← Book details Bani Da Gata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 29

Sashe 4

Bani Da Gata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Adamsy lokacin da yaje hospital Ma'azzara tayi wanka ta canza kaya tayi tsaf da ita bayan tayi sallah ra saka kakarta gaba tana mata hira, dan kasa kunna panpon tayi sai da ta kirawo.likita ya kunna mata.
Adamsy ya bawa Ma'azzara kayan breakfast ta ko amsa ta shige karkashin gado taci iya cinta, dan ya ce gaishana bazata ci komai ba bai wani saki fuskar saba ya dai ce mata ya mai jiki ya zauna kusan gaisha yana mata Sannu amma ina bata san inda take ba tana dai numfashin.
Ma'azzara kuwa bayan ta ci abun da taci ta fito taje ta wanko hannunta ta tsare Adamsy kur da idanu baima san tana yiba a shagwab'e ta ce" Uncle ni ce yar lelanka har goyani kake yi kana mun waka mai dadi da hira mai dadi , har wannan abun da naga kama Anty jiya nima kana mun wai bakajin tsamin bakin mutum wlh ni sai naji kamar zanyi amai...."Manyan idanunsa ya zaro ya mike ransa a bace ya ce"Ke wai uban waye...." maganar sa ce ta tsaya saboda kofar da aka turo Dr tane Adamsy ya juyo ya kallesa Dr ya ce"Yallabai an gama shirya tafiyar" Adamsy ya ce"Ok muje ko" wasu nurse suka shigo da gadon marasa lafiya suka ajiye suka dauki gaishana sai lokacin ta bude idanu tana tari ta kalli Adamsy, shima da sauri ya iso yana mata sannu.
Hannunta ta bashi da sauri Adamsy ya kama ya rike.
Gaishina ta jimke hannunsa, bakinta ta bude tana magana ba'a ji Ma'azzara ta matso ta ce"Gaishnata an sallame mu gida zamu kinji sauki gobe sai ki fadamun maganin zafi na tafi tallah...." Adamsy ya ce"Ke bamuson shirme" gaishina ta ce" Dan Allah ga Amana zan baka ka rik'eta amana bata da kowa bata da gata sai ni sai Allah ina yarinyar jiya ku taru ku rike Amana...." Cak bakinta ya tsaya tana shakuwa tana fadin wani abu amma ba'a jinta, Adamsy cikin tsawa ya cema Dr "Dallah malam ku duba lafiyarta kafin mu wuce Agadez". Adamsy bakinsa ya tsaya cak ganin gaishina bata motsi idanunta a bude tar.
Wata irin zufa yaji ta keto masa.
Nurse suka maidata kan gadon Dr ya fara dubata Ma'azzara ta matso kusan Adamsy ta kamo hannunsa ta ce" Uncle kaga yadda take ko jiyama haka tayi, dan Allah a mata magani itace gatana bani da gata sai ita." Adamsy ya kasa magana jikinsa sai rawa yake gabansa na faduwa.
Muryar Dr ya tsinto yana cewa" Allahu akbar kabiran kullun nafsin za'ikatul maut" Adamsy ya ce"Dr pls karaka cemun ta mutu, dan Allah ni ina zankai Amana, taya daga ganina baki sani ba ki bani amanar mutum, ya zanyi Innalillahi wa'inna ilaihirrajiun" Ma'azzara ta saki hannuna Adamsy tana ja baya ta kece da kuka ta ce"Karya kuke bata mutuba wlh idan kuka kashe mun gaishana wlh sai kunyi nadama a rayuwarku" ta fada tana kuka ta nufi gun gawar Adamsy ya karaso gurin gawar Ma'azzara ta taba jikin gaishana ba inda yake motsi Adamsy ya beka hannunsa ya shafema gaishana idanu.
Ma'azzara ganin da gaske gaishana ta mutu ta kurma wani gigitaccan ihu tayi luuuuuu zata fadi Adamsy ya tareta ta fado jikinsa sumammiya, Idanu Adamsy ya zaro ya ce"Ya Allah wannan lamari ya kenan"...................✍🏻
*Real Ladingo ce*😅

*Karku manta ya koma na kudi kan fara shi me sauƙi sbd masoya nera 200 kacal +22792589446/+22796515805*

Ummu Fareesa💋

*💖BANI DA GATA💖*

*MALLAKAR*
👇🏻

Yar mutan Niger🤙🏻

*Bismillahir Rahamanir Rahim*

*Chapter 3*

....Adamsy hankalinsa a tashe ya nufo kofar fita, yana rungume da Ma'azzara ganin bata motsi, duk ma ya rikice saboda bai saba shiga irin wannan tashin hankalin ba.
Har ya kai kofar zai fita likitan ya ce"yallabai maidota na temakon gagawa" Adamsy bai juyoba ya tsaya ya ce" Dr muje wani room din saboda inaso a bata kulawa mai kyau ta samu hutu kayi mata alluran bacci wqnsa akalla zata kai lokacin da za'a binne kakarta bata farfado ba, idan san samune ta wuni Rana bacci bayan ba nutsu zan dawo ga amanar Allah". Ya karasa maganar yana ficewa yana mai cike da tarin damuwa fuskarsa ta nuna hakan karara dan baisa ya zaiyi da amanar yarinyar ba.
Adamsy yana fita likitan yabi bayansa tare da nurse guda.
Wani room da ba kowa likitan ya nunama Adamsy ya shiga ya kwantar da ita saman karamin gadon ya gyara mata kwanciyarta ya juya ya fice.
Likinta ya dukufa ceton ran Ma'azzara cikin 30 minutes Ma'azzara ta dawo haiyacinta ta kurma wani uban ihu tana kiran uncle da gaishana, tana fizge-fizge daket likitan ya riketa dama nurse ta hada alluran ta ba Dr ya tsura mata ko minti biyar ba taiba bacci ya dauketa tana kiran uncle da gaishana.

Adamsy yana fita ya nufi motarsa inda ya faka ya shiga ya kira Ummee yana fad'a mata, hankali a tashe ta ce zata turo masa mutum biyu su raho da gawar zata tura a kira Salamatu kanwar gaishina ta fad'ama sauran dangisu su zo a hadu a zauna ayi zaman makokin ana gidan su ummeen tunda Bature da Hassana nason temakonsu itama tana so.
Adamsy ya hana ta fad'ama Husaina dan ka hankalinta ya tashi baya kusa bare ya lallabata.
Haka kuwa akayi Ummee ta turo masa agali da gumar akayi komai aka gama aka basu gawar suka nufi gida, lokacin Ummee har tasa an kirawo yan tsarekun yan uwan su Ma'azzara wanda basu damu da rayuwarsu ba amma harda kukan munafurci kafin ma a iso da gawar, Hussaina kuwa tana can tana barcinta cikin nutsuwa dan ummee bata so ta tajima har sai na binne gaishina.

Ba'adau wani dogon lokaci ba adamcy suka k'araso da gawar gaishina aka shirya gawar aka tafi da ita gidanta na gaskiya.
Usaina ba ita ta tashi ba sai bayan da aka kai gashina yenuwan nasu ma sun soma tafiya , dama su mutuwar bawani damunsu tayi ba dan koh muazzara basu tambaya ba sunsha koke kokensu na karya da nuna tsantsar damuwar .

Daki Adamcy ya wuce dan dubo usaina ya tadda ba kowa a dakin karan ruwan dake fito a setin toilet ya tabbatar mai da usaina na ciki,Zama yayi bakin gado yana jiran fitowarta yashiga kololuwar tunanin Muazzara shi Yanzu ya zeyi da amarta da akabashi Yanzu matarnan tamishi adalci data hadashi da amarna mutum tayaya ze rike amarta bayan ko kadan bason yarinyar yake ba jininshi kwata kwata be hadu da yarinyar ba abunda yakuma samai tsanar yarinyar haukar datake mai tana kiranshi da uncle shi sam besan yazeyi ba ,
Yayi nisa cikin tunaninshi Hussaina ta fito daga wankan datake zaune saman gado ta ganshi yayi jugum kallo daya za'amai asan hankalinshi baya kusa dashi ita sam batasan ma da shigowarshi ba
Murmushi tayi ta k'arasa kusa dashi ta dafo kafadan tace" Mon trèsor meya faru yaushe ka shigo ne, k'okarin seta kanshi yayi da boye damuwarsa ya janyota jikinshi ta zauna kan cinyarshi yace "Ma babe shigowa kenan ,tashi muje na shirya ki Chak yadauke ya dire gaban mirrow yashiga shafa mata mai tare da shiryata cikin salon so da kaunar junaa...

Ta cikin mirror din ta kalleshi tace" Mon trèsor ya jikin Gashinan yaushe za'a mata aikin ne matar nan ba karamin tausayinta nakeji ba kaga irin halin datake ciki da jiya bamu taimaka ba bansan halin da zata shigaba zuwa yau kilama ta iya rasa ranta,
Hankalinshi ne yakuma tashi yasan Husaina batasan da mutuwar gashina ba taya ze Sanar mata da gashina ta mutu yasan halin Husaina da rikicewa akan abunda bekai yakawo ba bare kuma wannan da suka shiga ranta daga haduwar farko.
Maganar Husaina takoma da Adamcy daga duniyar Nazarin daya shiga ,

*💖BANI DA GATA💖*

*MALLAKAR*
👇🏻
```Real Ladingo Sweet Baby```

*Bismillahir Rahamanir Rahim*

*Chapter 4*

.... Suna shiga gun Ummee Hussaina ta zare hannunta ana Adamcy, ta nufi gun Ummee ta zauna kusanta cike da jin kunya tace "Ummeena ina kwana ya hakurin mu Nini ta tafi ta barmu Allah ya jiqanta da rahamarsa, Allah ya kai haske da ni'ima kabarinta.." janyota jikinta Ummee tayi tana shafa kanta tace "Amin ya Allah Husainata, ya kuma muka ji da ƙarin hakurin wannan baiwar Allah itama?" Da sauri ta dago kai tana kallon Ummee kafin ta juya a hankali ta kalli Adamcy dake tsaye, a bakin ƙofa hannayen sa zube a cikin aljihunsa ya zubo musu idanunsa zuciyarsa cike da fargaban damuwar da zata shiga idan aka fada mata mutuwar Gaishina.

Tana kallon Ummee fuskarta cike da alamar tambaya tace "Wace ce kuma ta rasu Ummee?" Juyawa Adamcy yayi ya dauke kansa gefe, domin baya son ya kalleta yaga irin damuwar da zata shiga saboda ba zai iya jurewa ba, kara kamota jikinta Ummee tayi a tausashe tace "Wannan baiwar Allahn mara lafiya itama Allah ya karbi abarsa..” a razane ta juya tana kallon Adamcy daya dauke kansa da sauri yayi kamar bai ji abinda Ummeen ta fada mata ba, tana girgiza kanta ta fada jikin Ummee ta kankameta hade da fashewa da wani irin kuka mai karfi da taba zuciyar duk wani mai sauraro, yayinda a gefe guda kuma ga tsantsar tausayin Ma'azzara da damuwar irin halin da zata iya shiga idan taji labarin mutuwar kakarta mafi soyuwa agareta ya risketa, saboda ta lura akwai tsantsar kauna da soyayya mai ƙarfin gaske a tsakaninsu ita da kakar tata.
Chapter 4 · 0% Book details