← Book details Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 31

Sashe 12

Bakin Dare Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Babu yanda Saiam ba tayi da Samha akan ta bari ruwan da aka sa mata ya kare ba fir tak'i akan dole Saiam ta kira likita ya Sallamesu

Naila da sauri ta juya tayi waje sakamakon ganin towel d'in da Alhaji Bala ke d'aure dashi a kugunsa ya fad'o k'asa

Alhaji Bala sabida tashin hankali da tsoratar da yayi bai ma San a tsirara yake ba

Hajiya Lubna kuwa itama cikin rawar jiki ta nufi wajen Alhaji Balan daya jik'e da gumi ta d'auki towel d'insa dake k'asa tace

"Alhaji lafiya kuwa mai ya firgita ka haka da har towel d'inka ya bar jikinka Baka sani ba"?

Alhaji Bala sai a lokacin yasan a tsirara yake hannuwansa na rawa ya k'arbi towel d'in daga hannun Hajiya Lubna ya d'aura tare da zama a gefen gado still yana hango Hajiya Nafeesa a tsaye a idonsa

Numfashinsa sai fita yake da Sauri sauri

Hajiya lubna itama zama tayi agefensa Dan tunda take dashi bata tab'a ganinsa acikin irin wanan halin ba

A hankali tace "Alhaji Lafiya mai ya tsorata ka haka ko dai mafarki kayi"?

Alhaji Bala bai ce mata komai ba har lokacin jikinsa bai bar rawa ba

Magana Hajiya Lubna ta k'ara yi

Alhaji Bala ya daka mata wani mugun tsawa yana "dala ki rabu dani Wai meyesa bakida hankaline dolene sai na gaya miki abinda yake damuna"?

Hajiya Lubna da sauri ta mik'e tayi waje ba tare da ta tsaya bashi hakuri ko taji mai zai cigaba da cewa ba

dan haka take idan taga ransa a b'ace bata tsayawa a wajen barin gurin shi zai fiye mata alheri dan itama akwai zuciya

Naila data yi jugum a Palo tana ganin Hajiya Lubna ta fito ta tareta da sauri tare da tambayarta abinda ya samu Abbanta

Hajiya Lubna da itama ranta a b'ace bata cewa Naila komai ba illa ma hannunta da ta rik'e sukayi hanyar d'akinta

Naila kuwa ganin babu fuska yasa bata k'ara tambayarta ba ta kwanta kamar yanda Hajiya Lubna ta kwanta

Alhaji Bala aranar kwanan zaune yayi a tsorace gani yake ko yaya ya runtse idonsa Zai iya ganin Hajiya Nafeesa

Rayuka nawa ya kashe amma babu wacce ta tab'a masa fatalwa sai Hajiya Nafeesa tunda yake ko mafarkin wayanda ya kakashe bai tab'a yi ba sai Hajiya Nafeesa me hakan ke nufi agaskiya bai ga ta zama ba dole da asuba ya d'au hanyar Maiduguri yaje ya nemi taimakon mai gida

Allah Allah kawai yake gari ya waye

Wajen k'arfe 3:40 yafara gyangyad'i a zaune sai baccin ya kusa sace shi sai yayi firgigit ya zauna ahaka ya ringayi har sai da baccin yaci k'arfin idonsa ya kwanta bacci yayi awon gaba dashi

Mafarki ya fara yi da Hajiya Nafeesa tana ta kuka ga kirjinta na ta zubar da jini sai binshi take da gudu shima yana ta gudu da iya k'arfinsa sai ihu yake yana azo a taimaka mishi amma ina gani yake kamar ba gudu yake ba sabida Hajiya Nafeesa tana dab da k'arasowa inda yake
Hannu ta mik'a da niyyar damk'o shi ya mik'e a firgice yana ihu sabida ba ilimin islama ballantana yayi sallati

Yana zama ya kuma hango hajiya Nafeesa abakin k'ofa atsaye kamar dai yanda ya ganta a mafarki

Wani razannan ihu ya saki da iya k'arfinsa

Hajiya Lubna da Naila suka kwasa aguje sukayi d'akin

Suna bud'e k'ofa Hajiya Nafeesa ta b'ace

Alhaji Bala kuwa ya ringa wani irin k'yarma kamar mai jin sanyi ga wani uban gumi kamar Wanda aka kwarawa ruwa

Naila a bakin k'ofa ta tsaya dan towel d'insa ya kuma yin wani wajen

Hajiya Lubna kuwa fuska a d'aure ta nufi wajensa tana "Alhaji wai me hakane mai yake damunka kake ta mana ihu ka fad'amin ka k'i ka fad'amin abinda yake firgita ka wai mai haka ne dan Allah dan annabi"?

Hajiya Lubna tace tana jefa mishi towel d'insa daya yi gefe

Alhaji Bala ajiyar zuciya Kawai yake yana kalle kalle sai zare ido yake

Hajiya Lubna wadrobe ta nufa ta d'auko mishi wani dogon jallabiya da gajeran wando

Ta cilla mishi adai dai lokacin da Naila ta bar d'akin

Hajiya Lubna kuwa tace " ga kaya nan ka sa tunda abinda yake firgita ka saka yake kayi tsirara agaban 'yarka"

Alhaji Bala da sauri ya zura jallabiyar da gajeran wandon yabi bayan Hajiya Lubna data yi hanyar waje da sauri dan baya jin zai Iya zama a d'akin shi kad'ai

A palo suka zauna gaba d'aya Naila ta hau jerawa Alhaji Bala da jikinsa ke rawa Sannu

Alhaji Bala shi dai kansa a sunkuye yana hango yanda yaga Hajiya Nafeesa a mafarki da zahiri a hankali ya d'aga kai ya kalli agogon dake bangon palon yaga hud'u da minti Arbain an fara ma kiraye kirayen Sallahr asuba

Hajiya Lubna tagumi kawai tayi tana kallon shi aranta tana ta mamakin abinda yake tsorata shi ya fita daga hayyacinsa haka

Alhaji Bala kuwa yana ganin biyar tayi ya mik'e ya d'auko mukullin motarsa a d'aki sai juye juye yake dan duk a tsorace yake

Ko salla bai tsaya yi ba dan dama ba damunsa yayi ba sai yaga dama yake yi

Ko kallon Hajiya Lubna dake ta tambayarshi ina za shi bai yi ba ya fice da sauri dan burinsa bai wuce ya gan shi agaban Mai gida ba

B'angaren Akram kuwa aranar Sam bai runtsa ba da tunaninsu Saiam ya kwana ko yaya ya juya sai ya hango Samha a idonsa tana ta kuka

Wajen k'arfe uku bacci yayi awon gaba dashi atake ya hau mafarki da Hajiya Nafeesa tana ta kuka tana ce mishi ya kular mata da yaranta kar wani Abu ya same su sai kuka take a mafarkin tana had'e hannyenta alamar rok'o

Da Sallati Akram ya farka daga baccin da yake yana ta mamakin Mafarkin da yayi

A hankali ya sauko da k'afarsa daga kan gado ya nufi band'aki dan ya d'aura alwala

Alhaji Bala a zaune yake agaban mai gida yabi ya had'a gumi yana ta kallon K'asan da mai gida yake bugawa shima sai had'a gumi yake sai da ya samu minti Ashirin yana buga k'asa yana gogewa yana kuma zana k'asa sai girgiza kai yake alaman Al amarin babba ne

Alhaji Bala kuwa duk ya matsu ya gaya mishi abinda yake faruwa

A hankali Mai gida ya d'ago tare da sharce gumin dake tsatsafo mishi a goshi ya kalli Alhaji Balan da jikinsa ke rawa dan shi kansa tunda yake bai tab'a ganin mai gida a irin wanan yanayin ba

Mai gida magana ya fara yi yana "Kura akwai matsala matsalar ma kuwa gagaruma dan wanan fad'a ne tsakanin matacce da rayayye matar nan da ka kashe spirit d'inta na da k'arfi sosai wlh haka zata tayi ta bibiyarka har sai ka zamto kamar mahaukaci ka fito duniya ka fad'i hallayenka da kanka da irin sana'ar da kake yi kafin ta rabu dakai kayi kuskure daka bari jininta ya tab'aka"

Hankali a tashe Alhaji Bala yace "mai gida kamar ya jininta ya tab'ani kana nufin babu abinda zaka iya yi akai"?

" emana jininta ya tab'aka ai sabida hular kanta ta cire ta saka a kirjinta sai da ya jike da jini ta jefo ma a fuska ko ba ayi haka ba"?

Da sauri Alhaji Bala yace "anyi haka wlh na d'auka taurin zuciya yasa ta jefo min hular ta ni kuwa na k'arasa kasheta na shiga uku na lalace mai gida yanzu mai abun yi dan Allah ka taimaka min dan ni Dana San matar nan haka take wlh da ban soma ma kasheta ba da iya shegun zan d'ebo na fito"

Alhaji Bala yace cikin rawar murya

Mai gida ajiyar zuciya ya sauke yace "Abu biyu zaka iya yi ta rabu dakai na d'aya ka koma gidan ka d'auko wanan hular nata ka kona shi na biyu kaje gidan ka durk'usa agaban mijinta da yaranta kace su yafe maka idan sun yafe maka to zata rabu dakai amma idan kuwa acikin biyun nan ba'ayi d'aya ba to ni kam babu abinda zan iya yi akai kuma Abubuwa na dab da jagule maka ga rashin kwanciyar hankali da zakayi ta fama dashi"

Hankalin Alhaji Bala idan yayi dubu ya kai kololuwa wajen tashi a firgice ya mik'e yana "mai gida kasan mai kake cewa kuwa ta ina zan iya samo hular da ta cire?ta yaya zan koma gidan a matsayina na Wanda ya kasheta haba maigida ya zaka fad'i abinda ba zai yiwu ba"

Mai gida ce mishi yayi to "iya abinda na duba kenan Wanda zaka yi ta rabu dakai amma bayan shi babu abinda zaka iya yi akai amma dai zan baka wasu Abubuwa idan ka dace ba zata ringa zuwar maka ba"

Da sauri Alhaji Bala ya zauna yana "dan Allah ka taimakeni matar nan ta firgitani har tsirara nayi agaban 'yata bansani ba"

Mai gida wani kwarya ya d'auko Wanda aka nannad'e da jajayen k'yalaye ya mik'a mishi yana

" idan ka tashi ka warware wanan Jan k'yallen ka daura akan goshinka da k'afarka akwai wani kullin magani guda biyu a ciki bak'in jikawa zaka yi ka shafa a jikinka gabad'aya wari ne dashi kamar kashi amma haka zaka d'aure idan gari ya waye sai ka wanke

D'ayan kuma turara d'akinka zaka yi dashi kafin ka kwanta bacci"

Hannu yasa ya d'auko Wasu jajjayen candles ya kuma mik'a mishi yana " ka kashe wutan d'akinka sai ka kunna candles d'in idan dai kaga tazo maka bayan kayi abubuwan nan to babu abinda zan iya yi akai face dai zabin farkon Dana baka"

Alhaji Bala da Sauri yace "insha Allahu ma ba zata kuma zuwar min ba indai nayi yanda kace"

Mai gida girgiza kansa kawai yayi bai ce komai ba ahaka Alhaji Bala ya ajiye mishi makud'an kud'i ya tafi...........
[2:36PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫

*Written by*
馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝

*A heart touching story*

庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_

#[email protected]
*#IG PML WRITERS*
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com
Chapter 12 · 0% Book details