← Book details Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 31

Sashe 23

Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saheeba da sauri tace "ni bashi yake bani mamaki ba yanzu dama wannan Dan iskan mutumin ba Dan fashi bane ya tsaya aka kashe Mommy agaban idonsa bai iya tab'uka komai ba duk da sunan bincike ake tafiya dashi Fashi ayi kissa agaban idonsa ayiwa mata fyad'e duk yana tsaye yana da ikon da zai hana shi aiwatar da mugun nufinsa akan yaran mutane yana da ikon da zai hana shi ya Harbe mana Mommynmu amma ya tsaya aka kashe Mommy a gaban idonsa na tsane shi wlh bai burgeni ba bai tashi sawa a kama shi ba sai da aka kashe Mommy"

Ta k'arasa maganar sirarran hawaye na bin kuncinta

Nanauyan ajiyan zuciya Alhaji Nazifi ya sauke ya juya ya kalli Suhaima yace "karki tsane shi Suhaima akan aikinsa yake ba kowane zai iya d'aukan risk d'in da ya d'auka ba mutane da yawa sun sha rasa rayyukansu agarin binciken mai laifi irin na Alhaji Bala masu fuska biyu ni kuma ji nayi ina kaunarsa araina ba dan shi ba mutane ba zasu tab'a sanin waye Alhaji Bala ba haka zai ta tafka zalunci a doron k'asa ba tare da ansan shi bane ki daina alak'anta mutuwar Mahaifiyarku dashi domin ko da ya hana ko bai hana ba lokacinta ya Riga da yayi gaskiya Akram S Adam yayi namijin k'ok'ari sosai sai dai ayi mishi addu'ar gamawa da duniya lafiya dan""""

Kiran mak'ocinsu daya shigo wayarsa ne ya katse mishi maganar da yake yi yana d'agawa shima yace ya kunna TV yaga ikon Allah murmushi kawai yayi yace yagani

Aranar duk Inda ka zagaya hirar Alhaji Bala kawai ake yi duk wani social net labarin Kawai zaka ji anayi na irin namijin k'ok'arin da Akram yayi har asirin Alhaji Bala ya tonu

Manyan masu kud'i da 'yan siyasa zirya kawai suke ringa yi suna zuwa ganin Akram tare jinjina mishi aranar Akram Sam bai samu zama ba kansa har wani ciwo yake

Alhaji Bala kuwa hannunsa da k'afa sanye yake da ankwa banda 'yan sanda biyu dake gadinsa Dan ba waje d'aya aka sa shi dasu killer ba for the first time da yaji wani irin kunya da nadama ya lullub'eshi wai shi da jama'an gari suka sani amatsayin mai taimakon talakawa sai gashi asirinsa ya tonu cikin kankanin lokaci Lallai Akram ya gama dashi yanzu Ashe dan yagano shi waye da irin sana'ar da yake yi yasa ya bishi har port Harcourt yaringa siyar da alewa ya San yanzu 'Yan garinsu sun ji labari har da Mahaifiyarsa da wane ido zai kallesu da wane ido zai kalli jama'an gari inama mutuwa ta d'auke shi yanzu ina ma k'asa ta tsage ya shige ciki

Ahaka ya ringa zancen zuci hawaye na kwarara a idonsa

Samha kuwa wunin ranar sukuku tayi shi ta kuma rasa mai yake damunta babu Wanda ya kai ta farincikin tonuwar asirin Alhaji Bala Dan kullum addu'arsu kenan to amma me wani Abu mai nauyi take ji game da Akram duk fitar lafazinsa na jawabai da yake yi akan Alhaji Bala da hanyoyin da yabi har yayi nassarar kama Alhaji Bala sai taji gabanta ya fad'i ta kuma rasa dalili haka kawai take ji aranta tsabar kiyayyan da take musu ne ya janyo haka amma me ta k'asa d'auke idonta daga kansa a hotunan sa da ake ta watsawa a shafukan face book dasu watsapp

A cikin kankanin lokaci aka mik'a Alhaji Bala kotu Dan a yanke mishi hukuncin sabida duk shaidun da ake bukata akwai su

Motocin 'yan sanda sunfi ashirin da suka yi layi kawai dan rakiyar Alhaji Bala zuwa kotu

Alhaji Bala kuwa kamar ya shide yayi kukan yayi nadamar har ya saba da ganin Na Maliya na zuwa yi mishi dariyar keta banda Hajiya Nafeesa da Mai gida dake yawan zuwan mishi daddare yayi ta ihu kenan har gari ya waye nan da nan ya zama siriri k'arfi da yaji banda kasumbar da ya ajiye

Ana fitowa dashi 'yan jarida sukayi dafifi suna shek'a mishi tambayoyi hasken flash kake gani ko ta ina

Babu ma hanyar da zaa wuce

Alhaji Bala kuwa sunkuyar da kansa yayi k'asa hawaye kamar an bud'e famfo jama'ar gari kuwa duk sun hau hau saman kwanun gidajen mutane Dan su hango Alhaji Bala mai fuska biyu

'Yan sanda ture jama'a kawai suke Dan su samu hanyar wucewa

Wani Dan jarida ne ya rok'i Alfarmar abasu minti goma kawai suyiwa Alhaji Bala tambayoyi

Dak'yar aka amince suyi mishi tambayoyin inda Alhaji Bala yaji kamar ya nutse dan kunya

Wata 'yar jarida ce ta fara jefo mishi tambaya "Alhaji Bala mai zaka iya cewa game da tuhumar da ake maka na fashi da makami kai da jama'an gari suka san mutumin kirki ne mai taimakon talakawa"?

Tana rufe baki wani ya jefo masa nashi tambayar " Alhaji Bala tsawon wane lokaci ka d'auka kana wanan mumunar aiki shin dama can ta silar fashi kayi kud'i kake taimakon mutane ko kuwa dama kana da kud'in daga baya ka koma kana farautar dukiyoyin jama'a?

Alhaji Bala kansa ya k'ara sunkuyarwa Dan bai San mai zai ce musu ba sai da wani ya k'ara jefo mishi nashi tambayar yayi k'arfin hali ya d'ago aikuwa tuni aka hau kashe mishi ido da flash 'yan jarida kuwa kamar zasu shige jikinsa sabida kawai suji ta bakinsa kowa mik'a recorder d'insa yake saitin bakinsa Dan ya ji mai zai ce Sosai

Alhaji Bala cewa yayi "bansan mai zance ba ayanzu banida bakin magana a yanzu ni ban ma San yanda zan muku bayani ba kuma yanda kuke mamakin tuhumar da ake min nima haka nake mamakin tuhumar da ake min"

Haka kawai Yaji kalaman na fita a bakinsa Dan gani yake idan yayi saurin mik'a wuya mutane sai sunfi yarda da shi Dan fashi ne amma idan ya ringa musanta zargin da ake mishi ahaka zai yi ta wahalar da shariar

Mamakine ya rufe Akram da ya ji mai yace

Alhaji Bala na k'ok'arin magana ya ji an jefo mishi dutse a goshi kafin kace mai jama'an gari sun hau cewa "karya kake azzalumi asirinka ya tonu dutse ake jefa mishi ko ta ina

'Yan sanda kuwa tuni suka hau sakin harbi sama dan su tsawatar musu da haka suka samu suka dan watse suka koma daga nesa suna jefo duwatsu

'Yan jarida kuwa tuni suka yi nasu wajen dan wasu a cikinsu sun samu nasu rabon dutsen

Ahaka aka tisa keyar Alhaji Bala da goshinsa Ke tsiyayar da jini da gefen kansa suka d'au hanyar high court

Cikar da kotun yayi b'ata bakine dan har waje mutane ne burin kowa yaga Alhaji Bala mai fuska biyu manyan masu kud'i ma da suka san shi sun samu zuwa ciki har da Alhaji Nazifi da Ghali
'Yan sanda sai da sukayi dagaske suka shige da Alhaji Bala ciki 'yan jarida kuwa suma sun cika kotun burin kowa ace shi yafi d'aukan rahoto

Alhaji Bala kuwa addu'a kawai ya ringa yi mutuwa ta d'aukeshi dan abinda ake cewa kunya kam jinshi kawai yake a hankali ya d'ago da kansa aikuwa suka had'a ido da Mahaifiyarsa idonta yayi jajir sabida kukan da ta sha yana k'ok'arin d'auke idonsa suka had'a ido da Hajiya lubna idonta kamar ya fad'o sabida harararsa da take yi da gani itama zuwa tayi ta tona mishi asiri

Wajen da masu laifi suke tsayawa ya tsaya ya sunkuyar da kansa a lokacin da aka ringa shigowa dasu lion Akram ne k'arshe daya shigo yana sanye da Uniform d'insa ya balain yi mishi kyau waje ya samu ya zauna

ba tare da b'ata lokaci ba Alkali ya fara gabatar da laifin da ake tuhumar Alhaji Bala dashi

Duk had'in kan da ake so su Lion su bayar sun bayar dan sun fad'i irin aika aikan da suka ringa yi Black ne ma yaso yayi karya ya ji an kwashe shi da wani mugun mari daya sa sai da ya jingina da bango murya kawai yaji ana ka fad'i iya gaskiyarka ko na canja ma kamanin

Da Sauri Black ya fara basu labarin duk abinda ya sani kamar an kunna radio ko ajiyar zuciya baya saukewa sai da suka gama amsa duk tambayoyin da aka musu aka koma kan Alhaji Bala daya sunkuyar da kai idonsa a runtse

Full name d'insa Alkali ya kira Alhaji Bala ya d'ago ahankali yana kallonsa

Alkali tambayarsa yayi akan ya basu labarin yanda akayi ya tsinci kansa a cikin wannan mugun sana'a mai kuma zai iya cewa game da tuhumar da ake mishi

Alhaji Bala sai da ya d'auki tsawon minti goma yana tunanin mai zai ce dan fa Sam ba zai iya mik'a wuya Cikin sauki ba

Kau da kansa yayi yace duk abinda ake tuhumarsa da shi karyane sharri aka mishi

Yana rufe baki yaga fatalwowin wayanda ya kashe sun fara bullowa ta jikin bango dukansu da dogwayen bulala a hannunsu

A razane yaja da baya ya wage baki zai yi ihu aikuwa yafara jin lafta ko ta ina.................😂😂😂😂

I swear I don tire😡😡😡

🌑 🌑 *B🅰K'IN D🅰RE*🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑

*Written by*
💅💅 *Sadnaf*💅💅

*A heart touching story*

® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_ɯɛ ɖơŋ'ŧ ơŋٳყ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛ'Ş_

#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com

*Follow me on Wattpad@Sadnaf*

*AUNTY SIS*💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗💗
*Wherever you are just* *know that we are* *missing you so much*
*You will always stand as a legend* *in our world. We will forever Love and cherish you. Our heart warming prayers are always with you. Come back soon please*

*Page 17*

Tuni mutane suka k'aure da sallati sakamakon rawan alantar da Alhaji Bala ya ringa zubawa shi kad'ai yana ihu babu abinda kake ji sai sautun bulalai yana suyi hakuri zai fad'i gaskiya tuni ya fito daga inda masu laifi ke tsayawa ya nufi tsakiyar kotun ya ringa tsalla ihu yana shoshe shoshe

'Yan jarida kuwa tuni suka ja da baya suna d'aukarsa hotuna da video

Wasu 'yan sanda biyune sukayi k'arfin halin zuwa kusa dashi aikuwa suka ji saukan bulalai a gadon bayansu aguje suka bar wajen

Mutanen kotun kuwa hankalinsu a tashe suka zubawa Alhaji Bala ido dake Neman fita daga hayyacinsa sabida tsabar azaba
Chapter 23 · 0% Book details