Sashe 3
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
<<05>>
Kuka har da sheshshek'a takeyi sakamakon marin da ta sha a hannun Yaya Ma'aruf a dalilin take mishi yatsu da tayi da takalminta, Mami bata ce komai ba ta bi mijinta wanda ya rigasu shigewa gidan, ba'a gabanshi akayi marin ba. Ita kanta yau Bintu ta 6ata mata rai, har kusan fad'awa tayi kan wata tsohuwa wajen idi, tsohuwa ba hakuri tayita 6a6atu, saida Mami ta sanya baki tayi shiru. Mami ta dakawa Bintu tsawa akan maza-maza ta cire takalmin ta rik'eshi a hannu saidai tayi tafiyar haka.
Bintu ta k'ara rushewa da kuka, tana murnar Mami bata doketa ba, yanzu gashinan ta takewa Yaya Ma'aruf yatsun k'afa ya mareta. Haka tayi cikin gidan, Rufa'i na kwala mata kira don ya rarrasheta amma ko juyowa batayi ba.
Tana zaune tana kuka da jaye-jayen Allah Ya isa, Aisha kuwa banda dariya babu abinda takeyumi mata. Tun Bintu na jin haushinta har itama ta hau dariya tunanowa da yanda ta dage akan takalmin. Tayi kwafa.
"Allah kuwa sai ma na tonamai asiri."
"Asirin me?" Cewar Aisha.
Bintu ta k'ara yin kwafa.
"Kedai ki zuba ido."
Kiran da Mami ta kwala musu ne ya katse hirar. Bintu tace ita babu inda zata je. Haka Aisha ta fice ta barta.
Bata fita ba saida Mami ta shigo da kanta ta d'an yi mata fad'a kafin kuma ta sauko tana rarrashinta, haka ta fito tana zum6ure-zum6uren baki. Anan saman kafet ta tarar da kowa har Abba anyi zaman cin cin abinci. Ta dubi Yaya Ma'aruf ta dauke kai, a ranta tana fad'in.
"Ai sai na tonamaka asiri kwanan nan, d'an iska kawai."
Abba na murmushi yace "Haba Bintu, wanene ya ta6aki? Zo ki gayamin."
Ta k'arasa ta zauna, saidai bata iya cewa komai ba ganin Ma'aruf.
Suka soma cin abin, Abba na janta da hira har ta sake.
Bayan sun kammala, ita da Aisha suka kwashe kwanukan suka nad'e ledar cin abincin sukayi kicin.
Ranar sun sha yawo tare da Rufa'i.
* * *
Washegari sai wajejan k'arfe goma Bintu ta farka. Ta kasa kunne sosai jin hayaniyar mutane daga falon Mami. Hakan yasa ta fito daga ita sai riga da wando na bacci. Ta d'an la6e, tana kyallara ido ta gane duk 'yan uwan Abba ne, babu wacce ta soma ganewa sai Anti Ma'u. Kwafa tayi, har cikin ranta ta ji dad'in ganinta, a fili tace "Yau asirinku zai tonu."
Ta koma ciki ta fad'a wanka itama. Bayan ta fito tayi kwalliyarta harda jagira irin k'atuwar nan saidai nata yayi girma da yawa. Ta dubi matar jikin kwalin eye shadow, ta dubi kanta kafin ta ja tsaki, ba iri d'aya bane kwalliyarsu. Cikin ikon Allah, sai ga Aisha ta shigo. Tana kallon fuskar Bintu ta soma kyakyata dariya. Bintu ta hau tayata.
"Don Allah zo ki yimin kwalliya wacce ta ci uban ta jiya. Yau zan nunawa wata bata da wayo."
Aisha ta saki baki ta kama"Toh, wacece kuma?"
"Baruwanki Malama, yimin don Allah."
"Goge, ke wanke fuskara gaba d'aya."
Da gudu-gudu ta fad'a band'akin ta wanko ta dawo ta zauna. Cikin kwarewa irin na Aisha, da baiwarta da Allah Yayi mata na iya tsantsara kwalliya tayi mata kwalliya gami da sanyamata eye-shadow wanda a baya sam Bintu bata amincewa ta sanya. Ai kuwa tayi kyau fiye da zato. Banda "Masha Allah, Subhanallah." Babu abinda Aisha ke ambata, ta k'arashe da "Wallahi kin fi koyaushe kyau tun zuwanki baki ta6a kwalliya irin na yau ba."
Bintu tayi farr da ido, kai kace wata budurwar azo a gani ce.
"Nasani." Aisha ta kai hannu zata goge mata ta kauce tana dariya.
"Au godiya zanyi fa."
Aisha zata fita ta tsaidata.
"Aramin wayarki." Ta mik'a mata ta fita.
Ta hau dannawa, gaba d'aya ta mance yanda Aisha ta koyamata daukar hoto. Ta dire wayar da zummar da zarar ta kammala zataje d'an dolo mai wankinsu ya koyamata don batason Aisha tasan abinda zata aikata.
Ta had'e tsaf cikin atamfa ja da fara, d'inkin ya zauna d'abas a jikinta, tayi d'aurin d'ankwalinta na sabo, ta sak'alo jelun wuyanta ta k'ulle. Cikin sa'a sai ga Aisha ta dawo d'akin, tana ganin haka ta gyara mata. Bayan fitarta, Bintu ta fesa turare ta janyo flat shoe din da Rufa'i ya za6omata ta sanya. Aganinta bayar da kai ne ta fad'i a gaban Anti Ma'u, ita daman sam jininta bai had'u da ita ba, sai kuma yanzu ta k'ara gano silar rashin had'uwar jininsu, 'yar iska ce.
Ta d'auki wayar Aisha ta fito da niyyar zuwa wurin d'an dolo.
¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<06>>
"A'ah Bintuuu!!" Fad'in 'yan matan kenan sa'anninta. Kasancewar gaba d'aya sun santa. Tayi musu murmushi kafin ta k'araso kamar wata mutuniyar kirki ta zauna. Nan suka gaisa, ko kallon Anti Ma'u batayi ba. Har saida Anti Ma'un tayi magana.
"A'a, Bintu yau abin ba magana?"
Sai lokacin ta d'an yamutse fuska tace "Ina wuni."
"Bazan amsa ba tunda saida na rok'a." Fad'in Ma'u cikin fushi, bata ga abinda ta tarewa yarinyar nan ba da ta tsaneta. Ta kusa daina shiga harkarta. Bintu ta mik'e tana dariya.
"Ina zuwa."
Bata saurari kowa ba ta fice daga falon tana wani jijjiga jiki a dole tafiyar Ma'u take kwaikwaya. Aisha dariya ta su6uce mata sakamakon ta fahimci ko da wa Bintun take. Ma'u ta gane saidai ta basar.
Tana fita harabar gidan fa nutsu ta soma tafiyarta sak. Ta dubi hagu da dama, bata hango d'an dolo ba, dole tayi gaba wajen maigadinsu. Yana ganinta ya washe baki. "A'a, d'iyata, wannan cakarewa haka?"
Bintu ta rik'e k'ugu tana murmushi.
"Nagode Baba, kasan inda d'an dolo ya shiga?"
"Ganinan!"
Cewar d'an dolo da babbar murya a sa'ilin da yake bud'e kyaure ya sanyo kai, hannunsa rik'e da mp3 yana jin wak'a.
"Yauwa, zo muyi sirri."
Tayi gaba ya bi bayanta har zuwa wajen shukoki. Ta dubi kusa da su babu kowa, ta mik'a mishi wayar Aisha.
"Gwadamin yanda zan d'auki hoto."
D'an dolo yayi dariya.
"Kai, sau biyar kenan ina gwadamiki. Wane irin kwanya gareki?"
Ta harareshi. "Malam idan bazaka koyamin ba, bani waya."
"A'a yi hakuri." Ya soma nunamata yanda zatayi, kafin tace bari ta gwada. Ta nunoshi da wayar. "Gyara nayi maka hoto mugani."
Yayi tsayuwar DAB😜, ta kyalkyale da dariya kafin ta daukeshi.
"Lah kaga ya yi."
Suna cikin haka, Yaya Ma'aruf yazo wucewa. Ai da sauri D'an dolo yabar wurin. Ma'aruf ya bishi da kallo kafin ya maido dubansa ga Bintu cikin d'aurewar fuska.
"Ke, banyi miki gargad'i ba akan wasa da yaron nan ba ne?"
Ta turo baki, bata da niyyar magana don har lokacin bata bar jin haushinsa ba. Ya matso, ta matsa a tsorace. Ganin yana shirin cafkar kunnenta ya sanyata yin magana babu shiri.
"Wayyo, kwa.. Au, wallahi abu ya nunamin. Kayi hakuri bazan sake ba."
Ta k'arashe tana dafe da kuncinta. Ya zubamata ido cikin kallon raini. Ganin kamar bai wuce ba tayi magana.
"Anti Ma'u ma ta zo."
Jin abinda tace ya bashi dariya, hakan ya sanyashi murmushi mai ban sha'awa. Bintu bata ji. Tayi sak'ale tana kallon abin kamar a mafarki har ta saki kuncinta. Ai kuwa ya mintsili kumatun ya ja.
"Sa'anki ne ni?"
Daga haka ya saketa ta juya sai gida. A ranta tana fad'in.
"Yau zan sanyaka kuka ai." Ta k'arashe da dariyar mugunta.
Nan ta zauna ta saki jiki anata hira, sai gashi ya shigo.
Kowannensu ya gaisheshi. Bintu ta zubamusu ido kamar talabijin, sai wani murmushi suke sakarwa juna.
K'arshe yayi mata wata magana k'asa-k'asa sannan ya mik'e ya fita. Fitarsa da mintuna biyu, ta mik'e ta bi bayansa. Gaba d'aya manya da k'ananan 'yan matan irinsu Bintu suka saki shewa. Mami ta fito daidai lokacin tana tambayar abinda yayi musu dadi.
"Bakomai." Suka amsa. Bintu ta faki idonsu ta fice ta hanyar kicin. Yau kam komai zai shiga wayarnan. Kai tsaye ta nufi sashen Ma'aruf.
Sad'af sad'af take takawa a barandar har ta kai jikin k'ofar. Ai kuwa ta ci karo da takalmin Ma'u. Ta numfasa ta waiwaya bayanta. Babu wanda ke tahowa. Taji k'arar kid'a, wannan ya bata tabbacin koda ta murd'a babu wanda zai ji cikinsu.
Ta murd'a k'ofar ta tura a hankali. Ashe dagaske 'yan iskan abinda zasu kuma yi kenan. A tsaye ta hangesu ya yiwa Ma'u kyakkyawar runguma. Hannunta na rawa ta ciro wayar Aisha daga rigarta ta saita ta d'aukesu hoto. Har kala uku, ta ci sa'a akwai wanda fuskokinsu gaba d'aya suka fito sosai. A sannu ta mayar da k'ofar ta rufeta kamar yanda take. Babu wanda ya ji cikinsu sakamakon kid'an dake tashi.
Saida tayi nesa kad'an da wajen ta hau kyakyata dariya har tana rik'e ciki.
"Zakuyi bayani ne."
* * *
Misalin takwas na dare babu kowa a falon Mami bak'o, dukkansu sune. Har Abba yana zaune tare da su ana hira. Can sai ga Bintu ta shigo, bayan tayi zaman dirshan akan gado tayita bincike har ta gane yanda ake bud'o hotuna. Ta dubi kowa tana murmushi. Babu wanda ta ji dad'in gani kamar Ma'aruf. Ya dubeta ta sakarmai murmushi, shima fuska a sake yake kallonta. A yau yana cike da farinciki baison abinda zai dagula lissafinsa.
Ta k'arasa ta gaida Abba. Ya amsa fuska a sake.
Can ana hira Bintu ta katse ta hanyar kiran sunan Abba. Kowa yayi shiru yana dubanta.
"Na'am 'yar Abba, ya akayi?" Cewar Abban.
Ta dubi Ma'aruf sannan ta dubi Mami sai kuma tayi shiru.
"Bintu ya akayi? Yi magana mana." Mami ta fad'a.
"Daman wani iskanci akeyi a gidannan nakeso yau kowa ya ganewa idanunsa."
A tsorace Aisha ta dubeta, haka su Abba, abin ya basu mamaki.
"Innalillahi, a gidana? Me kika gani?"
Ta fiddo wayar Aisha ta bud'o hoton ta mik'awa Abba.
"Kagani."
Abba ya kar6i wayar yana dubawa. Nan da nan ya daure fuska gami da mik'awa Mami, mik'ewa kawai yayi ya nufi falonsa.
¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Kuka har da sheshshek'a takeyi sakamakon marin da ta sha a hannun Yaya Ma'aruf a dalilin take mishi yatsu da tayi da takalminta, Mami bata ce komai ba ta bi mijinta wanda ya rigasu shigewa gidan, ba'a gabanshi akayi marin ba. Ita kanta yau Bintu ta 6ata mata rai, har kusan fad'awa tayi kan wata tsohuwa wajen idi, tsohuwa ba hakuri tayita 6a6atu, saida Mami ta sanya baki tayi shiru. Mami ta dakawa Bintu tsawa akan maza-maza ta cire takalmin ta rik'eshi a hannu saidai tayi tafiyar haka.
Bintu ta k'ara rushewa da kuka, tana murnar Mami bata doketa ba, yanzu gashinan ta takewa Yaya Ma'aruf yatsun k'afa ya mareta. Haka tayi cikin gidan, Rufa'i na kwala mata kira don ya rarrasheta amma ko juyowa batayi ba.
Tana zaune tana kuka da jaye-jayen Allah Ya isa, Aisha kuwa banda dariya babu abinda takeyumi mata. Tun Bintu na jin haushinta har itama ta hau dariya tunanowa da yanda ta dage akan takalmin. Tayi kwafa.
"Allah kuwa sai ma na tonamai asiri."
"Asirin me?" Cewar Aisha.
Bintu ta k'ara yin kwafa.
"Kedai ki zuba ido."
Kiran da Mami ta kwala musu ne ya katse hirar. Bintu tace ita babu inda zata je. Haka Aisha ta fice ta barta.
Bata fita ba saida Mami ta shigo da kanta ta d'an yi mata fad'a kafin kuma ta sauko tana rarrashinta, haka ta fito tana zum6ure-zum6uren baki. Anan saman kafet ta tarar da kowa har Abba anyi zaman cin cin abinci. Ta dubi Yaya Ma'aruf ta dauke kai, a ranta tana fad'in.
"Ai sai na tonamaka asiri kwanan nan, d'an iska kawai."
Abba na murmushi yace "Haba Bintu, wanene ya ta6aki? Zo ki gayamin."
Ta k'arasa ta zauna, saidai bata iya cewa komai ba ganin Ma'aruf.
Suka soma cin abin, Abba na janta da hira har ta sake.
Bayan sun kammala, ita da Aisha suka kwashe kwanukan suka nad'e ledar cin abincin sukayi kicin.
Ranar sun sha yawo tare da Rufa'i.
* * *
Washegari sai wajejan k'arfe goma Bintu ta farka. Ta kasa kunne sosai jin hayaniyar mutane daga falon Mami. Hakan yasa ta fito daga ita sai riga da wando na bacci. Ta d'an la6e, tana kyallara ido ta gane duk 'yan uwan Abba ne, babu wacce ta soma ganewa sai Anti Ma'u. Kwafa tayi, har cikin ranta ta ji dad'in ganinta, a fili tace "Yau asirinku zai tonu."
Ta koma ciki ta fad'a wanka itama. Bayan ta fito tayi kwalliyarta harda jagira irin k'atuwar nan saidai nata yayi girma da yawa. Ta dubi matar jikin kwalin eye shadow, ta dubi kanta kafin ta ja tsaki, ba iri d'aya bane kwalliyarsu. Cikin ikon Allah, sai ga Aisha ta shigo. Tana kallon fuskar Bintu ta soma kyakyata dariya. Bintu ta hau tayata.
"Don Allah zo ki yimin kwalliya wacce ta ci uban ta jiya. Yau zan nunawa wata bata da wayo."
Aisha ta saki baki ta kama"Toh, wacece kuma?"
"Baruwanki Malama, yimin don Allah."
"Goge, ke wanke fuskara gaba d'aya."
Da gudu-gudu ta fad'a band'akin ta wanko ta dawo ta zauna. Cikin kwarewa irin na Aisha, da baiwarta da Allah Yayi mata na iya tsantsara kwalliya tayi mata kwalliya gami da sanyamata eye-shadow wanda a baya sam Bintu bata amincewa ta sanya. Ai kuwa tayi kyau fiye da zato. Banda "Masha Allah, Subhanallah." Babu abinda Aisha ke ambata, ta k'arashe da "Wallahi kin fi koyaushe kyau tun zuwanki baki ta6a kwalliya irin na yau ba."
Bintu tayi farr da ido, kai kace wata budurwar azo a gani ce.
"Nasani." Aisha ta kai hannu zata goge mata ta kauce tana dariya.
"Au godiya zanyi fa."
Aisha zata fita ta tsaidata.
"Aramin wayarki." Ta mik'a mata ta fita.
Ta hau dannawa, gaba d'aya ta mance yanda Aisha ta koyamata daukar hoto. Ta dire wayar da zummar da zarar ta kammala zataje d'an dolo mai wankinsu ya koyamata don batason Aisha tasan abinda zata aikata.
Ta had'e tsaf cikin atamfa ja da fara, d'inkin ya zauna d'abas a jikinta, tayi d'aurin d'ankwalinta na sabo, ta sak'alo jelun wuyanta ta k'ulle. Cikin sa'a sai ga Aisha ta dawo d'akin, tana ganin haka ta gyara mata. Bayan fitarta, Bintu ta fesa turare ta janyo flat shoe din da Rufa'i ya za6omata ta sanya. Aganinta bayar da kai ne ta fad'i a gaban Anti Ma'u, ita daman sam jininta bai had'u da ita ba, sai kuma yanzu ta k'ara gano silar rashin had'uwar jininsu, 'yar iska ce.
Ta d'auki wayar Aisha ta fito da niyyar zuwa wurin d'an dolo.
¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<06>>
"A'ah Bintuuu!!" Fad'in 'yan matan kenan sa'anninta. Kasancewar gaba d'aya sun santa. Tayi musu murmushi kafin ta k'araso kamar wata mutuniyar kirki ta zauna. Nan suka gaisa, ko kallon Anti Ma'u batayi ba. Har saida Anti Ma'un tayi magana.
"A'a, Bintu yau abin ba magana?"
Sai lokacin ta d'an yamutse fuska tace "Ina wuni."
"Bazan amsa ba tunda saida na rok'a." Fad'in Ma'u cikin fushi, bata ga abinda ta tarewa yarinyar nan ba da ta tsaneta. Ta kusa daina shiga harkarta. Bintu ta mik'e tana dariya.
"Ina zuwa."
Bata saurari kowa ba ta fice daga falon tana wani jijjiga jiki a dole tafiyar Ma'u take kwaikwaya. Aisha dariya ta su6uce mata sakamakon ta fahimci ko da wa Bintun take. Ma'u ta gane saidai ta basar.
Tana fita harabar gidan fa nutsu ta soma tafiyarta sak. Ta dubi hagu da dama, bata hango d'an dolo ba, dole tayi gaba wajen maigadinsu. Yana ganinta ya washe baki. "A'a, d'iyata, wannan cakarewa haka?"
Bintu ta rik'e k'ugu tana murmushi.
"Nagode Baba, kasan inda d'an dolo ya shiga?"
"Ganinan!"
Cewar d'an dolo da babbar murya a sa'ilin da yake bud'e kyaure ya sanyo kai, hannunsa rik'e da mp3 yana jin wak'a.
"Yauwa, zo muyi sirri."
Tayi gaba ya bi bayanta har zuwa wajen shukoki. Ta dubi kusa da su babu kowa, ta mik'a mishi wayar Aisha.
"Gwadamin yanda zan d'auki hoto."
D'an dolo yayi dariya.
"Kai, sau biyar kenan ina gwadamiki. Wane irin kwanya gareki?"
Ta harareshi. "Malam idan bazaka koyamin ba, bani waya."
"A'a yi hakuri." Ya soma nunamata yanda zatayi, kafin tace bari ta gwada. Ta nunoshi da wayar. "Gyara nayi maka hoto mugani."
Yayi tsayuwar DAB😜, ta kyalkyale da dariya kafin ta daukeshi.
"Lah kaga ya yi."
Suna cikin haka, Yaya Ma'aruf yazo wucewa. Ai da sauri D'an dolo yabar wurin. Ma'aruf ya bishi da kallo kafin ya maido dubansa ga Bintu cikin d'aurewar fuska.
"Ke, banyi miki gargad'i ba akan wasa da yaron nan ba ne?"
Ta turo baki, bata da niyyar magana don har lokacin bata bar jin haushinsa ba. Ya matso, ta matsa a tsorace. Ganin yana shirin cafkar kunnenta ya sanyata yin magana babu shiri.
"Wayyo, kwa.. Au, wallahi abu ya nunamin. Kayi hakuri bazan sake ba."
Ta k'arashe tana dafe da kuncinta. Ya zubamata ido cikin kallon raini. Ganin kamar bai wuce ba tayi magana.
"Anti Ma'u ma ta zo."
Jin abinda tace ya bashi dariya, hakan ya sanyashi murmushi mai ban sha'awa. Bintu bata ji. Tayi sak'ale tana kallon abin kamar a mafarki har ta saki kuncinta. Ai kuwa ya mintsili kumatun ya ja.
"Sa'anki ne ni?"
Daga haka ya saketa ta juya sai gida. A ranta tana fad'in.
"Yau zan sanyaka kuka ai." Ta k'arashe da dariyar mugunta.
Nan ta zauna ta saki jiki anata hira, sai gashi ya shigo.
Kowannensu ya gaisheshi. Bintu ta zubamusu ido kamar talabijin, sai wani murmushi suke sakarwa juna.
K'arshe yayi mata wata magana k'asa-k'asa sannan ya mik'e ya fita. Fitarsa da mintuna biyu, ta mik'e ta bi bayansa. Gaba d'aya manya da k'ananan 'yan matan irinsu Bintu suka saki shewa. Mami ta fito daidai lokacin tana tambayar abinda yayi musu dadi.
"Bakomai." Suka amsa. Bintu ta faki idonsu ta fice ta hanyar kicin. Yau kam komai zai shiga wayarnan. Kai tsaye ta nufi sashen Ma'aruf.
Sad'af sad'af take takawa a barandar har ta kai jikin k'ofar. Ai kuwa ta ci karo da takalmin Ma'u. Ta numfasa ta waiwaya bayanta. Babu wanda ke tahowa. Taji k'arar kid'a, wannan ya bata tabbacin koda ta murd'a babu wanda zai ji cikinsu.
Ta murd'a k'ofar ta tura a hankali. Ashe dagaske 'yan iskan abinda zasu kuma yi kenan. A tsaye ta hangesu ya yiwa Ma'u kyakkyawar runguma. Hannunta na rawa ta ciro wayar Aisha daga rigarta ta saita ta d'aukesu hoto. Har kala uku, ta ci sa'a akwai wanda fuskokinsu gaba d'aya suka fito sosai. A sannu ta mayar da k'ofar ta rufeta kamar yanda take. Babu wanda ya ji cikinsu sakamakon kid'an dake tashi.
Saida tayi nesa kad'an da wajen ta hau kyakyata dariya har tana rik'e ciki.
"Zakuyi bayani ne."
* * *
Misalin takwas na dare babu kowa a falon Mami bak'o, dukkansu sune. Har Abba yana zaune tare da su ana hira. Can sai ga Bintu ta shigo, bayan tayi zaman dirshan akan gado tayita bincike har ta gane yanda ake bud'o hotuna. Ta dubi kowa tana murmushi. Babu wanda ta ji dad'in gani kamar Ma'aruf. Ya dubeta ta sakarmai murmushi, shima fuska a sake yake kallonta. A yau yana cike da farinciki baison abinda zai dagula lissafinsa.
Ta k'arasa ta gaida Abba. Ya amsa fuska a sake.
Can ana hira Bintu ta katse ta hanyar kiran sunan Abba. Kowa yayi shiru yana dubanta.
"Na'am 'yar Abba, ya akayi?" Cewar Abban.
Ta dubi Ma'aruf sannan ta dubi Mami sai kuma tayi shiru.
"Bintu ya akayi? Yi magana mana." Mami ta fad'a.
"Daman wani iskanci akeyi a gidannan nakeso yau kowa ya ganewa idanunsa."
A tsorace Aisha ta dubeta, haka su Abba, abin ya basu mamaki.
"Innalillahi, a gidana? Me kika gani?"
Ta fiddo wayar Aisha ta bud'o hoton ta mik'awa Abba.
"Kagani."
Abba ya kar6i wayar yana dubawa. Nan da nan ya daure fuska gami da mik'awa Mami, mik'ewa kawai yayi ya nufi falonsa.
¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)