kafawa kanta har take tak'ama da shi. Ya za'ayi ta mance munanan kalamansa a kanta? Ai ya nuna ita d'in yarinya ce babu abinda zaiyi da ita, to kuwa zai yi nadamar furucinsa, shiga kuwa na English wears, yanzu ta soma. Jikinta ne kuwa, ta daina bari ya maimaita wannan abu da yayi. Ta sauke ajiyar zuciya tayi shiru tana jira ya bar falon. Ta jima zaune kafin ta jiyo motsinsa wajen kicin sai kuma da jimawa ta ji ya rufe k'ofarsa. Saida ta bari aka d'anyi mintuna ta lek'o, ganin duhu a falon ya tabbatar mata lallai ya kwanta kenan. Kunna fitilar ta yi ta ware ido, babu ledojin a tsakar falo hakan ya sanyata nufar kicin, nan ta ci karo da su a saman firij.
Haka ta koma dakinta ta rufe gam da mukulli bayan ta dauki komai na bukatarta.
* * *
Washegari ya kama Asabar, abinda ya sanya Bintu jin babu dadi, tana son gasa shi, saidai ta lura ta soma d'an jin nauyinsa don abinda yayi, ashe daman da gaske ne da ta ji ana cewa ana samun wani sauyi a jiki idan irin hakan ta faru a lokacin? Ita kam sai yanzu ta gaskata. Bata mantawa akwai sadda suke hira da Aisha akan ire-iren lamuran nan, ta 6alli rakenta tana tsotsa gami da lumshe ido.
"Banza kawai, jeki haukan soyayya ya kasheki kawai, gwara miki shan rake kullum kiyita sha kina nishadi abinki, da wata soyayya."
Bata manta amsar Aisha alokacin.
"Hum, bakisan menene ma'anar kalmar ba, kedai Allah Yasa wataran ki ji yanda..."
Bata manta yanda ta toshemata baki wai kada tayi mata mugun fata. Aisha ta fisge hannunta tana dariya kafin tace.
"Wallahi akwai abinda idan anyimiki ba zaki iya magana ba. Ke bakinki mutuwa zaiyi, zaki fahimci shegen kuri ne kawai kikeyi."
Dariya tayi ta cigaba da shan rakenta kawai.
Bintu ta numfasa ta mik'e cike da kwarin gwuiwa, ba fa zata bari tayi saurin karaya ba, lallai idan ta nunamishi sanyi da kuma nauyinsa da take ji zai fahimci yayi nasara akanta. Har alokacin tana jin 6acin ran zancen da yaje.
Har ta fito ta kammala komai bai fito daga d'akinsa ba, daman bata tsammatar hakan tunda yau babu aiki. Ta koma d'akinta tayi wanka, har ta dauko kananun kaya sai tayi murmushi ta mayar, gaskiya a yau dai ba zata iya sanyawar ba amma hakan ba wai yana nufin ta bar alak'a da su bane tunda sun zame mata kamar atamfa.
Ta sanya doguwar riga ta atamfa, hoda kawai ta shafa sai man le6e.
A falo tana zaune tana karyawa sai gashinan ya fito. Ko wanka baiyi ba, daga shi sai riga da wando dogo na bacci na (pyjamas). Ya zauna saman kujera. Bata ko kalleshi ba sai ma ta had'e fuska. Ido ya zubamata, haka kawai ya ji ta burgeshi yanda ta had'e fuskar. Ya bi d'an bakinnata da kallo kawai, shi kansa a yanzun sai yakejin kunyarta amma kasancewarsa namiji, ya maze har da wani had'e gira kad'an.
"Ina kwana." Ya gaisheta da gatse.
Sai kuma bataji dadin gaidashin da bata yi ba. Ta gaisheshi, ya amsa kafin yayi umarnin ta had'amishi abin kari. Babu musu ta had'a ta ajiye a gabansa.
Yana wani muzurai yana shan tea shi a dole kada yarinya ta ga fuskar rainashi. (Ikon Allah)
Har ta kammala ta mik'e babu wata magana da ta k'ara shiga tsakaninsu. Ya bita da kallo, sai yaga kamar ma atamfar ta fi yi mata kyau sosai. Ya kawar da wannan tunanin kamar yanda ya saba kaudawar duk lokacin da ya taso.
Haka suka ci hutun karshen satin kowannensu na kokarin nuna jarumtarsa a fuska, alamun fa babu wani abu a zuciya.
Ranar litinin tana zauna a falo bayan ta dawo daga makaranta, bayan ya dawo aiki yake sanarmata da tafiyar da ta kamashi zuwa Lagos, bisa wani aiki da zaiyi a karkashin branch na kamfaninsu dake can. Ai a take ta soma washe hak'ora.
"Yaushe ne tafiyar?"
Ya zauna yana dubanta fuska a sake.
"Oh, wato murna ma kikeyi?"
Ta rufe baki adalilin dariyar farincikin da ya taho mata.
"A'a, ai idan dadi yayi yawa kuka akeyi, nima bakinciki ne yayi yawa shiyasa ni darawa."
Ya jinjina kai ya dubi gefe yana murmushi mai bayyana hak'ora kafin ya dubeta.
"Bansan lokacin da raininki gareni ya k'aru har haka ba."
Ya mik'e tsaye, ya soma tafiya hanyar d'akinsa.
"Gobe zan wuce in sha Allah, mungama magana da Mami, Aisha zata zo ta tayaki zama."
Wani ihun murna ta saki wanda ya sanyashi juyowa. Da sauri tayi narai-narai da fuska.
"Toh Yaya, Allah Ya kiyaye."
Ya d'an zubamata ido sai kuma ya juya ya shige.
Murna bai barta ta k'arasa abinda takeyi ba, ai gwara ya d'anyi k'aura daga gidan ko ta sha iska. Haba, Kullum mutum yana gida idan ya taso ofis sai kace ba shi da abokai. Ta ja k'aramin tsaki kawai.
Shi kuwa mamaki ta ba shi ganin yanda take murna da tafiyarsa, wannan na nufin Bintu bata damu da shi ba? Ya tunano a baya idan wata 'yar tafiya ta sameshi yanda Ma'u ke damuwa har ta kai ga zubda ruwan hawaye na rashin son tafiyarsa. Amma yau ga Bintu ta zo matsayin matarsa, bata jin ko d'ar na tafiyar da zaiyi. Jikinsa ya d'anyi sanyi, haka kawai baiji dad'in yanda ta nuna d'in ba. Ya damu iyaka damuwa har saida ya gaza jurewa a ranar da zai tafi ya dubeta.
"Meyasa bakiyi bakinciki da tafiyata ba?"
Ta ji tambayar babu zato, sai kuma ta yi murmushi.
"To ai kaima zaka huta da ni, tunda kace ina matsawa rayuwarka. Kuma kace ni ba komai ka d'aukeni ba ko?"
Ya rasa kuma bakin magana. Ya watsamata wani kallo mai nuni da jin haushin kalamanta sannan ya sanya kai ya fita jaye da Trolley dinsa. Ta dafe bango da hannunta tana binsa da kallo gami da doka uban hamma. A hankali tace "Allah Ya kaika lafiya. Bari nayi baccina har na gaji ba takura."
Ta rufe k'ofar ta koma ciki, lokacin bakwai da mintuna na safe. Abin ya yi mata dadi don kuwa bata da paper.
[7/23, 11:59 AM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
A hankali ta zauna a k'asa ta jingina da gado yayinda ta takure k'afafunta da hannuwanta wuri d'aya. Har lokacin jikinta yana kyarma. Ta k'ara kai hannu ta share bakinta. Sai kuma ta fashe da kuka marar dalili. To ita kanta batasan abinda ya janyomata zubar hawayen ba, tasan dai ta tsorata sosai da irin abinda ya wanzu tsakaninsu. Can kuma ta mik'e ta koma kan gado gami da goge fuskarta. Lumshe ido tayi tana maida numfashi sannu-sannu. Abin mamaki sai kuma ta tsinci kanta da yin wani murmushi. Yaya Ma'aruf ya had'u, shine kawai abinda ta ayyana a ranta. Abubuwa da yawa sun tsaya mata a rai a d'an wannan rik'on da yayi mata da sak'on da ya isar.
"Ban hanaki yimin shiga haka ba?"
Abinda ya fad'o ranta kenan, ta mik'e tsaye da saurinta ta nufi gaban madubi tana k'arewa jikinta kallo.
Rigar kam babu laifi, da a gidan Mami takeyi ba zata barta ta sanya ba duk da cewar ita bata ga aibunta ba, amma ba laifi tayi shara-shara.
Ta dauki top d'inta ta d'ora akai gami da zama a gefen gadon ta rik'e cikinta da ke wani irin kuwwa sakamakon yunwar da ta ji ta motsa mata. Saidai kuma batajin zata iya fita yana a falon, wai Bintu ce da jin kunyar Ma'aruf yau? Abin da ya bata mamaki kenan har yasa ta murmusawa.
Haka ta zauna tana sak'e-sak'en zuci. Ta rasa yanda zata fassara hakikanin matsayin da ta ajiye Ma'aruf. D'an uwan ne ko Mijin? To ai kuwa tuni a matsayin mijin yake ko ta k'i kuwa. Saidai fa bata sonshi, shine babbar hujjar da ta kafawa kanta har take tak'ama da shi. Ya za'ayi ta mance munanan kalamansa a kanta? Ai ya nuna ita d'in yarinya ce babu abinda zaiyi da ita, to kuwa zai yi nadamar furucinsa, shiga kuwa na English wears, yanzu ta soma. Jikinta ne kuwa, ta daina bari ya maimaita wannan abu da yayi. Ta sauke ajiyar zuciya tayi shiru tana jira ya bar falon. Ta jima zaune kafin ta jiyo motsinsa wajen kicin sai kuma da jimawa ta ji ya rufe k'ofarsa. Saida ta bari aka d'anyi mintuna ta lek'o, ganin duhu a falon ya tabbatar mata lallai ya kwanta kenan. Kunna fitilar ta yi ta ware ido, babu ledojin a tsakar falo hakan ya sanyata nufar kicin, nan ta ci karo da su a saman firij.
Haka ta koma dakinta ta rufe gam da mukulli bayan ta dauki komai na bukatarta.
* * *
Washegari ya kama Asabar, abinda ya sanya Bintu jin babu dadi, tana son gasa shi, saidai ta lura ta soma d'an jin nauyinsa don abinda yayi, ashe daman da gaske ne da ta ji ana cewa ana samun wani sauyi a jiki idan irin hakan ta faru a lokacin? Ita kam sai yanzu ta gaskata. Bata mantawa akwai sadda suke hira da Aisha akan ire-iren lamuran nan, ta 6alli rakenta tana tsotsa gami da lumshe ido.
"Banza kawai, jeki haukan soyayya ya kasheki kawai, gwara miki shan rake kullum kiyita sha kina nishadi abinki, da wata soyayya."
Bata manta amsar Aisha alokacin.
"Hum, bakisan menene ma'anar kalmar ba, kedai Allah Yasa wataran ki ji yanda..."
Bata manta yanda ta toshemata baki wai kada tayi mata mugun fata. Aisha ta fisge hannunta tana dariya kafin tace.
"Wallahi akwai abinda idan anyimiki ba zaki iya magana ba. Ke bakinki mutuwa zaiyi, zaki fahimci shegen kuri ne kawai kikeyi."
Dariya tayi ta cigaba da shan rakenta kawai.
Bintu ta numfasa ta mik'e cike da kwarin gwuiwa, ba fa zata bari tayi saurin karaya ba, lallai idan ta nunamishi sanyi da kuma nauyinsa da take ji zai fahimci yayi nasara akanta. Har alokacin tana jin 6acin ran zancen da yaje.
Har ta fito ta kammala komai bai fito daga d'akinsa ba, daman bata tsammatar hakan tunda yau babu aiki. Ta koma d'akinta tayi wanka, har ta dauko kananun kaya sai tayi murmushi ta mayar, gaskiya a yau dai ba zata iya sanyawar ba amma hakan ba wai yana nufin ta bar alak'a da su bane tunda sun zame mata kamar atamfa.
Ta sanya doguwar riga ta atamfa, hoda kawai ta shafa sai man le6e.
A falo tana zaune tana karyawa sai gashinan ya fito. Ko wanka baiyi ba, daga shi sai riga da wando dogo na bacci na (pyjamas). Ya zauna saman kujera. Bata ko kalleshi ba sai ma ta had'e fuska. Ido ya zubamata, haka kawai ya ji ta burgeshi yanda ta had'e fuskar. Ya bi d'an bakinnata da kallo kawai, shi kansa a yanzun sai yakejin kunyarta amma kasancewarsa namiji, ya maze har da wani had'e gira kad'an.
"Ina kwana." Ya gaisheta da gatse.
Sai kuma bataji dadin gaidashin da bata yi ba. Ta gaisheshi, ya amsa kafin yayi umarnin ta had'amishi abin kari. Babu musu ta had'a ta ajiye a gabansa.
Yana wani muzurai yana shan tea shi a dole kada yarinya ta ga fuskar rainashi. (Ikon Allah)
Har ta kammala ta mik'e babu wata magana da ta k'ara shiga tsakaninsu. Ya bita da kallo, sai yaga kamar ma atamfar ta fi yi mata kyau sosai. Ya kawar da wannan tunanin kamar yanda ya saba kaudawar duk lokacin da ya taso.
Haka suka ci hutun karshen satin kowannensu na kokarin nuna jarumtarsa a fuska, alamun fa babu wani abu a zuciya.
Ranar litinin tana zauna a falo bayan ta dawo daga makaranta, bayan ya dawo aiki yake sanarmata da tafiyar da ta kamashi zuwa Lagos, bisa wani aiki da zaiyi a karkashin branch na kamfaninsu dake can. Ai a take ta soma washe hak'ora.
"Yaushe ne tafiyar?"
Ya zauna yana dubanta fuska a sake.
"Oh, wato murna ma kikeyi?"
Ta rufe baki adalilin dariyar farincikin da ya taho mata.
"A'a, ai idan dadi yayi yawa kuka akeyi, nima bakinciki ne yayi yawa shiyasa ni darawa."
Ya jinjina kai ya dubi gefe yana murmushi mai bayyana hak'ora kafin ya dubeta.
"Bansan lokacin da raininki gareni ya k'aru har haka ba."
Ya mik'e tsaye, ya soma tafiya hanyar d'akinsa.
"Gobe zan wuce in sha Allah, mungama magana da Mami, Aisha zata zo ta tayaki zama."
Wani ihun murna ta saki wanda ya sanyashi juyowa. Da sauri tayi narai-narai da fuska.
"Toh Yaya, Allah Ya kiyaye."
Ya d'an zubamata ido sai kuma ya juya ya shige.
Murna bai barta ta k'arasa abinda takeyi ba, ai gwara ya d'anyi k'aura daga gidan ko ta sha iska. Haba, Kullum mutum yana gida idan ya taso ofis sai kace ba shi da abokai. Ta ja k'aramin tsaki kawai.
Shi kuwa mamaki ta ba shi ganin yanda take murna da tafiyarsa, wannan na nufin Bintu bata damu da shi ba? Ya tunano a baya idan wata 'yar tafiya ta sameshi yanda Ma'u ke damuwa har ta kai ga zubda ruwan hawaye na rashin son tafiyarsa. Amma yau ga Bintu ta zo matsayin matarsa, bata jin ko d'ar na tafiyar da zaiyi. Jikinsa ya d'anyi sanyi, haka kawai baiji dad'in yanda ta nuna d'in ba. Ya damu iyaka damuwa har saida ya gaza jurewa a ranar da zai tafi ya dubeta.
"Meyasa bakiyi bakinciki da tafiyata ba?"
Ta ji tambayar babu zato, sai kuma ta yi murmushi.
"To ai kaima zaka huta da ni, tunda kace ina matsawa rayuwarka. Kuma kace ni ba komai ka d'aukeni ba ko?"
Ya rasa kuma bakin magana. Ya watsamata wani kallo mai nuni da jin haushin kalamanta sannan ya sanya kai ya fita jaye da Trolley dinsa. Ta dafe bango da hannunta tana binsa da kallo gami da doka uban hamma. A hankali tace "Allah Ya kaika lafiya. Bari nayi baccina har na gaji ba takura."
Ta rufe k'ofar ta koma ciki, lokacin bakwai da mintuna na safe. Abin ya yi mata dadi don kuwa bata da paper.
[7/23, 11:59 AM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)