Sashe 11
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Gaban Ma'aruf ya fad'i, ya soma ambaton Allah.
"Ina saurarenka Abbana."
D'akin ya d'anyi shiru kafin kuma Abba ya soma magana. Saida ya soma na nasihohi masu nuni da muhimmancin yarda da k'addara kafin ya gangaro zuwa ga abinda yakeson fad'a.
"Madallah, a matsayina na mahaifinka, ina mai neman amincewarka wajen had'aka aure da 'yar uwarka Fatima Bintu matuk'ar hakan bazai zamto cutarwa ba ga rayuwar d'ayanku. Ka sani, bani da burin tursasaka, ko a farkon aurenku ma kaida d'an uwanka ban tursasa d'ayanku ba, saidai kowannenki da kansa ya za6i matar aure. A wannan karon ma, ba hakan nakeson ayi ba. Na baka nan da kwanaki uku, kayi tunani ka yanke abinda kaga ya dace. Idan baka k'aunarta, to lallai ka sani, ba zan tursasa maka aurenta ba, hakanan itama Fatima Bintu, dukkan abinda tace akan lamarin, to fa bazan takura mata ba. Daman zumunci na so had'awa."
Abba ya d'anyi shiru yana duban Ma'aruf wanda gaba d'aya ya gama shiga hali na rikita.
"Kana iya tafiya."
Ya mik'e jiki kamar ba nashi ba, haka ya bar d'akin a daddafe. Bai iya k'arasawa falon Mami ba, zama yayi a kujerar dake a barandar Abba ya zubawa farfajiyar gidan ido kawai. Bintu? Bintu fa?!! Ita kuma Abba ya hango mishi matsayin abokiyar rayuwa? Ya Ilahi!
Saida ya kwashi mintoci kusan uku kafin ya mik'e ya bar wajen. Abba ya sauke labule ya koma saman dardumarsa ya zauna gami da d'aga hannu ya yi addu'ar neman abinda yafi alheri. Fatansa ya ga wannan aure ya tabbata.
A can kuwa, Ma'aruf fa ya shiga tara ba uku ba, kansa ya d'aure matuk'a. Meya kawowa iyayensa wannan tunanin? Su rasa wanda zasu hasko a matsayin matarsa sai Bintu? Yarinyar da kunya bata isheta ba?
Ya runtse idanu sannan ta bud'esu, nan da nan suka kad'a. A yau mutuwar Ma'unsa ta dawo mishi sabuwa fil! Ba don mutuwa ta mishi YANKAR KAUNA ba, yaushe iyayensa zasuyi tunanin aura mishi wata Bintu? A yau ya k'ara jin kewa mai d'umbin yawa na Ma'unsa. A gefe guda wani iri tsanar Bintu yake ji.
("Wai kai Malam wane irin naci ne haka? Tun d'azu kake bina, na gayamaka bana sonka, ko dole ne?!!")
( "Wallahi koda wasa kada kayi gangancin ta6a lafiyata, ana so dole ne? Ba gayamaka bana sonka!")
Ya runtse ido ya bud'e duk a lokaci guda. Cikin zafin nama ya mik'e ya nufi firij, ruwa ya ciro ya soma kwankwad'a kafin wani sanyi ya ziyarci ruhinsa. Lallai zai koyawa yarinyar hankali, zai tabbatar mata cewar ita d'in marar kunyar k'arya ce.
Alokaci guda ya saki wani guntun murmushi.
* * *
A gidan Rufa'i kuwa Bintu ta sake sai hada-hadar tafiya gidan yini sukeyi tare da Hajara wacce itama zata je. A ranar ne kuma za'ayi Dinner Party, ta kama dole da yamma ta koma gida don kwata-kwata Mami bata had'o mata da ankonsu na Dinner ba.
Bayan sun kammala, Rufa'i da kanshi ya saukesu wajejan uku na rana. A can suka iske Mami itama da Atine har da Hanif. Nan ta hau tambayar Binti dalilinta na k'in komawa gida, dariya kawai Bintu tayi bata ce mata komai ba. Ganin bata da niyyar maganar ta kyaleta. Aisha kawai ta sanarwa, saidai alokacin ta fahimci jini d'aya ba wasa ba, don kuwa da gaske Aisha ta ji babu dad'in abinda ta yiwa Yayanta. Bintu ganin haka itama ta watsar da ita, saidai basu ci ko rabin awa ba, Aisha ta sauke fushinta, ita d'in ko kusa bata da rik'o.
Da yamma Mami ta had'a Bintu da direba domin zuwa d'auko kayanta na dinner. A karshe Bintun tace zata fito kawai daga nan gidan. Yana sauketa, ya juya wajen Mami don su d'inma zasu halarci Dinner, kasancewar har da iyaye.
Ta dubi farfajiyar gidan, wani sanyi ya ziyarci zuciyarta ganin babu motar Ma'aruf wannan ya bata tabbacin baya gidan. Hankalinta kwance ta shiga.
Wanka ta soma yi sannan ta d'ora alwala. Saida ta idar da Magrib sannan tayi zaman gaban madubi ta shiga fente fuskarnan nata da kwalliya. A fili take fad'in.
"Yau zan kece raini."
Ta kammala shafe-shafenta sannan ta fiddo orange lace d'in da sukayi na 'yanmata, d'inkin doguwar riga(fitet gown) ta zura. Nan ta k'ara zaman tafkeken ribbons dinta sannan ta d'ora nad'in da sukayo akanta.
Ta saki baki tana duban kanta a madubi, iyakar had'uwa ta had'u. Wayarta dake k'ara tun d'azu tana yankewa, sai lokacin tayi niyyar d'agawa.
"A'i ya dai?"
K'arar da ta ji ya bata tabbacin sun kama hanya.
"Kin fito? Mami tace ki tsaya ga Yaya Ma'aruf zai taho ku fito tare."
"Tab!"
Da sauri ta katse wayar, ta jera da wa? Ita kuwa me ya kaita wannan gangancin. Da sauri-sauri ta had'a 'yar jakarta ta zura takalminta tana magana a fili.
"Hauka nakeyi zan fita da Yaya Ma'aruf? Kasheni kawai zaiyi "
Saidai me?
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
"Ina saurarenka Abbana."
D'akin ya d'anyi shiru kafin kuma Abba ya soma magana. Saida ya soma na nasihohi masu nuni da muhimmancin yarda da k'addara kafin ya gangaro zuwa ga abinda yakeson fad'a.
"Madallah, a matsayina na mahaifinka, ina mai neman amincewarka wajen had'aka aure da 'yar uwarka Fatima Bintu matuk'ar hakan bazai zamto cutarwa ba ga rayuwar d'ayanku. Ka sani, bani da burin tursasaka, ko a farkon aurenku ma kaida d'an uwanka ban tursasa d'ayanku ba, saidai kowannenki da kansa ya za6i matar aure. A wannan karon ma, ba hakan nakeson ayi ba. Na baka nan da kwanaki uku, kayi tunani ka yanke abinda kaga ya dace. Idan baka k'aunarta, to lallai ka sani, ba zan tursasa maka aurenta ba, hakanan itama Fatima Bintu, dukkan abinda tace akan lamarin, to fa bazan takura mata ba. Daman zumunci na so had'awa."
Abba ya d'anyi shiru yana duban Ma'aruf wanda gaba d'aya ya gama shiga hali na rikita.
"Kana iya tafiya."
Ya mik'e jiki kamar ba nashi ba, haka ya bar d'akin a daddafe. Bai iya k'arasawa falon Mami ba, zama yayi a kujerar dake a barandar Abba ya zubawa farfajiyar gidan ido kawai. Bintu? Bintu fa?!! Ita kuma Abba ya hango mishi matsayin abokiyar rayuwa? Ya Ilahi!
Saida ya kwashi mintoci kusan uku kafin ya mik'e ya bar wajen. Abba ya sauke labule ya koma saman dardumarsa ya zauna gami da d'aga hannu ya yi addu'ar neman abinda yafi alheri. Fatansa ya ga wannan aure ya tabbata.
A can kuwa, Ma'aruf fa ya shiga tara ba uku ba, kansa ya d'aure matuk'a. Meya kawowa iyayensa wannan tunanin? Su rasa wanda zasu hasko a matsayin matarsa sai Bintu? Yarinyar da kunya bata isheta ba?
Ya runtse idanu sannan ta bud'esu, nan da nan suka kad'a. A yau mutuwar Ma'unsa ta dawo mishi sabuwa fil! Ba don mutuwa ta mishi YANKAR KAUNA ba, yaushe iyayensa zasuyi tunanin aura mishi wata Bintu? A yau ya k'ara jin kewa mai d'umbin yawa na Ma'unsa. A gefe guda wani iri tsanar Bintu yake ji.
("Wai kai Malam wane irin naci ne haka? Tun d'azu kake bina, na gayamaka bana sonka, ko dole ne?!!")
( "Wallahi koda wasa kada kayi gangancin ta6a lafiyata, ana so dole ne? Ba gayamaka bana sonka!")
Ya runtse ido ya bud'e duk a lokaci guda. Cikin zafin nama ya mik'e ya nufi firij, ruwa ya ciro ya soma kwankwad'a kafin wani sanyi ya ziyarci ruhinsa. Lallai zai koyawa yarinyar hankali, zai tabbatar mata cewar ita d'in marar kunyar k'arya ce.
Alokaci guda ya saki wani guntun murmushi.
* * *
A gidan Rufa'i kuwa Bintu ta sake sai hada-hadar tafiya gidan yini sukeyi tare da Hajara wacce itama zata je. A ranar ne kuma za'ayi Dinner Party, ta kama dole da yamma ta koma gida don kwata-kwata Mami bata had'o mata da ankonsu na Dinner ba.
Bayan sun kammala, Rufa'i da kanshi ya saukesu wajejan uku na rana. A can suka iske Mami itama da Atine har da Hanif. Nan ta hau tambayar Binti dalilinta na k'in komawa gida, dariya kawai Bintu tayi bata ce mata komai ba. Ganin bata da niyyar maganar ta kyaleta. Aisha kawai ta sanarwa, saidai alokacin ta fahimci jini d'aya ba wasa ba, don kuwa da gaske Aisha ta ji babu dad'in abinda ta yiwa Yayanta. Bintu ganin haka itama ta watsar da ita, saidai basu ci ko rabin awa ba, Aisha ta sauke fushinta, ita d'in ko kusa bata da rik'o.
Da yamma Mami ta had'a Bintu da direba domin zuwa d'auko kayanta na dinner. A karshe Bintun tace zata fito kawai daga nan gidan. Yana sauketa, ya juya wajen Mami don su d'inma zasu halarci Dinner, kasancewar har da iyaye.
Ta dubi farfajiyar gidan, wani sanyi ya ziyarci zuciyarta ganin babu motar Ma'aruf wannan ya bata tabbacin baya gidan. Hankalinta kwance ta shiga.
Wanka ta soma yi sannan ta d'ora alwala. Saida ta idar da Magrib sannan tayi zaman gaban madubi ta shiga fente fuskarnan nata da kwalliya. A fili take fad'in.
"Yau zan kece raini."
Ta kammala shafe-shafenta sannan ta fiddo orange lace d'in da sukayi na 'yanmata, d'inkin doguwar riga(fitet gown) ta zura. Nan ta k'ara zaman tafkeken ribbons dinta sannan ta d'ora nad'in da sukayo akanta.
Ta saki baki tana duban kanta a madubi, iyakar had'uwa ta had'u. Wayarta dake k'ara tun d'azu tana yankewa, sai lokacin tayi niyyar d'agawa.
"A'i ya dai?"
K'arar da ta ji ya bata tabbacin sun kama hanya.
"Kin fito? Mami tace ki tsaya ga Yaya Ma'aruf zai taho ku fito tare."
"Tab!"
Da sauri ta katse wayar, ta jera da wa? Ita kuwa me ya kaita wannan gangancin. Da sauri-sauri ta had'a 'yar jakarta ta zura takalminta tana magana a fili.
"Hauka nakeyi zan fita da Yaya Ma'aruf? Kasheni kawai zaiyi "
Saidai me?
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)