Sashe 12
Angon Mata Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To dan ubanki baki isa ki haifi wannan cikin ba da raina a duniya, da kaina zan zubar dashi"
Haseena ta ja hannun Aisha da karfi suka fuce, gida suka dawo, Haseena ta yi parking a harabar gida, ta fito a fusace, Aisha na fitowa Haseena ta kai mata wani wawan mari da da ya yi sanadiyar ta fadi kasa, ta fara kuka
"Aunty ki yi hakuri"
"Don ubanki waya ce ki yi ciki a gidan nan?"
Cikin muryar kuka Aisha ta ce Aunty ba laifina bane Ya Umar shiya biyoni daki ya yi min ciki
Haseena ta kara kai mata wani duka
"Wallahi sai cikin nan ya bare yau"
Aisha tasa hannu ta kare cikinta tana kuka "Aunty ki barni da cikina, ki yi min komai amma karki taba min cikina"
Haseena ta daga kafarta zata bigawa cikin sai ta dakata sanadiyar bude Gate da Security suka yi alamun mota zai shugo, Haseena ta yi sauri ta daga Aisha
"Yer uwata yi hakuri kin ji, kar ki yi fushi"
Mota kirar Land cruised prado ya shugo harabar gidan, Haseena ta rungume Aisha tana rarrashinta
"Zaki sanu lafiya, kin ji yer uwata"
Aisha ta shiga manajin munafurci irin na Haseena
Abba da Ammi ne suka fito daga motar, Aisha na ganinsu ta janye jikinta daga na Haseena ta je rungume Ammi tana kuka
Ammi da Abba suka rikice gabadaya, Haseena ta shiga gaida su, basu bi ta kan gaisuwarsu ba suka fara tambayar meke faruwa
"Bata da lafiya yanzu muka dawo daga asibity"
Ammi da Abba suka zaro ido "meke damunta" suka fada a tare
Haseena shuru ta yi wani bakin ciki na cinta a rai, ganin bata basu amsa ba yasa Ammi ta fara duba Aisha, ta duba idanunta da tafin hannunta, ta kalli Abba, gaban Haseena sai faduwa yake yi
"Kamar Aisha nada ciki"
Wani farin ciki ya baiyana a fuskar Abba, Haseena ji ta yi kamar ta kwarmatsa ihu, Aisha ta rike cikinta kam kam kamar za'a kwace mata ta kara fashewa da kuka
Ammi ta Jawota jikinta "yata yanzu cikin kikewa kuka?"
"Ammi don Allah kar a rabani da Baby na, ina son Baby na sosai"
Ammi tai murmushi "wa zai rabaki da Bebinki, wani ya fada miki za'a rabaki da Bebinki, duk wanda ya taba Bebinki ya taba mu ne, ba za mu kyale mutum ba
Haseena ta hadiye miyau dakyar ta ce muje ciki ku zauna ko?
Abba ya ce ai ba sai mun shiga ciki ba, tunda komai lafiya kawai zamu wuce
Aisha ta kankame Ammi tana kara kuka, Ammi ta kalli Abba
"Ina ga mu tafi da Aisha gida, Jikina bai bani lafiya ba"
Haseena ta yi sauri ta ce "yanzu in kun tafi da ita, ai ni ba zan iya zama a gidan ba ni kadai, tunda shi baya nan"
Aisha ta kara kankame Ammi, Ammi ta yi wa Haseena wani kallo "Aisha ba za ta zauna a gidan nan ba, idan ba za ki iya zama ba, zaki iya binmu"
Haseena zuciyarta ta yi wani suya kamar ta je ta shake wuyar Ammi amma ta jure "to bari naje na hada kayana mu tafi"
Ammi ta kalli Aisha "to kema muje ki hada kayanki mu tafi"
Duk suka shiga ciki suka bar Abba tsaye a harabar gida
Haseena data shugo dakinta, safa da marwa ta shiga yi, gumi na keto mata
"Ba zaiyuhuba dole na dauki mataki, ba zan taba yarda a haife wannan cikin ba, da naga ranar haihuwar cikin nan gwara naga ranar mutuwata, zan bi kowani hanya koda kuwa na halaka ne na hana haihuwarsa"
Ta janyo akwatinta ta shiga jera kayanta
Aisha da Ammi a dakin Aisha, Aisha jikinta na rawa tana hada kayanta a akwati
Ammi ta kira sunanta, ta waigo ta kalli Ammin "naam"
"Me ke faruwa a gidan nan? Alamu sun nuna akwai matsala"
Aisha ta tuno fuskar Haseena, ta girgiza kai da sauri "A'a Ammi babu abinda ke faruwa"
"Karki boye min komai, tabbas akwai matsala"
"Babu komai Ammi"
"Waya ce zai rabaki da Bebinki"
Aisha ta yi tsuru tana kallan Ammi
"Aisha daure ki fada min komai, Aisha ta kara ganin fuskar Haseena tana harararta
"Ammi babu komai, kawai ina jin tsoro ne kada a raba ni da Bebinki"
Ammi ta yi shuru tana kallanta "to shikenan gama hada kayan mu wuce, Aisha ta cigaba da hada kaya jiki na rawa Ammi na taya ta
Bayan duk sun gama suka fito suka samu Abba tsaye yana jiransu, ma'aikatan gidan suka shigar da akwatunan bayan mota sannan duk suka shiga motan, Direba ya jasu suka bar gidan,
Da isowansu Ammi ta nunawa Haseena dakin da zata sauka, ita kuwa Aisha dakin Ammi Ammi ta sauke ta, ai kuwa ta yi farin ciki sosai,
Abba ya kira likita domin tabbatar da cikin Aisha, a gwaje gwajen likitan ya tabbatar da tana dauke da juna biyu, amma bata samun isashshen abinci kuma jininta ya yi kasa sosai
Hankalin Ammi da Abba duk ya tashi, nan take Ammi tasa ma'aikatan gidan su shiga girka nau'ikan abinci masu Karin jini duk saboda Aisha, Aisha ta fara ganin wani irin gata kamar za'a cinye ta
Don ya sakko daga fushin da ya yi, tunanin Aisha da kewarta su suka cika masa zuciya, har ya fara jin ba zai iya kara kwana daya ba batare da ya ji dumin jikinta ba, dakyar dai Wizzy ya shawo kansa akan ya bari gobe sai su taho
Haseena tsaye a can saman bene, wani wurin shakatawa ne a wurin, har Swimming pool, ta yi nisa tana tunanin yadda zata warware matsalarta, can ta tuno wata hatsabibiyar kawarta,
"Yes, Bilki ke ce zaki iya warware min matsala ta"
wayarta ta shiga lallatsawa ta kira Bilki, bugawa daya Bilkisu ta amsa
Haseena ta zaiyanowa Bilkisu damuwarta, Bilkisu ta bata shawara akan akwai wani hatsabibin boka shine zai iya lallata cikin Aisha kuma ya mallaka mata Don, suka ajje magana akan gobe zasu hadu su tafi wurin bokan
Bilkisu tana katse wayan ta yi dariya "ji shashasha mara hankali"
Aisha kwance kan gadon Ammi sai murmushi take yi tana shafa karamin cikinta
"Nakosa Abbanka ya dawo, ina kewarsa, ina kallan farin cikin da zai yi idan ya dawo"
Ta cigaba da shafar cikinta tana yer murmushi Ammi ta shugo da shayi a hannun ta, ta zauna gefen gado, Aisha ta tashi zaune tanawa Ammi murmushi
"Ga shayi kisha"
Aisha ta amsa "nagode" sannan ta fara sha a hankali, Ammi na kallanta cikin farin ciki
Washegari da sassafe su Don suka biyo jirgi suka dawo Abuja, Don gidanshi ya taho direct burinsa kawai ya yi gamo da Aisha, ya shiga falo yana kiran sunanta amma shuru, dakin Aisha ya shiga ya tsaya yana kallan dakin, ya je ya bude durowanta ya ga babu kayan ta, hankalinsa ya yi mugun tashi, ya fita da sauri ya je dakin Haseena, nanma shuru, itama ya bude durowanta amma babu kaya
"To meya faru bayan tafiyata"
Wayarsa ya shiga lallatsawa ya kira Haseena
Ta bangaran Haseena tana zaune bakin gado tana shirye shiryen haduwa da Haseena sai wayanta ya hau ringing, ganin Don yake kiranta yasa da sauri ta mike ta amsa jikinta na rawa
"Hello mijina"
"Ina kuka je?"
"Ka dawo ne?"
"Ba wannan na tambayeki ba"
"Ina kike kuma ina Aisha?"
"Muna family house, Abba da Ammi suka zo suka dauke mu jiya"
Sai ya yi wani ajiyar zuciya, ya yanke wayan "Allah nagode maka, amma meyasa su Abba suka dauke su, bari dai naje can gidan na ji kome ya faru"
Aisha zaune ita kadai a falo tana shan ice cream, Haseena ta shugo, Aisha tana ganin Haseena sai tsoro ya kamata, Haseena ta hango Ammi na sakkowa daga matakalan bene, sai ta yi kamar bata ganta ba, ta fara yiwa Aisha fada
"Haba sister, ya zaki dinga shan ice cream a halin da kike ciki, so kike ki haifa mana yaro da mura, daga yau kada na kara ganinki kina shan abu me sanyi"
Ta amshe robar Ice cream din daga hannun Aisha, dai dai da karasowar Ammi, Ammi sosai ta ji dadi a zuciyarta, tai murmushi ta ce Aisha gaskiya Haseena take fada miki, shan abu me sanyi ba naki bane Yanzu, Aisha bata ce komai ba, Haseena ta zauna gefen Aisha ta dan jawota jikinta, Aisha jikinta sai rawa yake yi
"Ki kwantar da hankalinki, Oga zai dawo"
Ammi tai murmushi ta zauna tana kallansu, sai Yanzu zuciyar Ammi ta sake da Haseena, ta kuma godewa Allah daya bawa danta mataye na gari
Duk kallansu ya koma wurin Don, da Yanzu ya shugo, Aisha ta mike da sauri wani farin ciki ya baiyana a fuskarta, Haseena da sauri ta je ta rungume shi, Ammi itama farin ciki ya cika ta, Don ya shafa bayan Haseena amma kallansa na kan Aisha
Aisha ta ce sannu da dawowa, ya danyi murmushi "yauwa" ya kalli Ammi "sannu Ammi ina wuni"
"Lafiya lau Umar, ya hanya?"
"Lafiya lau"
Ya banbare Haseena daga jikinsa "Baby mu je ko"
Suka je suka zauna, Ammi ta ce a zuciyarta daga ganin Haseena bata da kunya, tunda zata iya rungume Dana a gabana
Don ya kalli Aisha sosai sannan ya kalli Ammi "Aisha bata da lafiya nr"
Tai murmushi "meka gani?"
"Ta rame min sosai, kuma ta yi fari"
Haseena ta ce kada wanda ya fada masa, nice kawai zan fada masa komai, zan yi masa albishir sai ya bani tukuici
Don ya kalleta "to fada min meke faruwa?
Tai masa murmushi "ba Yanzu ba, saika samo min tukuici"
Don ya koma ga Ammi ganin Haseena na son bata masa lokaci
"Ammi ke ki fada min"
Ammi ta ce tunda Haseena ta ce kada kowa ya fada ita ce zata fada to ai shikenan saika samo mata tukuici
Don ya kalli Aisha yana murmushi "nasan ke ba za ki kunyata ni ba, fada min meke faruwa"
Aisha ta rufe fuskarta tsananin kunya tana murmushi
Don ya kalli Ammi "kin ga irin kunyar Aisha ko, kullum zaluntata take yi, Ammi ki yi mata fada"
Ammi tai murmushi "to Umar ai kunya yana da kyau, kuma yau da gobe zata zo ta sake"
Haseena ta ce hakane Ammi
Haseena ta ja hannun Aisha da karfi suka fuce, gida suka dawo, Haseena ta yi parking a harabar gida, ta fito a fusace, Aisha na fitowa Haseena ta kai mata wani wawan mari da da ya yi sanadiyar ta fadi kasa, ta fara kuka
"Aunty ki yi hakuri"
"Don ubanki waya ce ki yi ciki a gidan nan?"
Cikin muryar kuka Aisha ta ce Aunty ba laifina bane Ya Umar shiya biyoni daki ya yi min ciki
Haseena ta kara kai mata wani duka
"Wallahi sai cikin nan ya bare yau"
Aisha tasa hannu ta kare cikinta tana kuka "Aunty ki barni da cikina, ki yi min komai amma karki taba min cikina"
Haseena ta daga kafarta zata bigawa cikin sai ta dakata sanadiyar bude Gate da Security suka yi alamun mota zai shugo, Haseena ta yi sauri ta daga Aisha
"Yer uwata yi hakuri kin ji, kar ki yi fushi"
Mota kirar Land cruised prado ya shugo harabar gidan, Haseena ta rungume Aisha tana rarrashinta
"Zaki sanu lafiya, kin ji yer uwata"
Aisha ta shiga manajin munafurci irin na Haseena
Abba da Ammi ne suka fito daga motar, Aisha na ganinsu ta janye jikinta daga na Haseena ta je rungume Ammi tana kuka
Ammi da Abba suka rikice gabadaya, Haseena ta shiga gaida su, basu bi ta kan gaisuwarsu ba suka fara tambayar meke faruwa
"Bata da lafiya yanzu muka dawo daga asibity"
Ammi da Abba suka zaro ido "meke damunta" suka fada a tare
Haseena shuru ta yi wani bakin ciki na cinta a rai, ganin bata basu amsa ba yasa Ammi ta fara duba Aisha, ta duba idanunta da tafin hannunta, ta kalli Abba, gaban Haseena sai faduwa yake yi
"Kamar Aisha nada ciki"
Wani farin ciki ya baiyana a fuskar Abba, Haseena ji ta yi kamar ta kwarmatsa ihu, Aisha ta rike cikinta kam kam kamar za'a kwace mata ta kara fashewa da kuka
Ammi ta Jawota jikinta "yata yanzu cikin kikewa kuka?"
"Ammi don Allah kar a rabani da Baby na, ina son Baby na sosai"
Ammi tai murmushi "wa zai rabaki da Bebinki, wani ya fada miki za'a rabaki da Bebinki, duk wanda ya taba Bebinki ya taba mu ne, ba za mu kyale mutum ba
Haseena ta hadiye miyau dakyar ta ce muje ciki ku zauna ko?
Abba ya ce ai ba sai mun shiga ciki ba, tunda komai lafiya kawai zamu wuce
Aisha ta kankame Ammi tana kara kuka, Ammi ta kalli Abba
"Ina ga mu tafi da Aisha gida, Jikina bai bani lafiya ba"
Haseena ta yi sauri ta ce "yanzu in kun tafi da ita, ai ni ba zan iya zama a gidan ba ni kadai, tunda shi baya nan"
Aisha ta kara kankame Ammi, Ammi ta yi wa Haseena wani kallo "Aisha ba za ta zauna a gidan nan ba, idan ba za ki iya zama ba, zaki iya binmu"
Haseena zuciyarta ta yi wani suya kamar ta je ta shake wuyar Ammi amma ta jure "to bari naje na hada kayana mu tafi"
Ammi ta kalli Aisha "to kema muje ki hada kayanki mu tafi"
Duk suka shiga ciki suka bar Abba tsaye a harabar gida
Haseena data shugo dakinta, safa da marwa ta shiga yi, gumi na keto mata
"Ba zaiyuhuba dole na dauki mataki, ba zan taba yarda a haife wannan cikin ba, da naga ranar haihuwar cikin nan gwara naga ranar mutuwata, zan bi kowani hanya koda kuwa na halaka ne na hana haihuwarsa"
Ta janyo akwatinta ta shiga jera kayanta
Aisha da Ammi a dakin Aisha, Aisha jikinta na rawa tana hada kayanta a akwati
Ammi ta kira sunanta, ta waigo ta kalli Ammin "naam"
"Me ke faruwa a gidan nan? Alamu sun nuna akwai matsala"
Aisha ta tuno fuskar Haseena, ta girgiza kai da sauri "A'a Ammi babu abinda ke faruwa"
"Karki boye min komai, tabbas akwai matsala"
"Babu komai Ammi"
"Waya ce zai rabaki da Bebinki"
Aisha ta yi tsuru tana kallan Ammi
"Aisha daure ki fada min komai, Aisha ta kara ganin fuskar Haseena tana harararta
"Ammi babu komai, kawai ina jin tsoro ne kada a raba ni da Bebinki"
Ammi ta yi shuru tana kallanta "to shikenan gama hada kayan mu wuce, Aisha ta cigaba da hada kaya jiki na rawa Ammi na taya ta
Bayan duk sun gama suka fito suka samu Abba tsaye yana jiransu, ma'aikatan gidan suka shigar da akwatunan bayan mota sannan duk suka shiga motan, Direba ya jasu suka bar gidan,
Da isowansu Ammi ta nunawa Haseena dakin da zata sauka, ita kuwa Aisha dakin Ammi Ammi ta sauke ta, ai kuwa ta yi farin ciki sosai,
Abba ya kira likita domin tabbatar da cikin Aisha, a gwaje gwajen likitan ya tabbatar da tana dauke da juna biyu, amma bata samun isashshen abinci kuma jininta ya yi kasa sosai
Hankalin Ammi da Abba duk ya tashi, nan take Ammi tasa ma'aikatan gidan su shiga girka nau'ikan abinci masu Karin jini duk saboda Aisha, Aisha ta fara ganin wani irin gata kamar za'a cinye ta
Don ya sakko daga fushin da ya yi, tunanin Aisha da kewarta su suka cika masa zuciya, har ya fara jin ba zai iya kara kwana daya ba batare da ya ji dumin jikinta ba, dakyar dai Wizzy ya shawo kansa akan ya bari gobe sai su taho
Haseena tsaye a can saman bene, wani wurin shakatawa ne a wurin, har Swimming pool, ta yi nisa tana tunanin yadda zata warware matsalarta, can ta tuno wata hatsabibiyar kawarta,
"Yes, Bilki ke ce zaki iya warware min matsala ta"
wayarta ta shiga lallatsawa ta kira Bilki, bugawa daya Bilkisu ta amsa
Haseena ta zaiyanowa Bilkisu damuwarta, Bilkisu ta bata shawara akan akwai wani hatsabibin boka shine zai iya lallata cikin Aisha kuma ya mallaka mata Don, suka ajje magana akan gobe zasu hadu su tafi wurin bokan
Bilkisu tana katse wayan ta yi dariya "ji shashasha mara hankali"
Aisha kwance kan gadon Ammi sai murmushi take yi tana shafa karamin cikinta
"Nakosa Abbanka ya dawo, ina kewarsa, ina kallan farin cikin da zai yi idan ya dawo"
Ta cigaba da shafar cikinta tana yer murmushi Ammi ta shugo da shayi a hannun ta, ta zauna gefen gado, Aisha ta tashi zaune tanawa Ammi murmushi
"Ga shayi kisha"
Aisha ta amsa "nagode" sannan ta fara sha a hankali, Ammi na kallanta cikin farin ciki
Washegari da sassafe su Don suka biyo jirgi suka dawo Abuja, Don gidanshi ya taho direct burinsa kawai ya yi gamo da Aisha, ya shiga falo yana kiran sunanta amma shuru, dakin Aisha ya shiga ya tsaya yana kallan dakin, ya je ya bude durowanta ya ga babu kayan ta, hankalinsa ya yi mugun tashi, ya fita da sauri ya je dakin Haseena, nanma shuru, itama ya bude durowanta amma babu kaya
"To meya faru bayan tafiyata"
Wayarsa ya shiga lallatsawa ya kira Haseena
Ta bangaran Haseena tana zaune bakin gado tana shirye shiryen haduwa da Haseena sai wayanta ya hau ringing, ganin Don yake kiranta yasa da sauri ta mike ta amsa jikinta na rawa
"Hello mijina"
"Ina kuka je?"
"Ka dawo ne?"
"Ba wannan na tambayeki ba"
"Ina kike kuma ina Aisha?"
"Muna family house, Abba da Ammi suka zo suka dauke mu jiya"
Sai ya yi wani ajiyar zuciya, ya yanke wayan "Allah nagode maka, amma meyasa su Abba suka dauke su, bari dai naje can gidan na ji kome ya faru"
Aisha zaune ita kadai a falo tana shan ice cream, Haseena ta shugo, Aisha tana ganin Haseena sai tsoro ya kamata, Haseena ta hango Ammi na sakkowa daga matakalan bene, sai ta yi kamar bata ganta ba, ta fara yiwa Aisha fada
"Haba sister, ya zaki dinga shan ice cream a halin da kike ciki, so kike ki haifa mana yaro da mura, daga yau kada na kara ganinki kina shan abu me sanyi"
Ta amshe robar Ice cream din daga hannun Aisha, dai dai da karasowar Ammi, Ammi sosai ta ji dadi a zuciyarta, tai murmushi ta ce Aisha gaskiya Haseena take fada miki, shan abu me sanyi ba naki bane Yanzu, Aisha bata ce komai ba, Haseena ta zauna gefen Aisha ta dan jawota jikinta, Aisha jikinta sai rawa yake yi
"Ki kwantar da hankalinki, Oga zai dawo"
Ammi tai murmushi ta zauna tana kallansu, sai Yanzu zuciyar Ammi ta sake da Haseena, ta kuma godewa Allah daya bawa danta mataye na gari
Duk kallansu ya koma wurin Don, da Yanzu ya shugo, Aisha ta mike da sauri wani farin ciki ya baiyana a fuskarta, Haseena da sauri ta je ta rungume shi, Ammi itama farin ciki ya cika ta, Don ya shafa bayan Haseena amma kallansa na kan Aisha
Aisha ta ce sannu da dawowa, ya danyi murmushi "yauwa" ya kalli Ammi "sannu Ammi ina wuni"
"Lafiya lau Umar, ya hanya?"
"Lafiya lau"
Ya banbare Haseena daga jikinsa "Baby mu je ko"
Suka je suka zauna, Ammi ta ce a zuciyarta daga ganin Haseena bata da kunya, tunda zata iya rungume Dana a gabana
Don ya kalli Aisha sosai sannan ya kalli Ammi "Aisha bata da lafiya nr"
Tai murmushi "meka gani?"
"Ta rame min sosai, kuma ta yi fari"
Haseena ta ce kada wanda ya fada masa, nice kawai zan fada masa komai, zan yi masa albishir sai ya bani tukuici
Don ya kalleta "to fada min meke faruwa?
Tai masa murmushi "ba Yanzu ba, saika samo min tukuici"
Don ya koma ga Ammi ganin Haseena na son bata masa lokaci
"Ammi ke ki fada min"
Ammi ta ce tunda Haseena ta ce kada kowa ya fada ita ce zata fada to ai shikenan saika samo mata tukuici
Don ya kalli Aisha yana murmushi "nasan ke ba za ki kunyata ni ba, fada min meke faruwa"
Aisha ta rufe fuskarta tsananin kunya tana murmushi
Don ya kalli Ammi "kin ga irin kunyar Aisha ko, kullum zaluntata take yi, Ammi ki yi mata fada"
Ammi tai murmushi "to Umar ai kunya yana da kyau, kuma yau da gobe zata zo ta sake"
Haseena ta ce hakane Ammi