← Book details Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 31

Sashe 30

Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Akram girgiza mata kai yayi yace " kwarai shine ya koma haka bamu San mai yake damunsa ba zakiga yana ta ihu yana cizge fatar jikinsa yana fad'ar abubuwan da ya aikata yana ya tuba ya daina kullum sai ya rok'i a harbeshi ya mutu akan azabar da yake ciki"

Girgiza Kansu kawai suke yi suna mamakin halin da suka ganshi a ciki dan ko iya manya manya tsutsosin dake crawling a jikinsa ya ishe shi azaba

Samha na k'ok'arin magana Na Maliya ya bayyana yana kyalkyale dariya babu Wanda yake ganinsa sai Alhaji Bala

Alhaji Bala da muryarsa bata fita yana daga kwance ya fara ihu yana Na Maliya ya kashe shi ya huta

Aikuwa na Maliya na watsa mishi ruwan kaikayi ya mik'e da skeleton d'in jikinsa ya fara cizge Sauran fatar dake jikinsa yana ihu har Dana fuskarsa

A tsorace su Suhaima suka ja da baya suna kallon ikon Allah Alhaji Bala kuwa sai cizge cizge yake yi

Yafi k'arfin minti Ashirin ahaka kafin ya zub'e a k'asa yana kuka yana rok'on mutuwa tazo ta d'aukeshi

Girgiza kai su Samha kawai suke suna Al ajabin halin da suka ga Alhaji Bala a ciki Saiam kuwa cewa take lallai Allah ba azzalumin bawa bane tun a gidan duniya yake Hisabi ko ahaka aka bar Alhaji Bala ya girbi abinda ya shuka

Ahaka Akram ya maidasu gida suna Al ajabin halin da suka ga Alhaji Bala

Dangin Alhaji Nazifi kuwa ganin suna tayiwa Alhaji Bala zancen Aure yak'i basu had'in kai ne yasa suka sa ranar da za'a d'aurawa su Suhaima Aure shima zasu d'aura mishi da Nazifa Cousin d'insa
[8:15PM, 4/22/2018] ‪+234 813 272 6929‬: 🌑 🌑 *B🅰K'IN D🅰RE*🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑

*Written by*
💅💅 *Sadnaf*💅💅

*A heart touching story*

® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛ'Ş_

#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com

*Follow me on Wattpad@Sadnaf*

*END*

Shirye shirye ake tayi kowane b'angare babu kama hannun yaro inda kan amaren ya d'au zafi ga exams da suke yi ga gyaran jiki da ake musu kullum basu da lokacin Kansu ko kad'an Dan ana musu gyaran jiki suna karatun exams basa ma iya wani wayan kirki da angwayen nasu sai dai messages dama tuni suka daina zuwa zance

Alhaji Nazifi kuwa gyara yayi wa gidansa sosai Dan sai daya canza komai na gidan ya koma sabo hatta b'angaren Hajiya Nafeesa sai da aka saka sababin furniture's dangi kuwa sai murna suke suna yayi gyaran gida adaidai kamar yasan shima angwancewar zaiyi.

Ba k'aramin kud'i ya kashewa su Suhaima ba komai iri d'aya yayi musu sai dai bambamcin kala d'an k'aramin lefe ya k'ara musu bayan uban lefunan da aka kawowa kowace a cikinsu abinda ake cewa gata kam sun same shi Dan wasu kayan ma sai su shekara biyu basu yi amfani dashi ba

Akwana a tashi babu wuya duk abinda aka sawa rana sai yazo an shiga satin biki an fara shagulgula duk da Su Suhaima sun ce basa San wani party waleema kawai zasuyi a ranar da akayi d'aurin Aure amma sai da Angwayen suka tilasta musu zuwa dinner da suka had'a gabad'aya a wani katon hall Amare sun sha kyau sai walwali suke Akram ya k'asa d'auke idonsa daga kan Samha sai kallonta yake yi Dan tunda yake da ita idan ka d'auke wet lips ko kwalli bai tab'a ganinta dashi ba sai gashi ta sha Heavy make up ta canza mishi kamar ba ita ba Samha kuwa kamar ta nutse Dan kunyar irin kallon da Akram ke binta dashi dan ba normal kallo bane daya saba yi mata

Ahaka taro ya watse cike da farinciki da annashuwa

Samha a ranar Sam bata ganewa Akram dan sababin abubuwa ya b'ullo mata dashi da suka je sauke su a gida kamar ba Akram mai kunyar nan ba rikice mata yayi yana matse hannayenta ita kuwa jikinta ya hau rawa wani irin tsoronshi ya rufeta data ga yanda idonsa ya kad'a yayi jajur dak'yar ta fusge hannunta ta fito daga motar aguje har suna bangaje juna da Saheebar da itama ta fito jikinta na rawa dan kamar had'in baki Yazeed shima birkice mata yayi yana Neman maida ta cikinsa sabida rungumar da yayi mata

Jiki a sanyaye suka k'arasa part d'insu kowace da tunanin da take a zuciyarta take tsoron angwayen nasu ya rufesu

Su Saiam kuwa sai tambayarsu suke abinda yafaru suka gansu haka babu wacce ta iya magana acikinsu suka fara k'ok'arin rage kayan jikinsu

Suhaima ce karshen shigowa itama kana ganinta kasan a firgice take a k'asa ta zube tana sauke numfashi dan dak'yar ta iya kwatar kanta a hannun khaleed dan shi har dasu kiss ya mata

Su Saiam mai zasuyi idan ba dariya ba dan ko basu fad'a musu ba sun gano su

Suhaima ce tayi k'arfin halin magana tana "Aunty wai dan Allah wane irin turare kika fesa mana haka gaskiya kar ki k'ara fesa mana bama so fyad'e Khaleed ya kusa yimin a mota yana tambayata wane irin turare na fesa mai d'aga hankali"

Babu abinda su Saiam keyi sai dariya Safna kuwa tace " kinsan nawa muka kashe kuwa wajen had'a muku turaren nan ai sai ma gobe wlh wanka zamuyi muku dashi"

Samha da Saheeba kuwa tunda kowacensu ta zauna suke ta sake sake aranau suna ta ganin kiran angwayen nasu suka k'asa d'agawa

Suhaima ce kawai bakinta bai mutu ba sukayi ta magana dasu Saiam dan su basa jin wani nauyin juna tamkar kawaye haka suke

Safna ganin bakinsu Saheeba ya mutu basa magana yasa ta koma tana tsokanarsu dan tun yanzu su bari ma sai gobe Saiam ta karashe da 'wayaga idon Auta gobe a karshen gado tana dan Allah Akram kayi hakuri"

Samha kuka ta fashe dashi tana ta fasa Auren su Suhaima kuwa sukayi ta mata dariya

Washegari k'arfe 11 dubanin mutane suka shaida d'aurin Auren Suhaima da Khalid Saheeba da Yazeed Samha da Akram a karshe yayan Alhaji Nazifi ya matsa kusa da liman ya mik'a mishi bandir d'in dubu hamsin yace a d'aurawa Alhaji Nazifi Aure da 'yar uwarsa Nazifa

Alhaji Nazifi k'asa kwakwaran motsi yayi sabida mamaki har sai da aka d'aura Auren shi da Nazifa surukan nasu sai murna suke dan dama suna tunanin yanda zai yi rayuwa shi kad'ai idan y'ay'ansa suka tafi gidajen mazajensu

Ciki kuwa amadadin farinciki kuka amaren suka fara yi da suka tuna Hajiya Nafeesa kafin kace me kowace ta fara k'walla tana ina ma Hajiya Nafeesa tana rayye taga Auren 'ya'yanta gabad'aya tuni mutuwarta ya dawo musu sabo fill aka hau koke koke duk yanda anwagwayen suka so suyi hotuna da amaren nasu sai hakura sukayi

Alhaji Nazifi kuwa ana gama d'aurin Aure ya nufi b'angaren Hajiya Nafeesa ya tafi can kuryar d'akinta ya kwanta akan gadonta ya d'auko hotonsu dake taya shi kwana ya kife kansa akai yafara kuka yana mata addu'oin samun rahamar ubangiji dan bai tab'a tunanin zai auri wata ba bayan mutuwarta shi da yake tunanin bazai iya rayuwar Aure da wata ba sai gashi an d'aura mishi Aure da Nazifa

Kuka ya sha sosai har sai da yaji kansa na Neman darewa gida biyu dak'yar ya iya mik'ewa ya wanke fuskarsa yafito sabida kiran da ake ta damunshi dashi a waya.

Ciki kuwa Sai a lokacin su Saiam suka ji labarin Auren Alhaji Nazifi da Nazifa

Sunyi farinciki sosai da d'aurin Auren dan suna ta tunanin yanda Mahaifinsu zai yi rayuwa shi kad'ai idan sun tare.

Ahaka aka cigaba da shagulgula k'arfe biyu aka fara Walimar da Yayan Hajiya Nafeesa ya had'a musu a harabar gidansa

Nasiha da wa'azi akayi musu sosai mai ratsa jiki sai zubar da hawaye sukeyi

K'arfe hud'u da rabi dangin khaleed suka iso dan tafiya da amaryarsu dan Bauchi za'a kai Suhaima

Alhaji Nazifi kuwa dama guduwa yayi daga gidan yace yayansa ya wakilce shi wajen yi musu addu'a dan Sam bazai iya jure ganin kukansu ba dan sai arasa mai rarrashin wani

Rungume juna sukayi sosai suna kuka kamar zasu shide dak'yar aka bambare su daga jikin juna

Ahaka aka tafi kai Suhaima gidanta sai kuka take

K'arfe shidda dai-dai aka zo tafiya dasu Saheeba dan gidansu d'aya da Samha Katanga ne kawai ya raba su hakan kuwa ba k'aramin dadi yayi musu ba dan at least idan suna ganin juna zasu ringa rage kadaici

Suna rungume da juna har aka kaisu gidajensu sai kuka suke kamar zasu shidde kan Samha kuwa kamar ya rabe biyu sabida kuka

Ana fita dasu Samha aka shigo da amarya Nazifa b'angaren Hajiya Nafeesa aka kaita itama sai fargabar irin tarb'ar da angonta Alhaji Nazifi zai mata take dan tana da masaniyar bai San da Auren ba sai yau

Sai k'arfe goma sha d'aya su Akram suka shiga gidajensu Akram kamar ya zuba ruwa a k'asa ya sha dan cikar burinsa

A can karshen gado ya hango Samha nata kuka ta rik'e kanta

Nufarta yayi da sauri tare da watsar da kayan dake hannunsa birkitota yayi gabad'aya jikinsa hankalinsa a tashe ya fara tambayarta abinda ya sameta

Samha kuwa luf tayi a kirjinsa tana nuna mishi kanta

Hannu ya kai ya tab'a kanta aikuwa yaji da zafi rau da sauri ya duro daga kan gadon ya had'a mata ruwa mai dan dumi dan tayi wanka

Ganin tana ta wani nonok'ewa da dukan alamu a tsorace take yasa ya rok'eta data kwantar da hankalinta babu abinda zai mata ta dai bashi had'in ya bata abinci tasha magani stress ne ya mata yawa

Da haka hankalinta ya kwanta ta shiga band'akin tayi wanka tana fitowa ya tura mata gashashen kazar da ya shigo dashi gabanta ya rok'eta taci ta sha magani dak'yar taci cinya biyu tace ta koshi ta dai sha yoghurt d'in sosai

Paracetamol biyu ya bata ta sha daga nan ya umarceta data kwanta tayi bacci

Kan gadonta ta hau ko minti biyar batayi ba bacci yayi awon gaba da ita dan tana da tabbacin babu abinda Akram zai mata

Akram kuwa shima kintsawa yayi yayi nafilolinsa ya kwanta abayanta yana karewa surarta kallo sai hadiyar yawu yake yi

Su Suhaima da Saheeba kuwa angwayensu basu d'aga musu k'afa ba aranar suka baje amarensu
Chapter 30 · 0% Book details