Sashe 7
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To shikenan ai kin kyauta, ke baki da son jiki ba irin amal ba, amal bata son motsi nan da can koda yaushe tana nade akan gado kamar wata mage.."
'Yar dariya Hafsat tayi taci gaba da wanke wanken yayinda ita kuma hajiya kubra taci gaba da bata labari akan amal wannan yasa Hafsat sake fahimtar cewar ba karamin so hajiya kubra ke yiwa yar tata ba domin magana daya biyu sai ta sako zancen amal,
Tsaf Hafsat ta gyare kitchen din bayan ta kammala wanke wanken, falo suka koma suka zauna suka fara kallo atashar tauraron dan adam,
Wannan zaman da suka yi shine yabawa Hafsat damar sakin jiki sosai da hajiya kubra domin ta dan warware suna yin hira har tana bata labarin irin yanda rayuwarta ta gudana agidan marayu.....
_Fatan alkhairi ga masoya masu bibiyar labarin..!._
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*14*
aishaummi.blogspot.com
***Sosai hafsat ta sake da hajiya kubra domin hatta girkin rana tare suka yi suka shiryashi akan table saboda alhaji sa'id yana dawowa cin abinci daga office,
Har dare suna tare suna hira afalon alhaji sa'id wanda kusan rabin hirar ta amal ce, yauma kamar jiya atare suka fita ita da hajiya kubra suka yiwa alhaji sai da safe,
Yauma saida tayi karfin hali sannan tasamu bacci ya dauketa domin har lokacin tana kewar gidan marayu da kuma kewar kawarta amina,
Washe gari da safe suna kan table suna karyawa amal ta kira mahaifinta,nan hajiya kubra ta shiga murna domin bakinta yaki rufuwa,
Mikawa hajiya kubra wayar Alhaji sa'id yayi bayan sun kammala gaisawa shida amal din, cikin farin ciki hajiya kubra ta fara yiwa amal albishir na zuwan Hafsat gidan, Hafsat tana zaune tanaji bata dai jiyo abinda amal din taceba kawai dai taga hajiya kubra ta mika mata wayar tana fadin,
"To shikenan bari abata.."
Karbar wayar tayi ta kara akunnenta nan taji muryar amal din kamar zata fasa mata dodon kunne dan tsananin kara,
Tamkar dama sun san juna haka suka gaisa gamida yin sallama,
Cikin fara'a Alhaji sa'id ya mike domin fita adawo lafiya Hafsat tayi masa, zama tayi shiru bayan fitarsu shida hajiya kubra,tunani tafara aranta na yanda kowa agidan ke sonta da kaunarta tabbas ta yarda Allah shine kadirun ala man yasha'u domin ya sauya rayuwarta ya kuma juyata acikin lokaci kankani,
Yanzu kam ta warware sannan tagama sakewa da hajiya kubra, abu dayane kawai ke damunta shine kewar Amina tare da sauran jama'ar da ta dade da sani arayuwarta,
Haka dai ta rinka boye damuwarta taci gaba da zama tareda su hajiya kubra har tayi sati biyu agidan, kullum da daddare sai hajiya kubra ko Alhaji sa'id sun kira amal angaisa da ita, ita kuwa idan aka bata wayar domin su gaisa amal cewa take tana ta dokin ganinta saboda taji yanda su umminta ke zuzuta tsananin kamanninsu da Hafsat din,
Duk da cewar tana jin dadin zaman gidan kuma babu abinda ta nema tarasa amma hakan bai hanata shiga damuwa ba, tana yawan tuna rayuwarta ta baya wadda tayita acikin rashin gata da rashin galihu sannan uwa uba cikin maraici,wannan dalilin ne yasa take burin ta bada tata gudun mawar domin aganinta wannan wata damace ta samu wurin taimakon yan uwanta marayu,
Ganin kamar tana cikin damuwa yasa hajiya kubra tambayarta koda akwai abinda ke damunta, bata boye mata ba ta sanar mata da gaskiyar bukatarta na son zuwa kaiwa kawarta Amina wacce ke gidan Marayu ziyara,
"To ai duk wannan mai sauki ne Hafsat, idan kin shirya kiyi min magana sai insa driver yakaiki.."
"Toh Ummi nagode madalla Allah yasaka da alkhairi, Allah ya..."
Dakatar da ita hajiya kubra tayi,
"Bana son godiyar nan Hafsat, duk abinda nayi miki kaina nayiwa, yanzu me zaki kaiwa kawar taki?"
"Ummi girki kawai zanyi mata inkai mata domin wallahi hatta abinci wahala yake mana acan.."
"To shikenan gashi nan sai ki zabi abinda zaki dafa mata,duk abinda zaki bukata da akwai kuma kin san wurinda yake.."
Daga haka hajiya kubra ta juya tawuce cikin falo domin lokacin acikin kitchen suke Hafsat tana wanke wanke saboda sam bata son zama batare da tayi dan wani aiki ba,
Shinkafa da miyar kaji Hafsat ta dafawa Amina cikin manyan food flaks guda biyu, wanka tayi ta shirya cikin wata shaddar amal kalar ruwan toka,farin hijab tasa tafito ta iske hajiya kubra zaune tana karanta wani English novel,
"Hafsat anfito?"
"Ehh Ummi nashirya"
"To driver yana waje yana jiranki, yanzu idan kin tafi sai yaushe zaki dawo?"
"Ummi zan dan jima saboda kinga rabona da Amina an kwana biyu.."
"To shikenan sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya.."
"Amin" ta amsa tareda fita ta shiga kitchen ta debi girkin da tayiwa aminan tafita compound din gidan inda salisu driver yake jiranta,
Har wani nushadi takeji yau haka kawai saboda zataje taga Amina da sauran mutanen dake gidan marayun.
****
Tunda yusleem yaji mami tace masa anjanye maganar aurenshi shikenan yasaki jiki yayi watsi da maganar bai kara bi takanta ba amma ita mami abun yana nan aranta domin har yanzu kullum cikin tanadin kayan aurenshi take, duk inda taji ankawo kaya masu kyau ko masu tsada na mata sai ta siyo kuma zata nuna masa tace matarsa ta siyawa wacce zai auro nan gaba, shidai baya magana sai dai yayi shiru amma kuma shine zai biya kudin kayan da ta siyo wannan kam ko nawane baya shayin biya kuma bai taba musu ba,
Yauma hakance tafaru lokacin da ya shigo gidan ya isketa afalo ita da wata mata wacce ta Kawo mata kaya daga dubai, wasu dogayen riguna ne masu adon stones ajiki hadaddu,
Daga rigunan mami taci gaba dayi tana jujjuya su, bayan sallamar da yayi bai sake yin magana ba yasamu wuri ya zauna,
"Yusleem kaga rigunan nan daga dubai aka kawo kuma sunada kyau nayi sha'awarsu mutuka ko zaka siyawa matarka..?"
Yaji sarai abind mamin tace amma bai amsaba, kasancewar tasan halin abinta yasata daukar kala biyu, ja da kuma baka mai adon golden ajiki,
"Gashi na daukar maka guda biyu, duk guda daya 35 thousands ahakanma ragi tayi min amma bahaka take sayarwa ba.."
Gyada kai yayi har lokacin baice komai ba saboda shidai baiga amfanin kayan nan da mami ta dage taketa siya ba,
Saida mai kayan tatafi sannan yadubi mami wacce ke zaune har lokacin tana ta dudduba rigunan tana yaba kyawunsu,
"Wai mami dan Allah meye amfanin wadannan kayan da kiketa siye?"
"Amfaninsu? Amfaninsu kake tambaya? Kaifa mukayi dakai zaka nemo matar aure, ko kamanta? Ai zuba maka ido nayi ka gama zagaye zagayenka ka Kawo min wacce kakeso idan kuma hakan ya faskara to ni bazan gajiya ba wurin sake nemo maka wata.."
Shiru yayi ya lumshe manyan idanuwansa tareda jingina da jikin kujerar da yake zaune batare da yayi magana ba....
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*15*
***Lokacin da Hafsa takarasa gidan marayun ba karamin dadin ganinta Amina tajiba domin bata taba tsammanin sake yin tozali da itaba acikin rayuwarta,
Kebewa sukayi suka samu kasan wata bishiyar darbejiya suka zauna suka fara tattaunawa,
"Hafsa har kinyi kyau, ki ganki yanda kika sauya lokaci daya" Amina tace da Hafsat tana bin jikin Hafsat din da kallo,
"Amina kema insha Allah canji yana nan zuwar miki ai tunda mukayi hakuri da rayuwar da muka samu kanmu to da izinin Allah zamu dace da samun babban rabo.."
"Hmmm abar kaza dai kawai acikin gashinta hafsa, yawwa baki bani labarin yanda akayi ba rannan da kika tafi.."
Kwashewa duk yadda akayi hafsat tayi tafadawa amina da irin gatan da take samu yanzu,
Sun dade suna hira domin sai da la'asar liss sannan hafsat tatafi nan dinma kamar kada su rabu da amina saida hafsa tace ai zata rinka zuwa akai akai sannan hankalin amina ya kwanta.
Lokacin da hafsat takoma gida har alhaji sa'id yadawo daga office yana zaune a falon hajiya kubra shida ita bayan ya kammala cin abinci kasancewar yau bai dawo yin lunch ba,
Sallama tayi tashiga bayan sun amsa mata,
"Hafsa yau kuma ziyara aka kai?" Alhaji sa'id ya tambayeta yana murmushi,
"Ehh Abba" tabashi amsa,
"To ai yayi kyau, kin kyauta mutuka wannan ya nuna min cewa bazaki manta dasu ba duk abinda kika zama nan gaba"
"Ai da alama kam hafsat bazata manta dasu ba" hajiya kubra ta karbe zancen ta hanyar bawa alhajin amsa,
Zama hafsat tayi acikin falon tana sauraren hirar da su alhaji keyi wanda basu suka tashiba sai da sukaji anfara kiran sallar magrib.
Satin hafsat uku agidan amma kai idan kaganta zakace wata uku tayi domin tayi kiba tayi bul bul sosai, domin tana samun kulawa sosai daga iyayen rikon nata ga gata da suke nuna mata kamar sune suka haifeta,
Malamai guda biyu musamman alhaji sa'id ya daukosu domin su rinka koyar da ita karatun boko da na Arabic, sannan kuma yayi mata register a wata center ta mata wacce ake koyar da sana'o'i saboda tana son tasake samun kwarewa sosai akan sakar da ta iya,
Wadannan abubuwan da tasaka agaba sune suka saka bata da lokacin kanta yanzu koda yaushe tana da abinyi amma hakan bai hanata ware lokaci na ziyartar kawarta amina ba,
A fannin sakar ma tafi maida hankali domin hajiya kubra tafada mata cewar idan har ta gwanance to zata siyo mata keken saka kuma tanada shagon saida kayayyaki zata bata jari tafara saka kaya ana kaiwa shagon ana sayar mata wannan dalilin ne yasa ta bada himma sosai har ta samu kwarewa kamar yadda hajiya kubran keso,
Satinsu shida aka yayesu domin sun iya sosai, alkawarin da hajiya kubra ta daukar mata ta cika ta hanyar siyo mata keken saka harda sabuwar wayar hannu dambasheshiya mai kyau kirar kamfanin LG,
Murna wurin hafsa sai wanda yagani, samun keke da tayi sai yasake rike lokacin ta koda yaushe tana kai tana aiki acikin satittika kadan ta saka kaya masu yawan gaske, kayan sanyi na yara da towel da safa da hula,
Diban kayan akayi aka kai shagon hajiya kubra na kasuwa acikin satin aka Kawo kudin kayan domin har sun kare,
'Yar dariya Hafsat tayi taci gaba da wanke wanken yayinda ita kuma hajiya kubra taci gaba da bata labari akan amal wannan yasa Hafsat sake fahimtar cewar ba karamin so hajiya kubra ke yiwa yar tata ba domin magana daya biyu sai ta sako zancen amal,
Tsaf Hafsat ta gyare kitchen din bayan ta kammala wanke wanken, falo suka koma suka zauna suka fara kallo atashar tauraron dan adam,
Wannan zaman da suka yi shine yabawa Hafsat damar sakin jiki sosai da hajiya kubra domin ta dan warware suna yin hira har tana bata labarin irin yanda rayuwarta ta gudana agidan marayu.....
_Fatan alkhairi ga masoya masu bibiyar labarin..!._
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*14*
aishaummi.blogspot.com
***Sosai hafsat ta sake da hajiya kubra domin hatta girkin rana tare suka yi suka shiryashi akan table saboda alhaji sa'id yana dawowa cin abinci daga office,
Har dare suna tare suna hira afalon alhaji sa'id wanda kusan rabin hirar ta amal ce, yauma kamar jiya atare suka fita ita da hajiya kubra suka yiwa alhaji sai da safe,
Yauma saida tayi karfin hali sannan tasamu bacci ya dauketa domin har lokacin tana kewar gidan marayu da kuma kewar kawarta amina,
Washe gari da safe suna kan table suna karyawa amal ta kira mahaifinta,nan hajiya kubra ta shiga murna domin bakinta yaki rufuwa,
Mikawa hajiya kubra wayar Alhaji sa'id yayi bayan sun kammala gaisawa shida amal din, cikin farin ciki hajiya kubra ta fara yiwa amal albishir na zuwan Hafsat gidan, Hafsat tana zaune tanaji bata dai jiyo abinda amal din taceba kawai dai taga hajiya kubra ta mika mata wayar tana fadin,
"To shikenan bari abata.."
Karbar wayar tayi ta kara akunnenta nan taji muryar amal din kamar zata fasa mata dodon kunne dan tsananin kara,
Tamkar dama sun san juna haka suka gaisa gamida yin sallama,
Cikin fara'a Alhaji sa'id ya mike domin fita adawo lafiya Hafsat tayi masa, zama tayi shiru bayan fitarsu shida hajiya kubra,tunani tafara aranta na yanda kowa agidan ke sonta da kaunarta tabbas ta yarda Allah shine kadirun ala man yasha'u domin ya sauya rayuwarta ya kuma juyata acikin lokaci kankani,
Yanzu kam ta warware sannan tagama sakewa da hajiya kubra, abu dayane kawai ke damunta shine kewar Amina tare da sauran jama'ar da ta dade da sani arayuwarta,
Haka dai ta rinka boye damuwarta taci gaba da zama tareda su hajiya kubra har tayi sati biyu agidan, kullum da daddare sai hajiya kubra ko Alhaji sa'id sun kira amal angaisa da ita, ita kuwa idan aka bata wayar domin su gaisa amal cewa take tana ta dokin ganinta saboda taji yanda su umminta ke zuzuta tsananin kamanninsu da Hafsat din,
Duk da cewar tana jin dadin zaman gidan kuma babu abinda ta nema tarasa amma hakan bai hanata shiga damuwa ba, tana yawan tuna rayuwarta ta baya wadda tayita acikin rashin gata da rashin galihu sannan uwa uba cikin maraici,wannan dalilin ne yasa take burin ta bada tata gudun mawar domin aganinta wannan wata damace ta samu wurin taimakon yan uwanta marayu,
Ganin kamar tana cikin damuwa yasa hajiya kubra tambayarta koda akwai abinda ke damunta, bata boye mata ba ta sanar mata da gaskiyar bukatarta na son zuwa kaiwa kawarta Amina wacce ke gidan Marayu ziyara,
"To ai duk wannan mai sauki ne Hafsat, idan kin shirya kiyi min magana sai insa driver yakaiki.."
"Toh Ummi nagode madalla Allah yasaka da alkhairi, Allah ya..."
Dakatar da ita hajiya kubra tayi,
"Bana son godiyar nan Hafsat, duk abinda nayi miki kaina nayiwa, yanzu me zaki kaiwa kawar taki?"
"Ummi girki kawai zanyi mata inkai mata domin wallahi hatta abinci wahala yake mana acan.."
"To shikenan gashi nan sai ki zabi abinda zaki dafa mata,duk abinda zaki bukata da akwai kuma kin san wurinda yake.."
Daga haka hajiya kubra ta juya tawuce cikin falo domin lokacin acikin kitchen suke Hafsat tana wanke wanke saboda sam bata son zama batare da tayi dan wani aiki ba,
Shinkafa da miyar kaji Hafsat ta dafawa Amina cikin manyan food flaks guda biyu, wanka tayi ta shirya cikin wata shaddar amal kalar ruwan toka,farin hijab tasa tafito ta iske hajiya kubra zaune tana karanta wani English novel,
"Hafsat anfito?"
"Ehh Ummi nashirya"
"To driver yana waje yana jiranki, yanzu idan kin tafi sai yaushe zaki dawo?"
"Ummi zan dan jima saboda kinga rabona da Amina an kwana biyu.."
"To shikenan sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya.."
"Amin" ta amsa tareda fita ta shiga kitchen ta debi girkin da tayiwa aminan tafita compound din gidan inda salisu driver yake jiranta,
Har wani nushadi takeji yau haka kawai saboda zataje taga Amina da sauran mutanen dake gidan marayun.
****
Tunda yusleem yaji mami tace masa anjanye maganar aurenshi shikenan yasaki jiki yayi watsi da maganar bai kara bi takanta ba amma ita mami abun yana nan aranta domin har yanzu kullum cikin tanadin kayan aurenshi take, duk inda taji ankawo kaya masu kyau ko masu tsada na mata sai ta siyo kuma zata nuna masa tace matarsa ta siyawa wacce zai auro nan gaba, shidai baya magana sai dai yayi shiru amma kuma shine zai biya kudin kayan da ta siyo wannan kam ko nawane baya shayin biya kuma bai taba musu ba,
Yauma hakance tafaru lokacin da ya shigo gidan ya isketa afalo ita da wata mata wacce ta Kawo mata kaya daga dubai, wasu dogayen riguna ne masu adon stones ajiki hadaddu,
Daga rigunan mami taci gaba dayi tana jujjuya su, bayan sallamar da yayi bai sake yin magana ba yasamu wuri ya zauna,
"Yusleem kaga rigunan nan daga dubai aka kawo kuma sunada kyau nayi sha'awarsu mutuka ko zaka siyawa matarka..?"
Yaji sarai abind mamin tace amma bai amsaba, kasancewar tasan halin abinta yasata daukar kala biyu, ja da kuma baka mai adon golden ajiki,
"Gashi na daukar maka guda biyu, duk guda daya 35 thousands ahakanma ragi tayi min amma bahaka take sayarwa ba.."
Gyada kai yayi har lokacin baice komai ba saboda shidai baiga amfanin kayan nan da mami ta dage taketa siya ba,
Saida mai kayan tatafi sannan yadubi mami wacce ke zaune har lokacin tana ta dudduba rigunan tana yaba kyawunsu,
"Wai mami dan Allah meye amfanin wadannan kayan da kiketa siye?"
"Amfaninsu? Amfaninsu kake tambaya? Kaifa mukayi dakai zaka nemo matar aure, ko kamanta? Ai zuba maka ido nayi ka gama zagaye zagayenka ka Kawo min wacce kakeso idan kuma hakan ya faskara to ni bazan gajiya ba wurin sake nemo maka wata.."
Shiru yayi ya lumshe manyan idanuwansa tareda jingina da jikin kujerar da yake zaune batare da yayi magana ba....
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*15*
***Lokacin da Hafsa takarasa gidan marayun ba karamin dadin ganinta Amina tajiba domin bata taba tsammanin sake yin tozali da itaba acikin rayuwarta,
Kebewa sukayi suka samu kasan wata bishiyar darbejiya suka zauna suka fara tattaunawa,
"Hafsa har kinyi kyau, ki ganki yanda kika sauya lokaci daya" Amina tace da Hafsat tana bin jikin Hafsat din da kallo,
"Amina kema insha Allah canji yana nan zuwar miki ai tunda mukayi hakuri da rayuwar da muka samu kanmu to da izinin Allah zamu dace da samun babban rabo.."
"Hmmm abar kaza dai kawai acikin gashinta hafsa, yawwa baki bani labarin yanda akayi ba rannan da kika tafi.."
Kwashewa duk yadda akayi hafsat tayi tafadawa amina da irin gatan da take samu yanzu,
Sun dade suna hira domin sai da la'asar liss sannan hafsat tatafi nan dinma kamar kada su rabu da amina saida hafsa tace ai zata rinka zuwa akai akai sannan hankalin amina ya kwanta.
Lokacin da hafsat takoma gida har alhaji sa'id yadawo daga office yana zaune a falon hajiya kubra shida ita bayan ya kammala cin abinci kasancewar yau bai dawo yin lunch ba,
Sallama tayi tashiga bayan sun amsa mata,
"Hafsa yau kuma ziyara aka kai?" Alhaji sa'id ya tambayeta yana murmushi,
"Ehh Abba" tabashi amsa,
"To ai yayi kyau, kin kyauta mutuka wannan ya nuna min cewa bazaki manta dasu ba duk abinda kika zama nan gaba"
"Ai da alama kam hafsat bazata manta dasu ba" hajiya kubra ta karbe zancen ta hanyar bawa alhajin amsa,
Zama hafsat tayi acikin falon tana sauraren hirar da su alhaji keyi wanda basu suka tashiba sai da sukaji anfara kiran sallar magrib.
Satin hafsat uku agidan amma kai idan kaganta zakace wata uku tayi domin tayi kiba tayi bul bul sosai, domin tana samun kulawa sosai daga iyayen rikon nata ga gata da suke nuna mata kamar sune suka haifeta,
Malamai guda biyu musamman alhaji sa'id ya daukosu domin su rinka koyar da ita karatun boko da na Arabic, sannan kuma yayi mata register a wata center ta mata wacce ake koyar da sana'o'i saboda tana son tasake samun kwarewa sosai akan sakar da ta iya,
Wadannan abubuwan da tasaka agaba sune suka saka bata da lokacin kanta yanzu koda yaushe tana da abinyi amma hakan bai hanata ware lokaci na ziyartar kawarta amina ba,
A fannin sakar ma tafi maida hankali domin hajiya kubra tafada mata cewar idan har ta gwanance to zata siyo mata keken saka kuma tanada shagon saida kayayyaki zata bata jari tafara saka kaya ana kaiwa shagon ana sayar mata wannan dalilin ne yasa ta bada himma sosai har ta samu kwarewa kamar yadda hajiya kubran keso,
Satinsu shida aka yayesu domin sun iya sosai, alkawarin da hajiya kubra ta daukar mata ta cika ta hanyar siyo mata keken saka harda sabuwar wayar hannu dambasheshiya mai kyau kirar kamfanin LG,
Murna wurin hafsa sai wanda yagani, samun keke da tayi sai yasake rike lokacin ta koda yaushe tana kai tana aiki acikin satittika kadan ta saka kaya masu yawan gaske, kayan sanyi na yara da towel da safa da hula,
Diban kayan akayi aka kai shagon hajiya kubra na kasuwa acikin satin aka Kawo kudin kayan domin har sun kare,