Sashe 3
Bani Da Gata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba daɗewa suka dawo dakin tare da likita, ya dubata ya maida mata drip d'in yana mata faɗan ta natsu karta ƙara cirewa ita ko saurararsa ma bata yi saboda hankalinta na can kan Adamsy ta ƙura masa idanu kir sai kallonsa take kamar zata cinyesa, likata yayi mata allura ya fice.
Shi ko Adamsy bai ma san tanayi ba, dan yana can rungume da Husaina a jikinsa yana lallashinta yana faɗa ma daɗaɗan kalamai masu daɗi da sanyaya zuciya, yana ci gaba da lallashinta ya kira Ummeensa a waya ya miƙa mata, tana kuka ta karɓa ta manna akunnenta ta shiga zayyanewa Ummee duk abinda ke faruwa, gashi tana so a taimakawa yarinyar kuma taji tana kuka tana kiran Agaishana bata da lafiya, amma Adamsy yana so ya ƙiya, tana kuka ta ƙarasa faɗa mata komai, daga can Ummeen tace taba Adamsy wayar, yana kallonta ya karɓa ya manna a kunnensa, ya ɗan saurara yana jin abinda Ummeen take faɗa masa, ɗan kallon Husaina yayi kafin yace "Dama ai tunda tanaso Insha Allahu zanyi k'ok'ari iya ƙarfina Ummee zan taimaka mata." Tana jin haka ta janye jikinta da murna ta koma gurin Ma'azzara ta zauna a bakin gadon ta riƙe hannunta tana kallonta cike da tausayinta tace "A wane gari kike?" Tana kallonta a hankali cikin sanyin muryarta tace "Nan... Cikin Audaraas nake..." Nan ta yi mata kwantaccen komai ta faɗa mata har inda take, gyaɗa kai Husaina tayi tana ƙara jin tausayinta tace "Insha Allahu zamu je gidanku a taikamawa Agaishanki kinji.?" Tana murmushi ta gyaɗa mata kai cike da farin ciki ta lumshe idonta tana jin daɗi a ranta.
Sun jima a haka tana riƙe da hannunta, har drip d'in ya kare Adamsy yaje ya kirawo likita yazo ya cire mata ya kara dubata sosai, yace bata da wata matsala, ya basu sallama, Husaina ta tallabota ta taimaka mata ta tashi tana riƙe da ita ta sauko daga gadon suka fice daga d'akin Adamsy na biye dasu a baya yana taɓe bakinsa yana ji aransa, dan dai babu yanda zaiyi da Husaina ne dan baya son ɓacin ranta, amma da babu abinda zai kaisa taimakawa wannan abar mai wari har ya sake ɗaukarta a motarsa ya kaita gidansu.
Direct inda yayi parking motarsa suka nufa ya buɗewa Husaina ta shigar da ita baya ta zauna ta rufe mata ƙofa sannan ta shiga gaba kusa da Adamsy ta zauna ta ɗauke kai tana kallon titi ya tada motar suka fara tafiya, ganin tayi shiru tai banza dashi tama ɗauke kanta daga garesa yasa yayi murmushi ya kamo hannunta ya riƙe a nasa yana murzawa a hankali cikin taushin murya ya fara lallaɓarta "Haba Mon Bebeta kiyi hak'uri mana, insha Allahu nayi miki alƙawarin tunda har kina son yarinyar zanyi k'ok'arin taimaka musu, ki kwantar min da hankalinki pls, kin san a kanki zan iya yin komai? So pls ki saki fuskarki bana son ganinta a haka..." Ya faɗa yana shafa kumatunta, tana jin daɗi ta juyo tana kallonsa tana ƙara damƙe hannunsa sosai a nata ta sumbaci kumatunsa tana murmushi tace "Nagode Mon trèsor, Allah ya barmu tare." Yana ci gaba da tuki da hannu ɗaya, ya ɗago hannunta ya kai bakinsa ya sumbata yana ƙara jin sonta sosai a ransa da zuciyarsa.
Haka Ma'azzara tai ta kwatanta musu hanya har suka kai gidansu.
Gidane dan madedeci ginin k'asa da ko soron kofa babu. Parking Adamsy yayi ya kalli Husaina tana rike da hannunsa guda, murmushi dauke kan fuskarta Adamsy ya ce"Oya sai ki fita ku shiga" ya fadi yana tab'e baki da mamakin ta yadda mutum yake rayuwa anan.
Husaina ta saki hannunsa ta bude motar ta fito, ta budewa Ma'azzara ta ce"Fito meye sunanki?" Ma'azzara cikin sanyi maganarta ta ce"Ma'azzara" Husaina ta ce"Wow nice name" Baki Adamsy ya tab'e.
Ma'azzara tana fitowa Husaina ta kama hannunta suka nufi cikin dan k'aramin gidan, ba tare da kyankyamin komi ba.
Adamsy ya rakasu da idanunsa masu ruwan zaiba ya dauki wayarsa yana latsawa yayi dailing din wata number bugo d'aya aka dauka.
Adamsy ya ce"Salut cava?" Faruq yayi dariya ya ce CV très bien wai kai dan wulakanci shine ka bar Naimey kun tafi Agadez ko ka kirani kace hajiya Nini ta rasu ai da munzo tare kowa a motarsa zaizo." Adamsy ya saki siririn murmushi saida dimples dinsa suka loba fararan
hakoransa suka baiyana, cikin daddadar muryasa ya ce" Afuwan my Umaruru wlh a jirgi muka zo duk dan musa mu sutura amma ina Ummee ta ce an binneta tun yau da safe, naga kiranka yau Husaina rigima ta keji". Nan dai ya bashi labarin duk abinda da ya faru Faruq ya masa fadan kar yayi hakan dan wulakanci ba halinsa bane, ya temaka mata Allah zai bashi lada.
Suna shiga Ma'azzara ta nufo d'akin sa gudu tana shiga dakin ta iske Gaishina ba yadda take Ma'azzara ta fashe da kuka ta fada samanta.
Husaina ta shigo dakin hankalinta a tashe.
Ta ce"Ma'azzara kibar kuka tashi kamata muje hospital" Husaina ba tare da kyankyami ba ta kama gaishana tana fitar da numfashi daket Ma'azzara ta kamata tana kuka Husaina ta ce"Ma'azzara saketa zan rik'eta dauki kayan da zaki canza gobe da safe ki saka hijabi ki cire mayafin." Ma'azzara jikinta na rawa ta nufi gurin gari yayi zafinta ta ciro riga da zani na bakin yadisu na bugaje mai.kyau duk yasha ruwa a wanke fes sai kamshi yake ta daukarma gaishana ma ta cire mayafin, ta saka hijabi ta linke mayafin ta nasa cikin ledar kayansu ta iso gurin Husaina.
Husaina ta ce"yauwa to kamata mu tafi." Ma'azzara ta kama sharan kafadar gaishana Husaina share suka fito.
Adamsy yana hangosu ya kashe wayar da suke da Faruk Babban aminsa ya fito ya bude musu motar suka shigar Gaishina, wacce take a halin jigatuwa dan Adamsy yayi mugun tsorata da ganin tsohuwar sai sannu ya ke mata.
Ma'azzara ta shiga kusanta ta zauna Adamsy ya rufo mota ya kama hannun Husaina ya shigar da ita gaba ya rufo ya zagaya ya shiga ya tashi motar ya dauki hanyar hospital din da suka fito.
Husaina ta kwantar da kanta kirjin Adamsy yana driving da hannu daya dayan yana shafa kanta da fuskarta, Husaina ta ce" Adamsyna" Ya shafi fuskarta ya ce"Na'am Husaianta yi hakuri zan temaka musu hakika suna neman temako." Shiru Husaina tayi ta lafe jikinsa.
Ma'azzara ma tana rungume da Gaishina sai wani irin nishi take da huci.
Suna zuwa hospital likitoci suka amshi gaishana aka fara bata teamakon gagawa domin ceto ranta dan tana mawuyacin hali.
Husaina ta rungume Ma'azzara tana kuka tana lallashinta. Adamsy sai hararan Ma'azzara yake dan gani yake ta amshe masa matarsa.
Kusan 2 hours sukayi kafin likintan ya fito.
Lokacin Ma'azzara tayi bacci jikin Husaina.
Adamsy ya tari likitan ya ce"Dr yaya mai jikin?" Dr ya ce Alhmdllh da sauki amma gaskiya ciwon ya cita sosai dan kodarta d'ayar har ta fara zagwanyewa, dan wlh dole gobe sai an mata operation amma dole Agadez zaku kaita ayi k'ok'ari goben ." Adamsy ya ce"Allah ya kaimu insha Allah babu damuwa a bata duk kulawar da ya dace goben da zaran anyi sallah Asubah zan zo na tafi da ita." Dr ya amsa da "babu damuwa ku shiga ku ganta"Adamsy bai yi magana ba ya daga kansa ya dawo gurin Husaina ya ce"Bebeta ya za'ayi tayi bacci tashi muje gida na dan huta". Husaina ta tashi Ma'azzara firgigita ta farka.
Husiana ta kama hannunta suka nufi room din da gaishina take Adamsy na biye dasu.
Suna shiga suka ga an mata Karin ruwa harda abun Karin numfashi a jikinta.
Ma'azzara ta isa kusanta ta dora kanta saman kirjinta ta rufe idanunta.
Tausayinta ya cika Husaina tazo ta kama Ma'azzara ta temaka mata ta hau saman gadon, ta ce"kanwata ki kwanta ki huta zamu je gida da safe zamu zo insha Allah kinji". Ma'azzara ta gyada kanta bata bude idanuba.
Husaina ta gyara mata kwanciyarta ta juyo gurin Adamsy ta kama hannunsa ta ce"Yayana Muje na maka tausa kayi bacci". Murmushi Adamsy ya saki ya kara damke hannunta suka fito ta janyo masu kofar.
Tun a cikin motar Husaina take dannawa Adamsy jikinsa tana masa sannu murmushi kawai yake sakar mata har suka iso kofar gidan.
Rumfa ce katuwa a kofar gidan saboda yan amsar gaisuwa.
Gidan dan madedeci ne ya hadu ta ko ina tamkar ba a kauye ba, Lokacin da suka shiga duk jama'ar gidan sunyi bacci sai Ummee kadai a parlor tana jiransu.
Suna shigowa wata kyakyawar dattijuwa yar kimanin 45 year farar buzuwa mai kyan gaske wacce kallo daya zaka mata kasan akwai masu gidan rana.
Ummee ta tarbesu ta rungume Husaina Adamsy ya rungume Ummee ya shagwab'e ya ce"Ummee ni baki tawa sai ta yarki" Ummee ta kai masa dukan wasa ta ce"To yanzu abar gaishe-gaishe sai da safe kuje kuyi wanka ku huta na shirya maku komai". Ta fad'a tana sakinsu ta shige bedroom.
Adamsy ganin Ummee ta shige ya dauki Husaina cak suka nufi part din da suke sauka idan sunzo.
Suna zuwa wanka sukayi saka saka kayan bacci suka kwanta manne da junsu Husaina ta dan ma Adamsy tausa har tayi bacci kafin itama baccin ya dauketa tana manne jikin mijinta Asuba ta gari.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Washe gari bayan sunyi sallah Asubah Adamsy ya lallaba Husaina ta koma bacci, dan bayaso tasha wuya ta ce zata bishi Agadez dan so yake ya isa da wuri da zaran an gama operation ya dawo Audarass bayan ya nemi mai kula da tsohuwar.
Adamsy ya fad'ama Ummee komi ta bashi goyan baya barin ma da taji gaishana ce dan tasan tsohuwar sosai, duk zauwar da zatayi kauyan sukan gaisa kayan breakfast Ummee ta hada masa ya taho dasu.
Shi ko Adamsy bai ma san tanayi ba, dan yana can rungume da Husaina a jikinsa yana lallashinta yana faɗa ma daɗaɗan kalamai masu daɗi da sanyaya zuciya, yana ci gaba da lallashinta ya kira Ummeensa a waya ya miƙa mata, tana kuka ta karɓa ta manna akunnenta ta shiga zayyanewa Ummee duk abinda ke faruwa, gashi tana so a taimakawa yarinyar kuma taji tana kuka tana kiran Agaishana bata da lafiya, amma Adamsy yana so ya ƙiya, tana kuka ta ƙarasa faɗa mata komai, daga can Ummeen tace taba Adamsy wayar, yana kallonta ya karɓa ya manna a kunnensa, ya ɗan saurara yana jin abinda Ummeen take faɗa masa, ɗan kallon Husaina yayi kafin yace "Dama ai tunda tanaso Insha Allahu zanyi k'ok'ari iya ƙarfina Ummee zan taimaka mata." Tana jin haka ta janye jikinta da murna ta koma gurin Ma'azzara ta zauna a bakin gadon ta riƙe hannunta tana kallonta cike da tausayinta tace "A wane gari kike?" Tana kallonta a hankali cikin sanyin muryarta tace "Nan... Cikin Audaraas nake..." Nan ta yi mata kwantaccen komai ta faɗa mata har inda take, gyaɗa kai Husaina tayi tana ƙara jin tausayinta tace "Insha Allahu zamu je gidanku a taikamawa Agaishanki kinji.?" Tana murmushi ta gyaɗa mata kai cike da farin ciki ta lumshe idonta tana jin daɗi a ranta.
Sun jima a haka tana riƙe da hannunta, har drip d'in ya kare Adamsy yaje ya kirawo likita yazo ya cire mata ya kara dubata sosai, yace bata da wata matsala, ya basu sallama, Husaina ta tallabota ta taimaka mata ta tashi tana riƙe da ita ta sauko daga gadon suka fice daga d'akin Adamsy na biye dasu a baya yana taɓe bakinsa yana ji aransa, dan dai babu yanda zaiyi da Husaina ne dan baya son ɓacin ranta, amma da babu abinda zai kaisa taimakawa wannan abar mai wari har ya sake ɗaukarta a motarsa ya kaita gidansu.
Direct inda yayi parking motarsa suka nufa ya buɗewa Husaina ta shigar da ita baya ta zauna ta rufe mata ƙofa sannan ta shiga gaba kusa da Adamsy ta zauna ta ɗauke kai tana kallon titi ya tada motar suka fara tafiya, ganin tayi shiru tai banza dashi tama ɗauke kanta daga garesa yasa yayi murmushi ya kamo hannunta ya riƙe a nasa yana murzawa a hankali cikin taushin murya ya fara lallaɓarta "Haba Mon Bebeta kiyi hak'uri mana, insha Allahu nayi miki alƙawarin tunda har kina son yarinyar zanyi k'ok'arin taimaka musu, ki kwantar min da hankalinki pls, kin san a kanki zan iya yin komai? So pls ki saki fuskarki bana son ganinta a haka..." Ya faɗa yana shafa kumatunta, tana jin daɗi ta juyo tana kallonsa tana ƙara damƙe hannunsa sosai a nata ta sumbaci kumatunsa tana murmushi tace "Nagode Mon trèsor, Allah ya barmu tare." Yana ci gaba da tuki da hannu ɗaya, ya ɗago hannunta ya kai bakinsa ya sumbata yana ƙara jin sonta sosai a ransa da zuciyarsa.
Haka Ma'azzara tai ta kwatanta musu hanya har suka kai gidansu.
Gidane dan madedeci ginin k'asa da ko soron kofa babu. Parking Adamsy yayi ya kalli Husaina tana rike da hannunsa guda, murmushi dauke kan fuskarta Adamsy ya ce"Oya sai ki fita ku shiga" ya fadi yana tab'e baki da mamakin ta yadda mutum yake rayuwa anan.
Husaina ta saki hannunsa ta bude motar ta fito, ta budewa Ma'azzara ta ce"Fito meye sunanki?" Ma'azzara cikin sanyi maganarta ta ce"Ma'azzara" Husaina ta ce"Wow nice name" Baki Adamsy ya tab'e.
Ma'azzara tana fitowa Husaina ta kama hannunta suka nufi cikin dan k'aramin gidan, ba tare da kyankyamin komi ba.
Adamsy ya rakasu da idanunsa masu ruwan zaiba ya dauki wayarsa yana latsawa yayi dailing din wata number bugo d'aya aka dauka.
Adamsy ya ce"Salut cava?" Faruq yayi dariya ya ce CV très bien wai kai dan wulakanci shine ka bar Naimey kun tafi Agadez ko ka kirani kace hajiya Nini ta rasu ai da munzo tare kowa a motarsa zaizo." Adamsy ya saki siririn murmushi saida dimples dinsa suka loba fararan
hakoransa suka baiyana, cikin daddadar muryasa ya ce" Afuwan my Umaruru wlh a jirgi muka zo duk dan musa mu sutura amma ina Ummee ta ce an binneta tun yau da safe, naga kiranka yau Husaina rigima ta keji". Nan dai ya bashi labarin duk abinda da ya faru Faruq ya masa fadan kar yayi hakan dan wulakanci ba halinsa bane, ya temaka mata Allah zai bashi lada.
Suna shiga Ma'azzara ta nufo d'akin sa gudu tana shiga dakin ta iske Gaishina ba yadda take Ma'azzara ta fashe da kuka ta fada samanta.
Husaina ta shigo dakin hankalinta a tashe.
Ta ce"Ma'azzara kibar kuka tashi kamata muje hospital" Husaina ba tare da kyankyami ba ta kama gaishana tana fitar da numfashi daket Ma'azzara ta kamata tana kuka Husaina ta ce"Ma'azzara saketa zan rik'eta dauki kayan da zaki canza gobe da safe ki saka hijabi ki cire mayafin." Ma'azzara jikinta na rawa ta nufi gurin gari yayi zafinta ta ciro riga da zani na bakin yadisu na bugaje mai.kyau duk yasha ruwa a wanke fes sai kamshi yake ta daukarma gaishana ma ta cire mayafin, ta saka hijabi ta linke mayafin ta nasa cikin ledar kayansu ta iso gurin Husaina.
Husaina ta ce"yauwa to kamata mu tafi." Ma'azzara ta kama sharan kafadar gaishana Husaina share suka fito.
Adamsy yana hangosu ya kashe wayar da suke da Faruk Babban aminsa ya fito ya bude musu motar suka shigar Gaishina, wacce take a halin jigatuwa dan Adamsy yayi mugun tsorata da ganin tsohuwar sai sannu ya ke mata.
Ma'azzara ta shiga kusanta ta zauna Adamsy ya rufo mota ya kama hannun Husaina ya shigar da ita gaba ya rufo ya zagaya ya shiga ya tashi motar ya dauki hanyar hospital din da suka fito.
Husaina ta kwantar da kanta kirjin Adamsy yana driving da hannu daya dayan yana shafa kanta da fuskarta, Husaina ta ce" Adamsyna" Ya shafi fuskarta ya ce"Na'am Husaianta yi hakuri zan temaka musu hakika suna neman temako." Shiru Husaina tayi ta lafe jikinsa.
Ma'azzara ma tana rungume da Gaishina sai wani irin nishi take da huci.
Suna zuwa hospital likitoci suka amshi gaishana aka fara bata teamakon gagawa domin ceto ranta dan tana mawuyacin hali.
Husaina ta rungume Ma'azzara tana kuka tana lallashinta. Adamsy sai hararan Ma'azzara yake dan gani yake ta amshe masa matarsa.
Kusan 2 hours sukayi kafin likintan ya fito.
Lokacin Ma'azzara tayi bacci jikin Husaina.
Adamsy ya tari likitan ya ce"Dr yaya mai jikin?" Dr ya ce Alhmdllh da sauki amma gaskiya ciwon ya cita sosai dan kodarta d'ayar har ta fara zagwanyewa, dan wlh dole gobe sai an mata operation amma dole Agadez zaku kaita ayi k'ok'ari goben ." Adamsy ya ce"Allah ya kaimu insha Allah babu damuwa a bata duk kulawar da ya dace goben da zaran anyi sallah Asubah zan zo na tafi da ita." Dr ya amsa da "babu damuwa ku shiga ku ganta"Adamsy bai yi magana ba ya daga kansa ya dawo gurin Husaina ya ce"Bebeta ya za'ayi tayi bacci tashi muje gida na dan huta". Husaina ta tashi Ma'azzara firgigita ta farka.
Husiana ta kama hannunta suka nufi room din da gaishina take Adamsy na biye dasu.
Suna shiga suka ga an mata Karin ruwa harda abun Karin numfashi a jikinta.
Ma'azzara ta isa kusanta ta dora kanta saman kirjinta ta rufe idanunta.
Tausayinta ya cika Husaina tazo ta kama Ma'azzara ta temaka mata ta hau saman gadon, ta ce"kanwata ki kwanta ki huta zamu je gida da safe zamu zo insha Allah kinji". Ma'azzara ta gyada kanta bata bude idanuba.
Husaina ta gyara mata kwanciyarta ta juyo gurin Adamsy ta kama hannunsa ta ce"Yayana Muje na maka tausa kayi bacci". Murmushi Adamsy ya saki ya kara damke hannunta suka fito ta janyo masu kofar.
Tun a cikin motar Husaina take dannawa Adamsy jikinsa tana masa sannu murmushi kawai yake sakar mata har suka iso kofar gidan.
Rumfa ce katuwa a kofar gidan saboda yan amsar gaisuwa.
Gidan dan madedeci ne ya hadu ta ko ina tamkar ba a kauye ba, Lokacin da suka shiga duk jama'ar gidan sunyi bacci sai Ummee kadai a parlor tana jiransu.
Suna shigowa wata kyakyawar dattijuwa yar kimanin 45 year farar buzuwa mai kyan gaske wacce kallo daya zaka mata kasan akwai masu gidan rana.
Ummee ta tarbesu ta rungume Husaina Adamsy ya rungume Ummee ya shagwab'e ya ce"Ummee ni baki tawa sai ta yarki" Ummee ta kai masa dukan wasa ta ce"To yanzu abar gaishe-gaishe sai da safe kuje kuyi wanka ku huta na shirya maku komai". Ta fad'a tana sakinsu ta shige bedroom.
Adamsy ganin Ummee ta shige ya dauki Husaina cak suka nufi part din da suke sauka idan sunzo.
Suna zuwa wanka sukayi saka saka kayan bacci suka kwanta manne da junsu Husaina ta dan ma Adamsy tausa har tayi bacci kafin itama baccin ya dauketa tana manne jikin mijinta Asuba ta gari.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Washe gari bayan sunyi sallah Asubah Adamsy ya lallaba Husaina ta koma bacci, dan bayaso tasha wuya ta ce zata bishi Agadez dan so yake ya isa da wuri da zaran an gama operation ya dawo Audarass bayan ya nemi mai kula da tsohuwar.
Adamsy ya fad'ama Ummee komi ta bashi goyan baya barin ma da taji gaishana ce dan tasan tsohuwar sosai, duk zauwar da zatayi kauyan sukan gaisa kayan breakfast Ummee ta hada masa ya taho dasu.