← Book details Bintu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 33

Sashe 25

Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

  Ta rufe gidan ta bi bayanshi. Gaban motar ta zauna shima ya shiga ya tayar.
  Ta saci kallonsa, sai kawai ta ji ya burgeta ganin kamar yau din yana cike da nishad'i.
  Tunaninta ya tafi a inda zasuje, sai ware ido takeyi. Shima baice mata uffan ba. Ganin sun shiga layin gidansu ta saki ihu murna.
  "Ke banason hauka!" Ya fad'a cikin fad'a-fad'a.
  Ta nutsu tana dariya.
"Wallahi Yaya wani dad'i ne ya rufeni."
  Yayi murmushi kawai batare da yace uffan ba. Ji takeyi kamar ta 6alle murfin motar ta fad'a ciki tun kafin maigadinsu ya bud'e gate.
  Ai kuwa yana shiga da fakin ta bud'e murfi ta fita da saurinta ko waigowa batayi ba ballantana ta rufe mishi k'ofar motar.
  "Mamina! Mamina!!"
  Ta hau kwala kira. Da Aisha suka soma cin karo kuwa, duk da cewar sun saba ganin juna a makaranta, amma yau ganin na gida daban yake da na koyaushe. Fitowar Mami ya sanya Bintu runtumawa a guje ta rungumeta. Mami itama rungumeta tayi tana mai cike da tsantsar farincikin ganin yanda d'iyarta ta k'ara k'iba da kyawu.
  Ma'aruf da Aisha sai abin ya burgesu, wannan k'auna da Mami da Bintu ke yiwa juna daga Allah ne kawai.
  Can kuma ta saketa tana dariya gami da kwantar da kai a kafad'arta.
"Wallahi Mamina nayi kewarki da yawa."
  Mami ta rik'e hannunta suka k'arasa suka zauna.
"Nima nayi Bintuna, amma nagode Allah da yanda na ganki kinyi kyau."
   Ya k'araso ya zauna gami da gaida Mami. Ta amsa cike da farinciki. Yau wani dadi takeji. Nan fa suma masu aikin suka hau murnar ganin Bintu abokiyar hirarsu.
  Abba ma yana shigowa ya zauna a falon ransa fari k'al. Hira sukeyi kamar ba surukanta ba. Bayan Abba da Ma'aruf sun shiga falonsa ne Mami ke labarta mata cewa ansanya ranar bikin Aisharta nan kusa.
  Baki ta saki da mamaki.
"Amman Aisha bata gayamin ba?"
Aisha ta harareta da wasa. Mami ta amsa tana murmushi.
"Kwana uku kenan da kawo kud'in, nan da watanni uku za'ayi."
  Kai, ranar Bintu ta yi murnar da ta jima batayi ba. Idan ka ganta da Ma'aruf a gaban iyayen saika rantse babu wata 6araka a tsakaninsu.
   Har takwas na dare tana gidan. Lokacin ne kuma Ma'aruf ya dawo daga 'yar unguwar da ya je. Ya zauna yana duban yanda ta yi filo da cinyar Mami ta d'ora Hanif akan ruwan cikinta tana shan cakulet tana lasa mishi suna hira a haka.
Ya girgiza kai yana duban Mami.
"Mami kina son sangarta yarinyar nan, bansan dalili ba."
Ta shafa kan Bintu tana murmushi.
"Sunanmu d'aya, bani da kamarta."
Bintu ta lumshe ido ta bud'esu akan Ma'aruf. Ya ji wannan ya basar.
"Hakane. Sai ki taso mu tafi."
Ta nark'e murya.
"Kai Yayana tun yanzu?"
Ganin gaban Mami ne yasa shi yi mata murmushin dole.
"Au, da kwana zamuyi?"
Mami ta sanya baki. Haka Bintu ba don ta gaji da ganin Maminta ba ta shirya suka tafi bayan Mami ta yi mata alk'awarin zuwa.

[7/22, 3:58 AM] ‪+249 99 842 9948‬: ¶°°BINTU°°¶

©Rufaida Omar
(July...2016)

<<37>>
A mota suna tafe ya dubeta.
"Kinason Mami."
Ta numfasa da murmushi dauke saman fuskarta.
"Tana sona shiyasa."
Kamar yayi mata wata tambaya sai kuma ya share. Ya dubeta.
"Zakiyimin rakiya zance ne ko na mik'a ki gida?"
Tambayar ta zo mata iya wuya, shima d'in ya fad'a ne don ya ga yanda zatayi.
"Kaini gida." Ta fad'a kusan a k'ufule. Baice uffan ba ya kad'a kan motar zuwa gida. Tana ganin tamkar wasa yakeyi, saidai kuma ta gane lallai dagasken yakeyi don a k'ofar gidan ya faka motar gami da dannan mabud'i ta gefensa. Dubansa tayi, bai dubeta d'in ba, saidai murmushi da yakeyi na mugunta. Ta bud'e a fusace ta fice.
Saida ya ga shigarta sannan yayi dariya kad'an ya d'agawa Audu maigadi hannu.
"Ina dawowa yanzu."
Daga haka ya bar layin. Wasa yakeyi mata domin kuwa abin motsa baki yakeson zuwa siyomusu.
Bintu a fusace ta k'arasa ta bud'e kofar ta shiga. Ta kasa ta6uka komai, ta shiga safa da marwa falon bayan ta yar da jaka da mayafi da dankwali. A haka ta soma rage kayan jikinta. Ina Ma'aruf yaje? Wajen sauran cocaine(Sa'a) ko kuma Lawisa? Ran Bintu fa babu dad'i ta shiga wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa.
To me hakan ke nufi? Me zai dameta da fitar Ma'aruf zance?
Ta zauna daga ita sai undies, a fili kuma tayi furucin.
"Ai ba wani abu tsakaninmu, me zai dameni?"
Ta kusan mintuna uku, ta kasa hakuri ta fiddo wayarta a jaka. Ta lalubo wayarta ta nemo lambarsa.
"Angrybird." Shine abinda ta rubuta a sunan Ma'aruf. Haka ta danna kira.
Lokacin yana hanyar gidan, ya d'auko wayar ya duba. Baisan lokacin da ya dara ba ganin Bintu ce. Bai d'aga ba har ta yanke.
Sai lokacin Bintu ta ji haushin kanta sosai, ta ja tsaki gami da tattara kayanta zuwa d'aki. Haka kawai baya sonta sai ya zama ya dunga wulak'antata. Kawai ta soma zubar hawaye.
"To me zai dameki wai?"
Wata zuciyar ta k'ara jefomata tambayar da ta sanyata share hawayenta gami da mik'ewa. Wankan ma bazatayi ba, kawai ta bud'e cupboard d'inta ta d'auko rigar bacci doguwa har k'aurinta mai k'aramin hannu. Tana da (top) saidai ko bi ta kansa batayi ba, haushi da wani mugun abu da batasan ko menene ma ya tokare wuyanta.
Duk da 'yar yunwar da take ji, haka ta nemi makwanci. Babu yanda Mami batayi ba akan su tafi da abinci ya k'i, ashe don ya shiryamata mugunta yayi hakan. Tayi kwafa, zuciyarta tayi wani irin rauni, yanzu shi yana can yana dariya a gaban budurwarsa. Hawaye ta ji ya silalo mata. Ba zato kuma ta ji hon d'in motarsa.
Ta mik'e da sauri ta lek'a, ganin dagaske shi d'inne yasa ta sauke ajiyar zuciya gami da goge fuskarta.
Tana ji yana bugun k'ofar, saida ta d'an yi jim sannan ta mik'e ta fita ta bud'e. Ya had'e fuska gami da mik'amata ledojin hannunsa.
"Au, daman kina ji kika shareni?"
Batace uffan ba, ta kar6i ledojin ta ajiyesu zata shige d'aki.
"Ina zakije? Na sallameki ne?"
Ya fad'a yana dubanta. Dole ta dawo ta zauna tana 6ata rai.
Dakinsa ya shige. Saida ya gama abinda zaiyi sannan ya dawo falon har ta kai k'ololuwa wajen 6acin rai.
Zama yayi yana k'aremata kallo, lallai zaiyi maganinta tunda ba zata gaji da tsokanoshi ba.
"D'aukomin filet da kofi."
Ta tashi tayi gaba, cikin sauri take tafiya a fusace wanda ya ba shi damar k'arewa halittar kallo. Murmushi yayi, yasan hirar da yace zai tafi ne ya 6ata ranta. A ganinsa ko hirar ya je, me zai takura zuciyar d'ayansu?
Bayan dawowarta ya umarceta da bude ledojin, ta ciro kaza wacce aka nad'e a foil paper, ta juye. Ta fiddo youghurt din data gani sai lemu.
Tana kammalawa ta juya zata tafi, ji tayi mutum ya fisgota jikinsa.
Ta ware idanu tana dubansa a tsorace, hakan ya k'ara fito da manyan idanunta masu kyau tana dubansa. Shi d'inma ita yake duba, zuciyarsu na bugu da sauri-sauri. Ta soma kiciniyar zillewa, babu dama. Ya d'ago ha6anta, cikin k'aramin muryar ya soma magana.
"Hey, ba dai kishina kikeyi ba ko? Ban hanaki yimin shiga haka ba?"
Ta ji gabanta ya fad'a, saidai kusancinsu yasa batason cewa uffan. Gaba d'aya ma jikinta rawa yake, abu ne da bai ta6a faruwa gareta ba, wai namiji ya rik'eta har haka.
Da ace anan abin ya tsaya da saukinta ne, saidai kuma batayi aune ba ta ji ya soma isar ga sak'onsa a cikin mataunar abincinta(hhhhh.. Inji Tasleem.
Lol).
Bintu ta rasa a inda take, gaba d'aya ta tsorata, jikinta kamar ana kad'awa. To ba ita d'in ba, shi kansa bai tsira ba. Da k'arfi ta fisge jikinta ta ja baya, da gudu kuma tayi d'aki ta rufe gam! Shi kuwa saman kujera ya zauna ya dafe kansa, idanunsa a lumshe. Ya kwashi tsawon mintuna a haka kafin yayi baya ya jingina da kujera.
"Oh Allah, what's about to happen?"(Meke shirin faruwa?)
"Very soft." Ya fad'a a ransa lokacin da hancinsa ya k'ara shak'o k'amshi na jan bakinta.
"Kai, Bintu ce fa!" Wani sashe na zuciyar yayi mishi tuni. Ya bud'e idanunsa da suma suka chanja.
Eh Bintun ce! Ai halaliyarsa ce. Ya bawa kansa wannan amsar cike da jin kwarin gwuiwa da kore kalmar da na sanin da wani sace na zuciyarsa ke k'ok'arin tursasashi wajen yarda.
Saidai ba zai kashe kansa ba, ya shirya dambe da borin kunyar, har ya samu abinda gangar jiki da ruhinsa ke so suna kaiwa kasuwa. Don me zai bari shaid'an ya kusan cin galaba akanshi har ya ji zai iya amincewa da buk'atar Lawisa ya kai mata ziyara?
A'a, shi d'in bai kasance cikin mazinata ba, don haka dole ayi d'ayan biyu. Gudanar da zaman lafiya tsakaninsa da matarsa, ko kuma auro wacce zata iya da buk'atunsa.
Dakyar ya saita kansa ya rufe wannan tashar, zama yayi ya soma cin kazarsa hankalinsa kwance. Saida ya ci mai isarsa sannan ya sha youghurt ya d'ora mata sauran saman firij sanin da yayi na cewar dole zata buk'ata. Daga haka ya dauki ruwa ya kashe fitilu ya fad'a d'akinsa.
* * *
Bintu fa???
[7/22, 2:02 PM] ‪+249 99 842 9948‬: ¶°°BINTU°°¶

©Rufaida Omar
(July...2016)

<<38>>
A daki bintu tana shiga taji wani bakin ciki abinda yayiwa mata a zuciyarta hawaye hawaye hawaye hawaye hawaye hawaye hawaye hawaye hawaye suka dinga zubowa karshe ta shiga ta shiga kitchen ta dauko wuka ta cakawa kanta a ciki take nan ta fadi ta mutu
Ma'aruf Yana daki YA jiyo kara shima YA fito da gudu yayi kitchen yama zuwa yaga bintu ta gadi cikin jini YA dinga kuka YAna jijigata amma inaaa ta muta shima sai yayi tunanin mai zaije YA cewa mommy kawai shima YA dauko wukar YA cakawa kanshiiiii shima ya fadi mutuuuu. Kurunkus angama bintu 😏
😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😜😜😜😜😜😜😜😜😜
[7/22, 10:42 PM] ‪+234 806 038 4145‬: ¶°°BINTU°°¶

©Rufaida Omar
(July...2016)
Chapter 25 · 0% Book details