Sashe 28
Babana Da Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Itace ta fara fita da motarta yana bayanta, tafiya suke akan titi hankalinta na gunsu, yanda ya biyota abaya ya tuna mata da Deedah, Allah ya jiqan Deedah ta faďa a hankali.
Tana isowa kai tsaye office ďinta ta nufa shima bai kulataba yayi nasa office da little....
Haka rayuwarsu ta cigabada tafiya tsawon shekara ďaya kenan Iman ta kasa tsaida xuciyarta akansu, Dr Merah yayi iya qoqarinsa akanta taqi sai ya xuba mata ido yana kallonta yasan komai daren daďewa dole xata xabi ďaya acikinsu Sa'eed ko Deen ta aura.
Shaquwa ta musamman ta shiga tsakanin little, fauxie da baffa, akoda yaushe suna can sun maidashi kakansu shi kansa yana jin daďin kasancewa tare dasu badan komai ba dan shima ba yara ba jikoki daga shi sai masu yi masa aiki sai Deen Idan yana gidan bai fita aiki ba.
A yanda ta lura yaran a ynxu sunfi son xama da baffa akan ta, bata yaye little ba yana shekara ďaya da wata biyar idan ka ganshi xakayi tsammanin ya tasamma shekara biyu saboda girmansa da wayonsa ko ina xuwa yake gashi da rigima sosai, sau tari ba'a gidan suke kwana ba sai inda baffa, yanda suke sonsa yasanyata qaunar tsohon itama akai akai take xuwa gaidashi ta daukeshi da girma haka take ganinsa Kamar mahaifinta kamar yanda ya ďauketa ya',
Idan tayi ba dai dai ba yakan xaunar da Ita yayi mata faďa Kamar yanda xaiyiwa Deen, haka duk wani abu daya shige mata duhu na rayuwa shike warware mata, sai ta daukesa tabashi wani matsayi a xuciyarta na UBA, a Yanxu tana samun kulawar da bata samu a baya, ga yaranta suna jin daďin kasancewa dashi ba abinda xata cewa wannan tsohon bayan yi masa addua a tsawon rayuwarta.
A nata ganin Sa'eed yafi dacewa da aurenta, yafi kowa sanin halinta da mijinta sannan tasan halinsa fiye da halin Deen, miskilancin Deen kesa take qinsa komai yana yinsa cikin nuna isa da gadara, ta tambayi Dr Merah xabi acikinsu ya xaba mata Dr Deen Wanda Sam bata amince da wannan xabin ba, sai taje ga baffa tana tsammanin xaice ta auri yaronsa Deen ga mamakinta sai ji tayi yace,
'fatyma ki auri Wanda xuciyarki tafi amince maki dashi, Wanda kike gani yafi kusanci gareki inda hankalinki xaifi kwanciya kiyi xaman aure, ki kuma kula da yarannan guda biyu da suke amana agareki,
Sai taji kunyarsa da nauyinsa, akwai kawaici a gareta baxata iya fitowa ta gayamasa Sa'eed xuciyarta tafi aminta da ta aura ba, sai ta kawar da mgnr ta ďauko wani xancen suka cigaba da hira kamar ya' da uba....
Akwai wani lokaci da lauyoyin babanta dana Deedah suka xo gareta domin dukiyar mamanta dake hannunsu suna so su rabu da Ita,
Tayi mamakin dukiyar da Deedah ya bari, bar mgnr Waďanda ke cikin account ďinsa, bata taba sanin yanada irin waďanna kuďin ba, sai ta boye mamakinta lokacin da taga dukiyar baba, kusan tsoro da ruďewa tayi a inda take xaune,
Files files dake xube a gabanta na kamfani, gidajensa, filaye da shagunansa bata san iya Karsu ba, ga makullayen motocin da aka xube mata a qalla xasu kai ashirin inma basu haura hakan ba, anan gida ma tanajin makullan motarsa dake hannunta sun kai bakwai, na Deedah biyar ne Kuma tasan suka ďai ne motocinsa a duniya Gashi kuma taga xahiri sai ta qara yarda da mijinta akan babanta,
Ta dubi Sa'eed kafin ta maida dubanta ga Deen domin sune shaidarta sai lauyoyin, idanunta sukayi rau bakinta har rawa yake kamar xatayi kuka data tuna Deedah,
'Dukiyar Deedah na yafewa ďan mu Ahmed, ku shaidane ko bayan mutuwata idan ya girma xaku iya bashi, in kuma ina raye Alhamdulillah,
'sai dukiyar baba a raba biyu dani da qanwata, a ajiye mata nata daban, Acikin nawa xan sallami yan uwanmu da duka ma'aikatan gidan nan, sauran kuďin xn kaisu gidan marayu da asibiti saboda masu buqata, xan gina masa makarantar islamiya shida Deedah domin lada ta kai garesu Allah ya gafarta masu,
'banajin xn iyacin dukiyar baba koda kwandalace a ynxu danasan da jinin mahaifiyata da yayyuna da qannena aka tara wannan dukiyar, kuka take sosai
'Allah ya gafartawa baba, Allah ka yafewa baba, Allah ka yafe kuskurensa daya aikata,
Suka amsa da Amin suna kallonta cikin tausayawa....ta tsurawa dukiyar ido, xuciyarta ta taushe ta dacewa,
'duniya ba komai bace tamkar matafiyi ne akan tafarki, baba kaďai ya isheta misali, Waye baisan baba a Nigeria ba shahararren ďan siyasa mai ji da dukiya, a yau yana ina? ya tafi yabar kuďin a inda ya samesu, ya tafi inda abinda ka shuka shine jarinka, bai tafi da gidajen ba bai tafi da motocin ba, bai tafi qasashen da yake xuwa ba, qarqashin qasa ya tafi cikin yadin likkafani dai dai dana kowa, babu AC babu katifa mai taushi, sauran al'amarin tsakaninsa da ubangijinsa ne, to haka kowa fa xai mutu yabar wannan dukiyar dayake taqama da Ita, dukiyar nan da ake tarawa ana hana talakawa da masu buqata, dukiyar da ake kashe bayin Allah saboda ita, dukiyarda xaka ga yan uwa suna faďa suna gaba saboda ita, duk xa'a mutu abarta Allah ya gafartamana Amin.
2 months later ~~~
Tana xaune a falo cikin Atampha mai qarshen tsada, kanta babu kallabi ta matse gashinta a tsakiyar kanta, farin glass dake idanunta ya qara ma fuskarta ilhami da kwarjini tana naxarin wani littafin ilimin halin ďan adam Wanda a fakaice ba komai bane aciki ba sai applied Christianity, malaman kimiyar halin ďan adam ke amfani dashi jami'oi matsayin hanyoyin gyara mu'amalar xamantakewar ďan adam tana tsintar na tsinta tana xubar dana xubarwa, sunan littafin 'The power of positive thinking'.
Da Sallama ya shiga falon ya bayyana cikin kyakkyawar suit (Japanese) da baqin gilashin Prada a idanunshi, falon ya gauraye da qamshin Dior addict daka ganshi kaga gogaggen ďan boko.
Kallo ďaya tayi masa taji xuciyarta ta buga a yau, kamar yau tafara ganinsa, bawai yau ta fara ganinsa ba sai dai bata fiye yiwa mutum kyakyawan kallo ba, yau ta ganshine sosai a gabanta yayi mata kyau, shima gabansane ya faďi sakamakon ganin Iman yau a ainihinta ba cikin mayafi da labcoat ba kamar kullum,
Ta lalubi ďan kwalinta ta ďaura ta xare gilashin idanunta tayi mishi barka da xuwa,
Shiru ya ratsa na wani daqiqai wani chemistry mai ban mamaki na aiki a zuciyoyinsu da kwayoyin idanunsu yana shiga cikin xukatansu dai dai lokacin fauxie ta shigo da gudu da ball a hannunta little na biye da Ita yana kuka akan tabashi taqi sai dariya take masa,
Suna ganin Dr Deen duk sukayi kansa suka rungumesa suna dariya,
'ďanki kike hanawa ball fauxie, bakiji kunya ba yana kuka yana biye dake,
Ta soma dariya tana kallonsa kafin ta bawa little ball ďin,
'amma shine ya jefomin ita a goshi ina assignment,
'Kiyi haquri kidaina sashi kuka kinji,
Little ya dubesa yana gauranci da alama ya kawo qarar fauxie ne, daga shi har Iman suka kwashe da dariya yanda yake Mgnr komai baxaka fahimta aciki ba amma yanayin fuskarsa xaka gane da faďa yake Mgnr, Deen ya rarrashesa haďe da bashi ball ďin ya fice da gudu,
'yaya yau xakaje damu inda baffa,
'kujirani a waje gani fitowa ynxu sai muje, ta fita da gudu itama,
Deen ya dubeta wannan karon ba walwala a fuskarsa,
'inason nasan matsayina a gunki fatyma,
'Sa'eed na xaba, shi nake ganin yafi kowa sanina da halin dana fuskanta a baya, nasanshi ya sanni,
Ya dubeta da tsananin mamaki,
'kina tunanin har akwai wani abu daya shafi rayuwarki a baya wanda ban sani ba, fiye da shekara muna tare kina nufin bakisan hali na bakisan ko waye niba, ban taba roqon mace ta soni ba sai akan ki Iman, kinsan yawan matan dake bibiyata domin na auresu naqi saboda kece a xuciyata Kuma baffa yafi amincewa dake, mecece ribar aurenki da mai mata kije masa da qanwarki da yaronki....
'Acikin yan matan dake bibiyarka ka xabi ďaya ka aura Dr Deen, qanwata da yarona ko bada aure ba xn iya Kula dasu domin Nafison rayuwarsu akan tawa Nafison farin cikinsu akan nawa,
Wannan Karon ya harzuqa and he mean it, ya haqura da Iman a ynxu bai taba rarrashin mace ko roqonta akan taso Shiba sai akanta kuma take wulaqantashi, duk girmansa da ajinsa,
'Na tabbata ďan halak fatyma, kije gaki ga Sa'eed, ya tashi ya fice batare daya qara kallonta ba,
Nan take taji xuciyarta ta buga tabisa da kallo kada dai ya haqura da itane?
Daga inda take xaune tana jinsa yana kiran little akan yaxo su tafi,
She knows it Dr Deen yana sonta, kuma shi yafi dacewa data aura, shine baida mata shi kaďai xai iya riqe yaranta ba tsangwama gashi yaran sunyi sabo sosai da baffa, amma Sa'eed fa?
Shima yana sonta shima xai iya riqa yaranta haka shima yana buqatar kulawar Mace tunda bai samu agurin matar saba.....
Har dare yaran basu dawo ba tasan baxai wuce acan xasu kwana ba, ita a ynxu yaye little xatayi ta huta tunda dama bai damu dashan mamma ba, idan ba Ita ta matseshi tabashi ba baxai nema ba yanacin abincinsa sosai ga bakinsa ya saba dacin daďi kamar irin na fauxie duk kalar kwalama xaka Deen ya siyo ya kawowa yaran harma Sa'eed.
Kwana biyu bata qara sanya Deen a ido ba ko a asibiti sun daina haďuwa, ya daina kiranta a waya sai tayi qoqarin kiransa sai ta fasa kada dai da gaske yake ya haqura da ita,
A xahirin damuwarta a ynxu Iman na wani hali na soyayya, Wanda ita kanta batasan cewar soyayyar ce ke dawainiya da xuciyarta ba, soyayyar Dr Deen Wanda a halin ynxu batasan halin da yake ciki ba, ita dashi sai gani a nesa ko idan yaxo maida little shima daga gate,
Soyayyarsa a xuciyarta sai qara linkuwa take Kamar ana iza wuta, ta tuna ranar rabuwarsu ta qarshe,
_'Na tabbata ďan halak fatyma kije gaki ga Sa'eed._
Tana isowa kai tsaye office ďinta ta nufa shima bai kulataba yayi nasa office da little....
Haka rayuwarsu ta cigabada tafiya tsawon shekara ďaya kenan Iman ta kasa tsaida xuciyarta akansu, Dr Merah yayi iya qoqarinsa akanta taqi sai ya xuba mata ido yana kallonta yasan komai daren daďewa dole xata xabi ďaya acikinsu Sa'eed ko Deen ta aura.
Shaquwa ta musamman ta shiga tsakanin little, fauxie da baffa, akoda yaushe suna can sun maidashi kakansu shi kansa yana jin daďin kasancewa tare dasu badan komai ba dan shima ba yara ba jikoki daga shi sai masu yi masa aiki sai Deen Idan yana gidan bai fita aiki ba.
A yanda ta lura yaran a ynxu sunfi son xama da baffa akan ta, bata yaye little ba yana shekara ďaya da wata biyar idan ka ganshi xakayi tsammanin ya tasamma shekara biyu saboda girmansa da wayonsa ko ina xuwa yake gashi da rigima sosai, sau tari ba'a gidan suke kwana ba sai inda baffa, yanda suke sonsa yasanyata qaunar tsohon itama akai akai take xuwa gaidashi ta daukeshi da girma haka take ganinsa Kamar mahaifinta kamar yanda ya ďauketa ya',
Idan tayi ba dai dai ba yakan xaunar da Ita yayi mata faďa Kamar yanda xaiyiwa Deen, haka duk wani abu daya shige mata duhu na rayuwa shike warware mata, sai ta daukesa tabashi wani matsayi a xuciyarta na UBA, a Yanxu tana samun kulawar da bata samu a baya, ga yaranta suna jin daďin kasancewa dashi ba abinda xata cewa wannan tsohon bayan yi masa addua a tsawon rayuwarta.
A nata ganin Sa'eed yafi dacewa da aurenta, yafi kowa sanin halinta da mijinta sannan tasan halinsa fiye da halin Deen, miskilancin Deen kesa take qinsa komai yana yinsa cikin nuna isa da gadara, ta tambayi Dr Merah xabi acikinsu ya xaba mata Dr Deen Wanda Sam bata amince da wannan xabin ba, sai taje ga baffa tana tsammanin xaice ta auri yaronsa Deen ga mamakinta sai ji tayi yace,
'fatyma ki auri Wanda xuciyarki tafi amince maki dashi, Wanda kike gani yafi kusanci gareki inda hankalinki xaifi kwanciya kiyi xaman aure, ki kuma kula da yarannan guda biyu da suke amana agareki,
Sai taji kunyarsa da nauyinsa, akwai kawaici a gareta baxata iya fitowa ta gayamasa Sa'eed xuciyarta tafi aminta da ta aura ba, sai ta kawar da mgnr ta ďauko wani xancen suka cigaba da hira kamar ya' da uba....
Akwai wani lokaci da lauyoyin babanta dana Deedah suka xo gareta domin dukiyar mamanta dake hannunsu suna so su rabu da Ita,
Tayi mamakin dukiyar da Deedah ya bari, bar mgnr Waďanda ke cikin account ďinsa, bata taba sanin yanada irin waďanna kuďin ba, sai ta boye mamakinta lokacin da taga dukiyar baba, kusan tsoro da ruďewa tayi a inda take xaune,
Files files dake xube a gabanta na kamfani, gidajensa, filaye da shagunansa bata san iya Karsu ba, ga makullayen motocin da aka xube mata a qalla xasu kai ashirin inma basu haura hakan ba, anan gida ma tanajin makullan motarsa dake hannunta sun kai bakwai, na Deedah biyar ne Kuma tasan suka ďai ne motocinsa a duniya Gashi kuma taga xahiri sai ta qara yarda da mijinta akan babanta,
Ta dubi Sa'eed kafin ta maida dubanta ga Deen domin sune shaidarta sai lauyoyin, idanunta sukayi rau bakinta har rawa yake kamar xatayi kuka data tuna Deedah,
'Dukiyar Deedah na yafewa ďan mu Ahmed, ku shaidane ko bayan mutuwata idan ya girma xaku iya bashi, in kuma ina raye Alhamdulillah,
'sai dukiyar baba a raba biyu dani da qanwata, a ajiye mata nata daban, Acikin nawa xan sallami yan uwanmu da duka ma'aikatan gidan nan, sauran kuďin xn kaisu gidan marayu da asibiti saboda masu buqata, xan gina masa makarantar islamiya shida Deedah domin lada ta kai garesu Allah ya gafarta masu,
'banajin xn iyacin dukiyar baba koda kwandalace a ynxu danasan da jinin mahaifiyata da yayyuna da qannena aka tara wannan dukiyar, kuka take sosai
'Allah ya gafartawa baba, Allah ka yafewa baba, Allah ka yafe kuskurensa daya aikata,
Suka amsa da Amin suna kallonta cikin tausayawa....ta tsurawa dukiyar ido, xuciyarta ta taushe ta dacewa,
'duniya ba komai bace tamkar matafiyi ne akan tafarki, baba kaďai ya isheta misali, Waye baisan baba a Nigeria ba shahararren ďan siyasa mai ji da dukiya, a yau yana ina? ya tafi yabar kuďin a inda ya samesu, ya tafi inda abinda ka shuka shine jarinka, bai tafi da gidajen ba bai tafi da motocin ba, bai tafi qasashen da yake xuwa ba, qarqashin qasa ya tafi cikin yadin likkafani dai dai dana kowa, babu AC babu katifa mai taushi, sauran al'amarin tsakaninsa da ubangijinsa ne, to haka kowa fa xai mutu yabar wannan dukiyar dayake taqama da Ita, dukiyar nan da ake tarawa ana hana talakawa da masu buqata, dukiyar da ake kashe bayin Allah saboda ita, dukiyarda xaka ga yan uwa suna faďa suna gaba saboda ita, duk xa'a mutu abarta Allah ya gafartamana Amin.
2 months later ~~~
Tana xaune a falo cikin Atampha mai qarshen tsada, kanta babu kallabi ta matse gashinta a tsakiyar kanta, farin glass dake idanunta ya qara ma fuskarta ilhami da kwarjini tana naxarin wani littafin ilimin halin ďan adam Wanda a fakaice ba komai bane aciki ba sai applied Christianity, malaman kimiyar halin ďan adam ke amfani dashi jami'oi matsayin hanyoyin gyara mu'amalar xamantakewar ďan adam tana tsintar na tsinta tana xubar dana xubarwa, sunan littafin 'The power of positive thinking'.
Da Sallama ya shiga falon ya bayyana cikin kyakkyawar suit (Japanese) da baqin gilashin Prada a idanunshi, falon ya gauraye da qamshin Dior addict daka ganshi kaga gogaggen ďan boko.
Kallo ďaya tayi masa taji xuciyarta ta buga a yau, kamar yau tafara ganinsa, bawai yau ta fara ganinsa ba sai dai bata fiye yiwa mutum kyakyawan kallo ba, yau ta ganshine sosai a gabanta yayi mata kyau, shima gabansane ya faďi sakamakon ganin Iman yau a ainihinta ba cikin mayafi da labcoat ba kamar kullum,
Ta lalubi ďan kwalinta ta ďaura ta xare gilashin idanunta tayi mishi barka da xuwa,
Shiru ya ratsa na wani daqiqai wani chemistry mai ban mamaki na aiki a zuciyoyinsu da kwayoyin idanunsu yana shiga cikin xukatansu dai dai lokacin fauxie ta shigo da gudu da ball a hannunta little na biye da Ita yana kuka akan tabashi taqi sai dariya take masa,
Suna ganin Dr Deen duk sukayi kansa suka rungumesa suna dariya,
'ďanki kike hanawa ball fauxie, bakiji kunya ba yana kuka yana biye dake,
Ta soma dariya tana kallonsa kafin ta bawa little ball ďin,
'amma shine ya jefomin ita a goshi ina assignment,
'Kiyi haquri kidaina sashi kuka kinji,
Little ya dubesa yana gauranci da alama ya kawo qarar fauxie ne, daga shi har Iman suka kwashe da dariya yanda yake Mgnr komai baxaka fahimta aciki ba amma yanayin fuskarsa xaka gane da faďa yake Mgnr, Deen ya rarrashesa haďe da bashi ball ďin ya fice da gudu,
'yaya yau xakaje damu inda baffa,
'kujirani a waje gani fitowa ynxu sai muje, ta fita da gudu itama,
Deen ya dubeta wannan karon ba walwala a fuskarsa,
'inason nasan matsayina a gunki fatyma,
'Sa'eed na xaba, shi nake ganin yafi kowa sanina da halin dana fuskanta a baya, nasanshi ya sanni,
Ya dubeta da tsananin mamaki,
'kina tunanin har akwai wani abu daya shafi rayuwarki a baya wanda ban sani ba, fiye da shekara muna tare kina nufin bakisan hali na bakisan ko waye niba, ban taba roqon mace ta soni ba sai akan ki Iman, kinsan yawan matan dake bibiyata domin na auresu naqi saboda kece a xuciyata Kuma baffa yafi amincewa dake, mecece ribar aurenki da mai mata kije masa da qanwarki da yaronki....
'Acikin yan matan dake bibiyarka ka xabi ďaya ka aura Dr Deen, qanwata da yarona ko bada aure ba xn iya Kula dasu domin Nafison rayuwarsu akan tawa Nafison farin cikinsu akan nawa,
Wannan Karon ya harzuqa and he mean it, ya haqura da Iman a ynxu bai taba rarrashin mace ko roqonta akan taso Shiba sai akanta kuma take wulaqantashi, duk girmansa da ajinsa,
'Na tabbata ďan halak fatyma, kije gaki ga Sa'eed, ya tashi ya fice batare daya qara kallonta ba,
Nan take taji xuciyarta ta buga tabisa da kallo kada dai ya haqura da itane?
Daga inda take xaune tana jinsa yana kiran little akan yaxo su tafi,
She knows it Dr Deen yana sonta, kuma shi yafi dacewa data aura, shine baida mata shi kaďai xai iya riqe yaranta ba tsangwama gashi yaran sunyi sabo sosai da baffa, amma Sa'eed fa?
Shima yana sonta shima xai iya riqa yaranta haka shima yana buqatar kulawar Mace tunda bai samu agurin matar saba.....
Har dare yaran basu dawo ba tasan baxai wuce acan xasu kwana ba, ita a ynxu yaye little xatayi ta huta tunda dama bai damu dashan mamma ba, idan ba Ita ta matseshi tabashi ba baxai nema ba yanacin abincinsa sosai ga bakinsa ya saba dacin daďi kamar irin na fauxie duk kalar kwalama xaka Deen ya siyo ya kawowa yaran harma Sa'eed.
Kwana biyu bata qara sanya Deen a ido ba ko a asibiti sun daina haďuwa, ya daina kiranta a waya sai tayi qoqarin kiransa sai ta fasa kada dai da gaske yake ya haqura da ita,
A xahirin damuwarta a ynxu Iman na wani hali na soyayya, Wanda ita kanta batasan cewar soyayyar ce ke dawainiya da xuciyarta ba, soyayyar Dr Deen Wanda a halin ynxu batasan halin da yake ciki ba, ita dashi sai gani a nesa ko idan yaxo maida little shima daga gate,
Soyayyarsa a xuciyarta sai qara linkuwa take Kamar ana iza wuta, ta tuna ranar rabuwarsu ta qarshe,
_'Na tabbata ďan halak fatyma kije gaki ga Sa'eed._