← Book details Bani Da Gata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 29

Sashe 28

Bani Da Gata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ummee dake tsaye ne tasaki murmushi, sosai itakam take mamakin ƙarfin hali, da shegen yawan tusosi irin na Salamatu, ba abunma dake bata dariya kaman yanda Kaltume mai adashe ke ihu tana neman agaji,  Malam Musa kuwa babu yanda baiyi ba akan Salamatu ta sauka akan Kaltume, amma sam taƙi saima ƙara zauneta take, Halliru kuwa komawa gefe yayi yanata buga dariyarsa, don ya tabbata Kaltume yau saitayi jinyar kusan sati guda, donshi kansa da sukayi faɗa da Salamatu, duk da baiji ɗoyin bujenta ba, amma saida yayi kwana uku cur yana jinyan jikinsa da kuma numfashinsa wanda ya sanja, yazama idan ma ya shaƙi numfashi warin tusosin Salamatu kawai yake shaƙa, saboda yanda tayita buga masa su, hakanan sanadin faɗansa da ita ya daina jin wari da kuma ƙamshi.
Ganin dagaske Salamatu na shirin  nakasa Kaltume yasanya Ummee ƙarasowa da sauri, cikin tausasa murya tace "Hajiya Salamatu ayi haƙuri hakanan, nasan zuwa yanzu ta tuba."
Jin baƙuwar murya yasa Salamatu ɗagowa don ganin wake magana, ganin Hajiya Ummee ya sanyata washe baki, lokaci guda ta miƙe tsaye, cikin farincikin ganin Ummin tace.
"Ranki ya daɗe sannunki da zuwa, ae inanan ina koyawa wannan Kaltumen hankali, bansan da zuwanki ba." Taƙare maganar tana me laluban zaninta ta ɗaura.
Kaltume kuwa jin Salamatu ta ɗagata hakan yasa awahalce ta yunƙura zata tashi, wani irin amaine yazo mata take tashiga kwarara aman awajen, tayi matuƙar galabaita.
Tsalle Salamatu tayi ta dire, cikin sabon fitinan daya ciyota tace.
"Kutumar Ubancan! Kaltume ni kike zubawa ƙazanta acikin gida? kan babban bala'i, to wallahi saikin kwashesa tsaf, kokuwa kisa harshenki ki lashesa, idan bahaka ba kuwa mu ɗaura daga inda muka tsaya, dan Uban mutum ae yanzun kam zai san cewa ba tsoronsa nakeji ba!."
Tuni cikin Kaltume ya ɗuri ruwa, cikin matsanancin tsoro, tayi ƙoƙarin maida aman daya kuma taso mata, tayi imani cewa yanzu kam Salamatu na ƙara maida ita cikin bujenta, to wallahi mutuwa zatayi, yanzun ma kaɗan ya hana ta suma, ko yanzun ma bawai ta tsira bane, dole nema sai taje asibitin cikin gari anyi mata wankin ciki, don warin tusan Salamatu kaɗai ya isa ruɓar da hanji.

Ummee ne taja Salamatu suka koma gefe dan sauri take zata koma, ita kuwa Kaltume tuni ta rarrafa ta arce da gudu batare data kwashe aman da tayin ba, kwafa Salamatu tayi tare da cewa.
"Wallahi zankwashe nakuma samiki aleda abiyoki dashi har gida."

Murmushi kawai Ummee tayi tare da gyara zama, nan suka sake sabon gaisuwa da Salamatun harma dasu Malam Musa, da kuma Halliru,   babban ledan dake gabanta ta miƙowa Salamatun cikin halinta na nagarta tace.
"Wannan saƙone daga wajen Farouq , wato wanda yake neman auren Ma'azzara, shida kansa yace akawo muku!."
Baki Salamatu ta washe take ta jawo ledan tare da buɗewa, ganin abun dake ciki yasa ta dafe ƙirji, cikin mamaki tace.
"Ƙalu innalillahi duka wannan nawane? kayafa nake gani niƙi niƙi Hajiya, halan ko mai shegen arzikine shiɗin?."

Jin abun da Salamatun ta faɗa yasa Halliru matsowa da sauri, ya ƙaraso wajen yana kiran Ladi matar sa , so yake ya leƙa cikin ledan amma tuni Salamatu ta kulle bakin ledan ta ɗaga ƙasan bujenta ta tura ledan, fuskarta cike da tsananin farin ciki marar misaltuwa tace.
"Wayyo daɗi barni daraina karka kasheni, ashe Ma'azzara zata zamo alkhairi agaremu, kai nagode sosai Hajiya, Allah yaƙara muku arziki dukanku, a'a wannan abu ae yayi daɗi  hahahhhhh, lallai wasu zasu mutu da baƙinciki." Taƙare maganar cikin matsanancin shauƙi, har wani karkaɗa ƙafanta take, tana girgiza kai alaman duniya tafara samuwa agareta.
Murmushi Ummee tayi, tare da miƙewa tayi musu sallama, nan fa Salamatu ta rakota Itada da Halliru da Ladi matarsa, suna tambayar lafiyar Ma'azzara da uwayan hidanta, sun duk a gaishe su, har bakin ƙofar gida suka rakata, Salamatu ta dawo sai washe haƙora take, kai kace bushara akai mata da aljanna.
Tana dawowa gida ta baje akan ɗan rumfan dake bakin ƙofar ɗakinta, nanta buɗe ledan tare da zazzage duk wani abu dayake ciki, atamfofine masu kyau sosai guda uku, sai kuma yadin shadda na maza masu kyau suma guda uku, sai kuma takalman maza ƙafa uku, haka na mata ma irin flat shoe ɗinnan suma masu kyau,  sai kum kuɗi naira Jaka ashirin ta cefa, guɗa Salamatu tayi saikuma ga tusa mai ƙarfi ta biyo baya, cikin tsananin jin daɗi tace.
"Ayyiririii!! Saini Salamatu, tabbas dama naji ajikina cewa duniya takusa fara damawa dani, ahayye nanaye!." Taƙare maganar tana sake sakin guɗa.
Ganin uban kayan dake gaban Salamatun yasa Halliru sakin murmushi, cikin jin daɗi yace.
"Kai amma kuwa Salamatu mun more suruki, lalle zamu fantama ji wasu yadukan shadda masu uban kyau." Yaƙare maganar yana kai hannunsa daniyar ɗaukan shadda ɗaya ya duba.
Hannu Salamatu ta sanya ta buge nasa hannun, wata uwar tusa ta sake mai shegen masifar wari tare da galla masa harara, aharzuƙe tace "To mazari, sarkin azarbabi, harwani bakin yaba kaya kake dashi, inace nannan kwanakin baya, kadinga zugani kan cewar kada na yarda na bar musu Ma'azzara, yanzu kuma shine da alkhairi ya isoni, kake neman shigewa jikina muci tare ko, to ƙwalelenka."

Hannu Halliru ya sanya ind a ya toshe hancinsa, sosai warin tusan kesawa yana jin ɗaci amaƙoshinsa, kwantar da murya yayi cikin son lallaɓata yace.
"Haba Salamatu mufa ƴan uwan junane, kuma kin manta tun kwanaki muka shirya muka kuma daina faɗa, inkin bani ae ba raguwa zakiyi ba Salamatu, kuma kin manta da cewar ma ita matan ɗazu da sunan Hajiya ta ƙiraki? Hajiya Salamatu fa tace, kika sani ma ko shirye shiryen kaiki Makka suke!." Halliru yafaɗi haka cikin son Koɗa Salamatun.
Aikuwa ta famfu don lokaci guda taji kanta yaƙara girma, take ta washe baki, nan fa taciro shadda kala biyu da takalmi kala ɗaya ta basa,  take ya cika da matsanancin murna, haka ma taɗauki shadda kala ɗaya da takalma kala biyu tabawa Malam Musa dake tsaye yana jinsu tun ɗazun, dubu bibbiyu tabawa kowannensu,ita kuma tasa sauran aƙasan bujenta, nan sukayi mata godiya.

*Naimey*
Yau tsawon sati ɗaya da kwna 2 da faruwar al'amarin, Ma'azzara ta kame kanta bata yarda ta nuna wata damuwarta tana ƙoƙarin cire uncle Adamcy a ranta, sau biyu rak suka hadu, amman bata yarda ta nuna masa wani abubu gaishe sa kawai take, ta saki ranta suna hira da Hussy tana ma ummu wasa. Hakan yasa Hussy watsar da duk wani kokwanto, Hassana kusan kullum se tazo amman bata samun ganin Adamcy ko Ma'azzara dan ta maida hankalinta karatu, bata dawowo sai kusan 5 pm.

Yau ta kama Weekend ne Adamcy yana gida amman yana ɓangaransa can suka wuni suna sheƙe ayarsu da Hussy unmu Saudat kuwa na gun Ma'azzara, wacce yau se kuka take ta rasa dalilinsa.
Tunda Adamcy ya fita bayan sun gama more rayuwar su da Husst, yafita gidan bashi yadawo ba sai bayan sallan isha.

Hussaina ce zaune tayi jigum inda take karanta text message ɗin da ƴar uwarta Hassana taturo mata, wanda gama wayarsu da ita kenan,  ahankali take karanta text message ɗin, inda aka rubuta saƙo kamar haka.
_Ni ƴar uwarki ce Hussaina, bazan faɗa miki maganar da take bahaka ba, babban kuskuren dakikayi arayuwa shine bawa tsintacciyar mage dama, nafaɗa miki amma kinƙi amincewa, kan cewar lallai yarinyar nan da Adamsy son juna suke, shikenan to amma inaso kibani haɗin kai don mujarraba, idan muka gwadasu kikaga saɓanin abun dana faɗa miki, nayarda kada ki gaskata tunani na._
Shiru Hussaina tayi, har acikin ranta gani take cewa shirme kawai Hassanan nata ke faɗi, waima bayan tace Ma'azzara ne keson Adamsy, yanzu ta dawo tamace wai Admsyn nata ma nason Ma'azzara, murmushi kawai Hussaina tayi, tabbas tasan idan tabiyewa bahagon tunani irin na Hassana, to fa tabbas zata kwan aciki, amma kodan ta ƙaryata tunanin Hassanan zata amince su jarraba, tasan dai babu wani abu tsakanin Ma'azzara da Adamsy, sam baima yiwuwa ace wai Adamsy da  Ma'azzara son juna suke, tasa aranta cewa shirmene kawai irin na Hassana.
Tayi nisa acikin tunaninta,saiji tayi ya kwanta abayanta, murmushi tayi tare da juyowa ta fuskancesa.
Idanunsa ɗaya ya kashe mata, ahankali yace. "Kin manta dani ko?."  
Lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa ta shafa, tare da shigewa cikin jikinsa, fuskarta ya ɗago inda ya haɗe bakinsu waje ɗaya,  ahankali yake bata professional kissing.

Ma'azzara kuwa tana idar da sallan isha, miƙewa tsaye tayi, ɗan madaidaicin fridge ɗin dake cikin ɗakin ta buɗe, goran yoghurt ta ciro, inda tasha kaɗan ta maida sauran,   komawa kan gado tayi ta kwanta tare da duƙunƙunewa waje ɗaya, ahankali hawaye ke tsiyaya daga cikin idanunta, kasancewar tayi kuka sosai, hakan yasa tana kwanciya bacci ya ɗauketa, wanda ke cike da mafarkin Uncle ɗinta, mafarki masu daɗi tayi dangane dashi, wanda sune suka gusar da damuwar zuciyarta.

Washegari, Saturday.
Tun 7 yabar gidan domin suna da meeting da wani babban kamfani da zasuyi.
Kasancewar yau weekend yasan ya koda tatashi bata fito ba, sai wajen 8 sannan ta sauƙo,  Nan ta iske Aunty Hussaina zaune a falo, tana bawa Ummu Saudat nono,  cikin girmamawa tagaishe da Auntyn nata, tare da zama akusa da ita, nan ta karɓi Ummu Saudat ɗin, tanayi mata wasa, duban tsab Hussaina tayiwa Ma'azzaran, take taji wani abu ya ɗarsu aranta,  saurin kawar da tunanin da ke ranta tayi, ahankali taƙira sunan Ma'azzaran.
Ɗago kai Ma'azzara tayi ta dubeta, murmushi tayi tare da cewa "Na'am Aunty."
Cikin kulawa Hussaina tace "Meyasame ki naga idanunki sun kunbura, kuka kikayi ne?."
Da sauri Ma'azzara tayi ƙasa da kanta, cikin sanyin murya tace.
"A'a Aunty kawai dai ƙwaro ne ya shiga idona."
Murmushi Hussaina tayi tare da cewa, "Allah ya sauwaƙe."
Tashi tsaye tayi tare da duban Ma'azzaran tace. "Gacan kayan break ɗinki nan a dinning, ki kulamin da Ummu Saudat, ni zanje gida bazan jimaba zan dawo."
"To" Kawai Ma'azzara tace, tare da ƙarasawa gaban dinning ɗin, still tanayiwa Ummu Saudat wasa.
Chapter 28 · 0% Book details