Sashe 35
Angon Mata Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta ciro kudi masu yawa ta bashi ta sallameshi, ta tafi da hoton scanning na baby tana kallo tana jin farin ciki, koda ta dawo gida ta nunawa Don amsa yai yana kallo saiya jefar dashi
"Wannan ba jini na bane"
Ta kalleshi cikin fushi "to jinin waye ne?"
Kallanta yai sai ya ji ta bashi tausayi, tsayawa yai a gabanta ya dafe hannayensa a kafadunta
"Ki yi hakuri na cutar dake na baki maganin hana daukar ciki, ina me baki hakuri kuma wallahi na yi nadama yanzu ina son yara, yara rahamane ban san haka ba sai akan Leemat, ko kallanta nai farin ciki nake ji, kuma sai yanzu nasan darajar diya mace, yanzu babu macen da zan iya yin zina da ita saboda ina da ya mace, amma Haseena ba zan boye miki ba baki da ciki"
Haseena janyewa tai daga hannun daya dora mata a kan kafada "karka kara ce min banda ciki, gaskiya zamu sami babban matsala da kai, kuma meyasa baka bawa Aisha maganin hana daukar cikin ba sai ni da baka son hada zuri'a dani"
"Wallahi na bawa Aisha kuma tasha akan idona, kawai Allah ne ya yi ikonsa ya gwada min ban fishi dibara ba, sannan insha Allah Haseena ba zan kara ce miki baki da ciki ba, Allah ya sauke ki lafiya"
Bai kara ce mata komai ba ya juya ya fice ta bishi da harara
Aunty Rasheeda ta yi iya kokarinta akan Aisha don kuwa ta yi mata odan kayan mata daga wurin M JARUMA, Aisha kuwa babu wasa, shan maganin take kamar hauka don tana son mijinta ya jita zakwai, kuma ta yi matsi sosai, ta kara kyau, komai nata tsaf tsaf
Ranar da Aisha zata koma gida Aunty Rasheeda da Aunty Zainab suka zo, shima Namijin duniya ya karaso sai zumudi yake yi kamar wani sabon ango
Aisha ta tare a sabon gida, bangarenta ya hadu matuka, a bangarenta daga babban falo sai dakuna guda biyu da bayikansu a ciki, sai dining da kitchen, hakama bangaren Haseena
Ammi dasu Aunty Rasheeda sai da suka kai har dare kafin suka tafi gidajensu, Aisha ta rage daga Haseena sai Leemat a daki, Aisha sai kallan Leemat take yi da take bacci, smile take yi ta shiga shafa kanta
"My Baby ke ce rayuwata, zan iya komai a kanki, hatta rayuwata zan iya badawa saboda ke, da numfashina babu wanda zai cutar dake"
Haseena ce ta bankado kofa ta shigo rike da wuka, a rikice Aisha ta tashi zaune tana kallanta, muryar Aisha na rawa ta ce Aunty Haseena me zaki yi da wuka?
Haseena fuskarta a murkude ta shiga fadin "yarki zan kashe, ba zan jure ganinta tana numfashi ba a duniya, na tsane ta"
Aisha sauka tai daga kan gadon tana kallan Haseena cikin tsoro "na yarda ki kashe ni amma ban yarda ki taba lafiyar yata ba"
Haseena ta ce nike bakya gabana damuwa yarki
Aisha ta tsorata sai ta fashe da kuka "me yata tai miki, me ta sani, bata san komai ba wannan ai rashin imani ne, ki yi min duk abinda zaki yi min amma banda yata"
"Ba zan tsaya bata lokaci ba dole Leemat yau tabar duniya"
Haseena ta shiga nufo kan gadon, hankalin Aisha ya tashi, tsoro ne ya fita daga idonta bata san lokacin da wani karfi ya zo mata ba, tunkarar Haseena tai ta tureta, wukar ya fadi kasa, Aisha tai maza ta dauki wukar, Haseena ta zaro ido tana kallanta
"Ina wasa dake ko ni sa'arki ce, maza ko bani wukar nan"
Aisha ta kalleta cikin tsananin tsana gami da nuna ta da wukar "kafin ki kashe min yarinya ni zan fara kashe ki"
Haseena cikin fushi ta ce don ubanki ni zaki kashe, nafi karfinki wallahi tai kan Aisha ta jata da kokawa wukar ya fadi gefe, Aisha wani karfi ya kara shigarta, kokawa suke yi sosai, suna kaiwa juna duka ta ko'ina, sanadiyar haka Leemat ta farka tana tsala ihu sai Aisha ta barke da kuka zuciyarta ta kara karfi, wani wawan duka ta kaiwa Haseena a ciki, ta cigaba da kaiwa Haseena duka Haseena ta shiga ihu, ta yi nasarar kai Haseena kasa, ta hau ruwan cikinta ta fara koda mata mari tana nushin bakinta da hancinta, Haseena sai ihu take yi tana neman tallafi, Aisha itama kuka take yi, hawaye da majina sun dabaibaye mata fuska fadi take Haseena saina kasheki kafin ki kashe min yata
Don yana parking motarsa a motor park ya shiga ciki, ihun Haseena ya shiga juyowa yana fitowa daga bangaren Aisha, da sauri ya je domin ya ga meke faruwa
Aisha sai data galabaitar da Haseena, ta farfasa mata hanci da baki, jini sai zuba yake yi sannan ta dauki wukar da Haseena ta shigo dashi ta daga zata cakawa Haseena
"Aisha miye haka, kisa zaki yi?"
Aisha ta juya ta kalli Don da ya shigo a rikice
"Babu ruwanka, ka cire kanka, yau babu wanda zai hanani kashe Haseena"
Haseena ganin Don yasa ta fara fadin "don Allah ka taimake ni karta kashe ni"
Don fa yaga da gaske Aisha take yi, kasa yai da murya cikin laluma ya ce Aishata ban sanki da gardama ba kuma ban sanki da taurin kai ba, please ki aje wukar nan don Allah kuma don soyayyarki ga manzon Allah SAW
Wani irin kuka Aisha ta saki me matukar taba zuciya sai ta jefar da wukar ta tashi daga ruwan cikin Haseena ta fada kan gado ta cigaba da kuka, Leemat na tayata kuka, Haseena ta mike da sauri ta shiga magana cikin muryar kuka "kenan da baka zo ba shikenan kashe ni zata yi?"
Don ya kalleta cikin jin haushi "meya kawoki bangarenta, bangarenki ne?"
"Yanzu hanani zuwa bangaren Aisha zaka yi bayan dani da ita duk daya ne, kallan yar uwata nake mata"
karasawa yai wurin su Aisha ya dauki Leemat ya shiga rarrashinta, Haseena ji tai kamar ta mutu, kallan Aisha dake ta faman kuka yai
"Aisha tashi ki fada min meya hadaki da Haseena"
Aisha bata tanka shi ba ta cigaba da kukanta, Haseena ta ce idan ta fada maka me zaka yi, shigar mata fadar zaka yi sai ka rama mata, eh lallai kana ta kara tabbatar min da kafi son Aisha a kaina to baka nemi zaman lafiya ba?
Don ya mike a fusace "wallahi Haseena idan baki yi hankali dani ba saina nada miki na jaki"
Galla masa harara tai sannan ta ce koma miye ne ka fadawa matarka ba zan taba yafe mata jinin data zubar min ba, sai na dau fansa
Tana gama fada ta juya ta fice Don ya bita da kallo cike da takaici sannan ya dawo kan Aisha
"Please wifey ki yi hakuri ki tashi kiba Leemat nono tana ta kuka"
Aisha ta tashi ta zauna ta amshi Leemat ta fito da nono ta shiga bata amma taki kallan Don bare ma tai masa magana
"Aisha fushi kike yi dani, ni kuma miye laifina?"
Banza tai dashi tana kuka tana bawa Leemat nono tana kallan fuskarta, tausayinta kawai take ji tana tunanin yadda zata cigaba da zama da Haseena a gida daya tana son daukar ran yarta
Don ya kama kai ya yi shuru yana tunani
Leemat tasha nono me isanta, bacci ya dauketa, saita kwantar da ita, ta yi hanyar bayi Don ya rike mata hannu "Aisha ina son magana dake, bana son ina miki magana kina banza dani kin jini ko"
Dawowa tai ta zauna bakin gado batare data kalleshi ba
"Aisha meya hadaki fada da Haseena har ya kawo kina son ki kashe ta"
Fashewa da kuka Aisha tai ta kalleshi "ni ba zan zauna a gidan nan ba, ka fitar dani idan ba haka ba Haseena zata kashe min Leemat"
"Aisha idan har zan fahimci zancenki Haseena tazo ne da niyyar ta kashe Leemat"
Aisha bata ce masa komai ba sai kuka, idanun Don sunyi jawur rike Aisha yai a rikice ya shiga girgiza ta "ki fada min Haseena tazo kashe min yata ne?"
Aisha ta shiga magana cikin muryar kuka "ni ba zan iya fada maka komai ba, kawai ka fitar dani ni da yata daga nan gidan, bana son abinda zai taba lafiyar yata Leemat"
Cikin tsananin fushi Don ya mike ya fice daga dakin Aisha ta cigaba da kuka
Haseena tsaye cikin dakinta gaban mirrow, kallan kanta take yi jikin madubin cikin tsananin bacin rai
"Yau Aisha ce ta yi min duka kamar karamar yarinya, ba zai yu ba saina rama"
Don ne ya karaso kofar dakin Haseena ya shiga bibbiga kofar dakin, hankalin Haseena ya kai kan biga kofar, sarai tasan Don ne, sai tai banza dashi ta shiga bayi
Don cikin fushi ya cigaba da bibbiga kofar kamar zai balla "Haseena ki bude kofar" shuru yake ji "na ce ki bude kofar ko"
Harta fito wanka bibbiga kofar yake yi, zira kayan bachcinta tai ta kwanta
Don ya ce sai dai idan ba zaki fito ba, wallahi saina miki abinda ban taba yi miki ba
Ta tabe baki ta gyara kwanciyar ta
Aisha hakura tai ta kwanta tana kallan babynta, Don ya shigo ya zauna bakin gado ya kama kai cikin tsananin bacin rai, Aisha ta kula da halin da mijinta yake ciki, tashi tai ta zauna tana kallanshi, sai ta dafa hannunta a bayanshi
"Mijina ka zo ka kwanta"
Don ya girgiza kai alamun a'a "ba zan iya bacci ba, Haseena ta gama bata min rai"
Aisha ta rungume shi ta baya, ta kai kanta ta wuyarsa "yi hakuri, ka manta da ita kawai, kar kai fushi da ita"
Don ya juyo ya kalleta "Aisha meyasa zuciyarki keda taushi, kina da rauni, ki rage wannan tausayin naki, bana so"
Aisha ta ce hakuri ne kawai, ni ban dauki duniyar a bakin komai ba
Don ya ce Haseena fa yarmu tazo kashewa, ki yi tunanin haka
"To ka dai yi hakuri bana son ganinka cikin damuwa nima zan iya shiga cikin damuwa"
"To shikenan" tashi yai ya shiga tube kayansa, ita dai sai binsa da kallo take yi, bayan ya gama cire kayan ya wuce bayi, sai ta kwanta ta shiga tunani
"Wannan ba jini na bane"
Ta kalleshi cikin fushi "to jinin waye ne?"
Kallanta yai sai ya ji ta bashi tausayi, tsayawa yai a gabanta ya dafe hannayensa a kafadunta
"Ki yi hakuri na cutar dake na baki maganin hana daukar ciki, ina me baki hakuri kuma wallahi na yi nadama yanzu ina son yara, yara rahamane ban san haka ba sai akan Leemat, ko kallanta nai farin ciki nake ji, kuma sai yanzu nasan darajar diya mace, yanzu babu macen da zan iya yin zina da ita saboda ina da ya mace, amma Haseena ba zan boye miki ba baki da ciki"
Haseena janyewa tai daga hannun daya dora mata a kan kafada "karka kara ce min banda ciki, gaskiya zamu sami babban matsala da kai, kuma meyasa baka bawa Aisha maganin hana daukar cikin ba sai ni da baka son hada zuri'a dani"
"Wallahi na bawa Aisha kuma tasha akan idona, kawai Allah ne ya yi ikonsa ya gwada min ban fishi dibara ba, sannan insha Allah Haseena ba zan kara ce miki baki da ciki ba, Allah ya sauke ki lafiya"
Bai kara ce mata komai ba ya juya ya fice ta bishi da harara
Aunty Rasheeda ta yi iya kokarinta akan Aisha don kuwa ta yi mata odan kayan mata daga wurin M JARUMA, Aisha kuwa babu wasa, shan maganin take kamar hauka don tana son mijinta ya jita zakwai, kuma ta yi matsi sosai, ta kara kyau, komai nata tsaf tsaf
Ranar da Aisha zata koma gida Aunty Rasheeda da Aunty Zainab suka zo, shima Namijin duniya ya karaso sai zumudi yake yi kamar wani sabon ango
Aisha ta tare a sabon gida, bangarenta ya hadu matuka, a bangarenta daga babban falo sai dakuna guda biyu da bayikansu a ciki, sai dining da kitchen, hakama bangaren Haseena
Ammi dasu Aunty Rasheeda sai da suka kai har dare kafin suka tafi gidajensu, Aisha ta rage daga Haseena sai Leemat a daki, Aisha sai kallan Leemat take yi da take bacci, smile take yi ta shiga shafa kanta
"My Baby ke ce rayuwata, zan iya komai a kanki, hatta rayuwata zan iya badawa saboda ke, da numfashina babu wanda zai cutar dake"
Haseena ce ta bankado kofa ta shigo rike da wuka, a rikice Aisha ta tashi zaune tana kallanta, muryar Aisha na rawa ta ce Aunty Haseena me zaki yi da wuka?
Haseena fuskarta a murkude ta shiga fadin "yarki zan kashe, ba zan jure ganinta tana numfashi ba a duniya, na tsane ta"
Aisha sauka tai daga kan gadon tana kallan Haseena cikin tsoro "na yarda ki kashe ni amma ban yarda ki taba lafiyar yata ba"
Haseena ta ce nike bakya gabana damuwa yarki
Aisha ta tsorata sai ta fashe da kuka "me yata tai miki, me ta sani, bata san komai ba wannan ai rashin imani ne, ki yi min duk abinda zaki yi min amma banda yata"
"Ba zan tsaya bata lokaci ba dole Leemat yau tabar duniya"
Haseena ta shiga nufo kan gadon, hankalin Aisha ya tashi, tsoro ne ya fita daga idonta bata san lokacin da wani karfi ya zo mata ba, tunkarar Haseena tai ta tureta, wukar ya fadi kasa, Aisha tai maza ta dauki wukar, Haseena ta zaro ido tana kallanta
"Ina wasa dake ko ni sa'arki ce, maza ko bani wukar nan"
Aisha ta kalleta cikin tsananin tsana gami da nuna ta da wukar "kafin ki kashe min yarinya ni zan fara kashe ki"
Haseena cikin fushi ta ce don ubanki ni zaki kashe, nafi karfinki wallahi tai kan Aisha ta jata da kokawa wukar ya fadi gefe, Aisha wani karfi ya kara shigarta, kokawa suke yi sosai, suna kaiwa juna duka ta ko'ina, sanadiyar haka Leemat ta farka tana tsala ihu sai Aisha ta barke da kuka zuciyarta ta kara karfi, wani wawan duka ta kaiwa Haseena a ciki, ta cigaba da kaiwa Haseena duka Haseena ta shiga ihu, ta yi nasarar kai Haseena kasa, ta hau ruwan cikinta ta fara koda mata mari tana nushin bakinta da hancinta, Haseena sai ihu take yi tana neman tallafi, Aisha itama kuka take yi, hawaye da majina sun dabaibaye mata fuska fadi take Haseena saina kasheki kafin ki kashe min yata
Don yana parking motarsa a motor park ya shiga ciki, ihun Haseena ya shiga juyowa yana fitowa daga bangaren Aisha, da sauri ya je domin ya ga meke faruwa
Aisha sai data galabaitar da Haseena, ta farfasa mata hanci da baki, jini sai zuba yake yi sannan ta dauki wukar da Haseena ta shigo dashi ta daga zata cakawa Haseena
"Aisha miye haka, kisa zaki yi?"
Aisha ta juya ta kalli Don da ya shigo a rikice
"Babu ruwanka, ka cire kanka, yau babu wanda zai hanani kashe Haseena"
Haseena ganin Don yasa ta fara fadin "don Allah ka taimake ni karta kashe ni"
Don fa yaga da gaske Aisha take yi, kasa yai da murya cikin laluma ya ce Aishata ban sanki da gardama ba kuma ban sanki da taurin kai ba, please ki aje wukar nan don Allah kuma don soyayyarki ga manzon Allah SAW
Wani irin kuka Aisha ta saki me matukar taba zuciya sai ta jefar da wukar ta tashi daga ruwan cikin Haseena ta fada kan gado ta cigaba da kuka, Leemat na tayata kuka, Haseena ta mike da sauri ta shiga magana cikin muryar kuka "kenan da baka zo ba shikenan kashe ni zata yi?"
Don ya kalleta cikin jin haushi "meya kawoki bangarenta, bangarenki ne?"
"Yanzu hanani zuwa bangaren Aisha zaka yi bayan dani da ita duk daya ne, kallan yar uwata nake mata"
karasawa yai wurin su Aisha ya dauki Leemat ya shiga rarrashinta, Haseena ji tai kamar ta mutu, kallan Aisha dake ta faman kuka yai
"Aisha tashi ki fada min meya hadaki da Haseena"
Aisha bata tanka shi ba ta cigaba da kukanta, Haseena ta ce idan ta fada maka me zaka yi, shigar mata fadar zaka yi sai ka rama mata, eh lallai kana ta kara tabbatar min da kafi son Aisha a kaina to baka nemi zaman lafiya ba?
Don ya mike a fusace "wallahi Haseena idan baki yi hankali dani ba saina nada miki na jaki"
Galla masa harara tai sannan ta ce koma miye ne ka fadawa matarka ba zan taba yafe mata jinin data zubar min ba, sai na dau fansa
Tana gama fada ta juya ta fice Don ya bita da kallo cike da takaici sannan ya dawo kan Aisha
"Please wifey ki yi hakuri ki tashi kiba Leemat nono tana ta kuka"
Aisha ta tashi ta zauna ta amshi Leemat ta fito da nono ta shiga bata amma taki kallan Don bare ma tai masa magana
"Aisha fushi kike yi dani, ni kuma miye laifina?"
Banza tai dashi tana kuka tana bawa Leemat nono tana kallan fuskarta, tausayinta kawai take ji tana tunanin yadda zata cigaba da zama da Haseena a gida daya tana son daukar ran yarta
Don ya kama kai ya yi shuru yana tunani
Leemat tasha nono me isanta, bacci ya dauketa, saita kwantar da ita, ta yi hanyar bayi Don ya rike mata hannu "Aisha ina son magana dake, bana son ina miki magana kina banza dani kin jini ko"
Dawowa tai ta zauna bakin gado batare data kalleshi ba
"Aisha meya hadaki fada da Haseena har ya kawo kina son ki kashe ta"
Fashewa da kuka Aisha tai ta kalleshi "ni ba zan zauna a gidan nan ba, ka fitar dani idan ba haka ba Haseena zata kashe min Leemat"
"Aisha idan har zan fahimci zancenki Haseena tazo ne da niyyar ta kashe Leemat"
Aisha bata ce masa komai ba sai kuka, idanun Don sunyi jawur rike Aisha yai a rikice ya shiga girgiza ta "ki fada min Haseena tazo kashe min yata ne?"
Aisha ta shiga magana cikin muryar kuka "ni ba zan iya fada maka komai ba, kawai ka fitar dani ni da yata daga nan gidan, bana son abinda zai taba lafiyar yata Leemat"
Cikin tsananin fushi Don ya mike ya fice daga dakin Aisha ta cigaba da kuka
Haseena tsaye cikin dakinta gaban mirrow, kallan kanta take yi jikin madubin cikin tsananin bacin rai
"Yau Aisha ce ta yi min duka kamar karamar yarinya, ba zai yu ba saina rama"
Don ne ya karaso kofar dakin Haseena ya shiga bibbiga kofar dakin, hankalin Haseena ya kai kan biga kofar, sarai tasan Don ne, sai tai banza dashi ta shiga bayi
Don cikin fushi ya cigaba da bibbiga kofar kamar zai balla "Haseena ki bude kofar" shuru yake ji "na ce ki bude kofar ko"
Harta fito wanka bibbiga kofar yake yi, zira kayan bachcinta tai ta kwanta
Don ya ce sai dai idan ba zaki fito ba, wallahi saina miki abinda ban taba yi miki ba
Ta tabe baki ta gyara kwanciyar ta
Aisha hakura tai ta kwanta tana kallan babynta, Don ya shigo ya zauna bakin gado ya kama kai cikin tsananin bacin rai, Aisha ta kula da halin da mijinta yake ciki, tashi tai ta zauna tana kallanshi, sai ta dafa hannunta a bayanshi
"Mijina ka zo ka kwanta"
Don ya girgiza kai alamun a'a "ba zan iya bacci ba, Haseena ta gama bata min rai"
Aisha ta rungume shi ta baya, ta kai kanta ta wuyarsa "yi hakuri, ka manta da ita kawai, kar kai fushi da ita"
Don ya juyo ya kalleta "Aisha meyasa zuciyarki keda taushi, kina da rauni, ki rage wannan tausayin naki, bana so"
Aisha ta ce hakuri ne kawai, ni ban dauki duniyar a bakin komai ba
Don ya ce Haseena fa yarmu tazo kashewa, ki yi tunanin haka
"To ka dai yi hakuri bana son ganinka cikin damuwa nima zan iya shiga cikin damuwa"
"To shikenan" tashi yai ya shiga tube kayansa, ita dai sai binsa da kallo take yi, bayan ya gama cire kayan ya wuce bayi, sai ta kwanta ta shiga tunani