Sashe 27
Bintu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
<<39>>
Zuwan Aisha gidan ya yi musu dadi. Haka zasu zauna suyita hirar duniya idan ba makaranta. A kokarin Bintu bai wuce koyaushe ta nunawa Aisha lafiya lau suke da mijinta ba. Har takan dauki waya tayi kiransa saidai har wayar ta gama rurinta baya ko kallonta. Saidai a wayance tayita zuba zance don burge Aisha.
Satinsa d'aya da tafiya, amma ko text bai ta6a yi mata ba, da zummar gaisuwa. A yanzu kuwa ta daina samun layinsa, saidai ta ji Aisha tace yayi kiranta ko kuma Mami. Jikinta yayi sanyi, haka kawai ta tsinci kanta da shiga damuwa. Kodai furucinta ya bawa Yaya Ma'aruf haushi? Ashe zai damu da ta nuna damuwa akanshi?
Ta kai dubanta ga Aisha wacce ke kwance rigingine a saman gado tana amsa wayar masoyinta Ashir, sai wani narke murya takeyi da murmushi. Daga inda take ta zubawa wayarta ido kawai amma kunnuwanta suna ga Aisha tana sauraronta.
Kawai sai ta ji abin ya burgeta, inama ita da Yaya Ma'aruf su dawo haka? Sai ta ji nauyi, kada dai ta kamu da son Ma'aruf ne? Ta girgiza kai, kokusa bata fahimtar abinda akeyi a group din nasu ta whatsapp ta tsinci kanta da komawa contact ta lalubo lambar Ma'aruf, har lokacin hotonnan ne akai bai chanja ba. Ta bud'o tana duba, a hankali takejin wani abu na yawo a zuciya da gangar jikinta. Tayi nisa a kallonsa ta ji Aisha ta makomata filo.
"To 'yar is me kikeyi kika wani nutsu?"
Bintu batajin wasa a yau, ta ajiye wayar ta dawo kusa da Aisha ta zauna.
"Tashi ki bani wasu amsoshi don Allah."
Aisha ta mik'e zaune ganin Bintu dagaske take ba wasa.
"Ina sauraronki."
Bintu ta muskuta tana fuskantarta.
"Ya mutum zai gane ya fad'a tarkon so?"
Me Aisha zatayi banda dariya. Ta d'aga hannu sama.
"Allah na godemaka da Ka bani tsawon ran ganin wannan rana. Cabd'i!"
Ta girgiza kai kad'an tana had'e rai cikin son kauda 'yar kunyar da ta ji.
"Malama banason haka, idan bazaki bani amsa ba ki bar yimin dariya."
Ganin Aisha bata da niyyar dainawa ya sanyata daukar wayarta a fusace ta shige d'aki. Kan gado ta fad'a tana murmushi, daman tasan hakan zata faru tunda ta riga ta gama cika baki a baya. Tana jin sadda Aisha ta shigo gami da zama gefenta, ta had'e rai. Aisha ta gimtse dariyarta ta soma magana duk kuwa da cewa Bintun ta juyamata baya.
"Idan ka soma son mutum, zaka tsinci kanka cikin yawan tunaninsa, haka kuma da zarar ka ganshi kun had'a ido zaka ji kamar wasu kibiyoyi ke fitowa daga idanunsa suna shiga naka har suna haddasa maka wani kasala, har ka kasa jure kallon ka sauke idanunka. Komai na mutum zai dawo yana burgeka, ko muryar mutum ka ji sai ka ji wani sanyi na dadi. Babban abinda ke tabbatarwa ka kamu da soyayyar mutum shine KISHI. Nan duniya zakaji baka kaunar abokin takara a zuciyarsa. Ba kuma ka kaunar wani ya ra6eshi da sunan so. Ko yaya kaga ya sakarwa wani fuska ya kula da shi fiye da yanda yake kula da kai sai ka ji tashin hankali sosai, da damuwa da bakin ciki a zuciya. Matukar kina jin wadannan abubuwan da na lissafa, shakka babu (You Are In Love)."
Bintu ta bud'e lumsassun idanunta tana duban fuskar gadonta, ta ji gabanta yana bugu da sauri-sauri. Ta kamu da son Ma'aruf yanzu? Kenan dukkan abinda takeji a ranta akansa soyayya ce?
"Kenan alamomin da nakeji akan Yaya Ma'aruf suna nuni da cewar inasonsa?"
Batasan sadda ta watsowa Aisha tambayar ba. Aisha ta rasa inda zata tsoma ranta don dad'i, don ta jima da gane cewar babu abinda ya ta6a shiga tsakaninsu kawai dai ta barta a yanda ta so ne.
"Idan har kina jin abubuwan da na lissafa akansa, to lallai kin fad'a cikin matsanancin soyayyarsa."
Sai kuma ta ji wata iriyar kunyar Aisha, lura da hakan ne yasa Aisha mik'ewa ta fita da zummar d'ora musu girki.
Ta sauke ajiyar zuciya ta mik'e zaune.
"Inason Yaya Ma'aruf." Shine abinda ta furta cikin siririyar murya.
* * *
"Ina sonki Fatima Bintu." Cewar Ma'aruf kenan a yayinda yake kwance cikin kujera idanuwa a lumshe yana tunanin Bintu wanda ya zame mishi jiki tun zuwansa Lagos. Gaba d'aya kewarta ta dameshi, baisan ya damu da yarinyar ba sai bayan da ya nisanta da ita. Yana fushi da ita akan ta nuna halin ko'in kula da tafiyar da zaiyi, wato dai bata damu da shi ba. A rayuwarsa yana so yaga an damu da shi. Sai ya kai zuciyarsa nesa yake k'in daukar kiranta, lallai shi yana son tilasatawa ransa ya fiddata. Yanaso yabar tunanin wani abu nata da ita kanta. Yana so ya yakiceta a ransa. Wannan yasa ya yanke shawarar yin wata d'ayan da ogansu yace yayi acan batare da ko sau d'aya ya dawo hutun karshen sati Kano ba. Sanin da yayi ma idan yazo ba wani abun zai samu awajenta ba.
Ya numfasa ya mik'e zaune. Kalmar nan ta "So" baiyi zaton zai k'ara furtata ba ballantana ya ji ta a ransa. Sai ga shi zuwa yanzu ya gama tabbatarwa ransa ya fad'a dumu-dumu cikin kogin son matarsa kuma 'yar uwarsa abokiyar fad'ansa Bintu.
Sai kuma yayi murmushi sadda ya tunano rashin jituwarsu tun afarkon zuwanta gidansu har zuwa girmanta.
Rufa'i ya dannawa kira, ya sanar dashi cewar wata d'aya zaiyi don haka ya dauki su Aisha ya maidasu gaban Mami. Daman ya kammala waya da Abba ya shaida mishi. Ya yiwa Bintu gajeran sak'o babu wani abin jan hankali ciki ya shaidamata su had'a kayansu Rufa'i zaizo ya tafi da su gidan Mami.
Ta yi kasak'e tana duban sak'on alokacin suna tare da Aisha tana k'ara koyar da ita yanda zata shawo kansa. Ta sanarwa Aisha kafin su soma shiri. Ranta duk babu dad'i jin zai cinye wata d'aya a garin da basu da wani addini sosai.
Haka suka kammala shiri suka nufi gidan Mami.
Saidai tana ganin Mami ta mance da batunsa ta hau murna. Ganin yanda ta d'an rame sai Mami tayi zaton ko ciki ne. Ta shiga nan nan da ita. Murmushi kawai sukayi ita da Aisha.
[7/24, 9:37 AM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
Zuwan Aisha gidan ya yi musu dadi. Haka zasu zauna suyita hirar duniya idan ba makaranta. A kokarin Bintu bai wuce koyaushe ta nunawa Aisha lafiya lau suke da mijinta ba. Har takan dauki waya tayi kiransa saidai har wayar ta gama rurinta baya ko kallonta. Saidai a wayance tayita zuba zance don burge Aisha.
Satinsa d'aya da tafiya, amma ko text bai ta6a yi mata ba, da zummar gaisuwa. A yanzu kuwa ta daina samun layinsa, saidai ta ji Aisha tace yayi kiranta ko kuma Mami. Jikinta yayi sanyi, haka kawai ta tsinci kanta da shiga damuwa. Kodai furucinta ya bawa Yaya Ma'aruf haushi? Ashe zai damu da ta nuna damuwa akanshi?
Ta kai dubanta ga Aisha wacce ke kwance rigingine a saman gado tana amsa wayar masoyinta Ashir, sai wani narke murya takeyi da murmushi. Daga inda take ta zubawa wayarta ido kawai amma kunnuwanta suna ga Aisha tana sauraronta.
Kawai sai ta ji abin ya burgeta, inama ita da Yaya Ma'aruf su dawo haka? Sai ta ji nauyi, kada dai ta kamu da son Ma'aruf ne? Ta girgiza kai, kokusa bata fahimtar abinda akeyi a group din nasu ta whatsapp ta tsinci kanta da komawa contact ta lalubo lambar Ma'aruf, har lokacin hotonnan ne akai bai chanja ba. Ta bud'o tana duba, a hankali takejin wani abu na yawo a zuciya da gangar jikinta. Tayi nisa a kallonsa ta ji Aisha ta makomata filo.
"To 'yar is me kikeyi kika wani nutsu?"
Bintu batajin wasa a yau, ta ajiye wayar ta dawo kusa da Aisha ta zauna.
"Tashi ki bani wasu amsoshi don Allah."
Aisha ta mik'e zaune ganin Bintu dagaske take ba wasa.
"Ina sauraronki."
Bintu ta muskuta tana fuskantarta.
"Ya mutum zai gane ya fad'a tarkon so?"
Me Aisha zatayi banda dariya. Ta d'aga hannu sama.
"Allah na godemaka da Ka bani tsawon ran ganin wannan rana. Cabd'i!"
Ta girgiza kai kad'an tana had'e rai cikin son kauda 'yar kunyar da ta ji.
"Malama banason haka, idan bazaki bani amsa ba ki bar yimin dariya."
Ganin Aisha bata da niyyar dainawa ya sanyata daukar wayarta a fusace ta shige d'aki. Kan gado ta fad'a tana murmushi, daman tasan hakan zata faru tunda ta riga ta gama cika baki a baya. Tana jin sadda Aisha ta shigo gami da zama gefenta, ta had'e rai. Aisha ta gimtse dariyarta ta soma magana duk kuwa da cewa Bintun ta juyamata baya.
"Idan ka soma son mutum, zaka tsinci kanka cikin yawan tunaninsa, haka kuma da zarar ka ganshi kun had'a ido zaka ji kamar wasu kibiyoyi ke fitowa daga idanunsa suna shiga naka har suna haddasa maka wani kasala, har ka kasa jure kallon ka sauke idanunka. Komai na mutum zai dawo yana burgeka, ko muryar mutum ka ji sai ka ji wani sanyi na dadi. Babban abinda ke tabbatarwa ka kamu da soyayyar mutum shine KISHI. Nan duniya zakaji baka kaunar abokin takara a zuciyarsa. Ba kuma ka kaunar wani ya ra6eshi da sunan so. Ko yaya kaga ya sakarwa wani fuska ya kula da shi fiye da yanda yake kula da kai sai ka ji tashin hankali sosai, da damuwa da bakin ciki a zuciya. Matukar kina jin wadannan abubuwan da na lissafa, shakka babu (You Are In Love)."
Bintu ta bud'e lumsassun idanunta tana duban fuskar gadonta, ta ji gabanta yana bugu da sauri-sauri. Ta kamu da son Ma'aruf yanzu? Kenan dukkan abinda takeji a ranta akansa soyayya ce?
"Kenan alamomin da nakeji akan Yaya Ma'aruf suna nuni da cewar inasonsa?"
Batasan sadda ta watsowa Aisha tambayar ba. Aisha ta rasa inda zata tsoma ranta don dad'i, don ta jima da gane cewar babu abinda ya ta6a shiga tsakaninsu kawai dai ta barta a yanda ta so ne.
"Idan har kina jin abubuwan da na lissafa akansa, to lallai kin fad'a cikin matsanancin soyayyarsa."
Sai kuma ta ji wata iriyar kunyar Aisha, lura da hakan ne yasa Aisha mik'ewa ta fita da zummar d'ora musu girki.
Ta sauke ajiyar zuciya ta mik'e zaune.
"Inason Yaya Ma'aruf." Shine abinda ta furta cikin siririyar murya.
* * *
"Ina sonki Fatima Bintu." Cewar Ma'aruf kenan a yayinda yake kwance cikin kujera idanuwa a lumshe yana tunanin Bintu wanda ya zame mishi jiki tun zuwansa Lagos. Gaba d'aya kewarta ta dameshi, baisan ya damu da yarinyar ba sai bayan da ya nisanta da ita. Yana fushi da ita akan ta nuna halin ko'in kula da tafiyar da zaiyi, wato dai bata damu da shi ba. A rayuwarsa yana so yaga an damu da shi. Sai ya kai zuciyarsa nesa yake k'in daukar kiranta, lallai shi yana son tilasatawa ransa ya fiddata. Yanaso yabar tunanin wani abu nata da ita kanta. Yana so ya yakiceta a ransa. Wannan yasa ya yanke shawarar yin wata d'ayan da ogansu yace yayi acan batare da ko sau d'aya ya dawo hutun karshen sati Kano ba. Sanin da yayi ma idan yazo ba wani abun zai samu awajenta ba.
Ya numfasa ya mik'e zaune. Kalmar nan ta "So" baiyi zaton zai k'ara furtata ba ballantana ya ji ta a ransa. Sai ga shi zuwa yanzu ya gama tabbatarwa ransa ya fad'a dumu-dumu cikin kogin son matarsa kuma 'yar uwarsa abokiyar fad'ansa Bintu.
Sai kuma yayi murmushi sadda ya tunano rashin jituwarsu tun afarkon zuwanta gidansu har zuwa girmanta.
Rufa'i ya dannawa kira, ya sanar dashi cewar wata d'aya zaiyi don haka ya dauki su Aisha ya maidasu gaban Mami. Daman ya kammala waya da Abba ya shaida mishi. Ya yiwa Bintu gajeran sak'o babu wani abin jan hankali ciki ya shaidamata su had'a kayansu Rufa'i zaizo ya tafi da su gidan Mami.
Ta yi kasak'e tana duban sak'on alokacin suna tare da Aisha tana k'ara koyar da ita yanda zata shawo kansa. Ta sanarwa Aisha kafin su soma shiri. Ranta duk babu dad'i jin zai cinye wata d'aya a garin da basu da wani addini sosai.
Haka suka kammala shiri suka nufi gidan Mami.
Saidai tana ganin Mami ta mance da batunsa ta hau murna. Ganin yanda ta d'an rame sai Mami tayi zaton ko ciki ne. Ta shiga nan nan da ita. Murmushi kawai sukayi ita da Aisha.
[7/24, 9:37 AM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)