Sashe 28
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fita mami tayi ita kuma ta tsaya tana nazarin ta yadda zata fita falo domin bata son su hadu da yusleem, ta dade tsaye akofar dakin tana ta tunani kafin daga bisani tayi kuru tafita,
Akan kujera ta hango yusleem kwance yana kallon tv ita kuma mami tana zaune tana hada ruwan zafi,
Kin kallon yusleem tayi taje kusa da mami ta zauna itama tasoma hada ruwan zafin,
"Kai yusleem bazaka yi breakfast din bane?"
"Mami sai zuwa anjima yanzu ruwan zafi kadai zan Sha"
"To bari akawo maka"
Hada masa tea din hafsat tayi ta dauka takai mishi, zaune yatashi yana kallon fuskarta amma saita kawar da tata fuskar,
"Yaya wankan safe...?" Yafadi lokacin da zai karbi cup din, shiru tayi masa tayi hanzarin barin wurin aranta tana tunanin yanda akayi yazama marar kunya tsakanin daren jiya zuwa yau,
Misalin karfe 10 nasafe suna zazzaune acikin falon sai ga khadija tashigo, tana sanye da orange colour din atamfa da mayafi kalar atamfar da yar karamar hand bag,
Duba yusleem tayi tatafi bayan sun gaggaisa, bayan tafiyar khadija mai gadi yashigo yace anyi baki wai masu siyan gidane suka zo, mamice tafita bayan ta dauki wasu takardu,
Wasu mutane guda biyu tasamu tsaye a compound din gidan suna jiranta amma yau babu dr sufyan,
"Sannu alhaji, wadannan sune takardun gidan gashi.."
Karbar takardun wani dan dattijon mutum yayi yafara dubawa, yajima yana nazarin takardun kafin ya dago yana kallon mami,
"Hajiya wannan wanda sunansa yake jiki shine mai gidan?"
Jijjiga kai mami tayi,
"Ehh shine yarona ne"
"Yana ina yanzu?"
"Yana ciki"
"Zan iya ganinsa?"
"Me zai hana, bisimillah zo mu karasa"
Yusleem yana zaune a falo ya tisa Hafsa agaba yana tsokanarta sai gasu mami sun shigo tashi yayi daga kusa da Hafsa yakoma wata kujerar ya zauna,
"Yusleem ga bakinka" inji mami, cikeda mamaki ya kalli mutanen nan yaga babu wanda yasani acikinsu, zama wannan dattijon yayi ya kalli yusleem,
"Yusleem baka ganeni ba ko?"
Daga kai yusleem yayi alamun eh,
"Zaka iya tunawa shekaru shida da suka wuce kaje neman aiki a wata ma'aikata ta yada labarai? A lokacin anyi maka interview daga baya kadawo akace maka baka samu aikinba"
Murmushi yusleem yayi alamun ya tuna,
"Ok sai yanzu natuna ai dayake shekarun an dan kwana biyu"
"To yusleem tun lokacin da kayi interview kasamu wannan aikin kuma abangarena wato department dina, nine nan nahanaka aikinka nace baka samuba amma gwamnati ta daukeka sannan duk watan duniya tana biyanka albashi na naira dubu hamsin da biyar banda allowances d sauran alkhairan da baza arasaba, nine na rinka rike kudin ina harkokin gabana dasu har lokacin da zaka samu promotion daga grade level 9 zuwa grade level 12,haka na rinka ninke kudinka ina kasafin gabana har saida naji wani malami yayi wa'azi akan mutane masu aikata laifi irin nawa, to tun daga nan nasoma binciken hanyar da zanbi insadu dakai inbaka hakkinka da aikinka amma kuma duk lokacin da nakira wayarka bata shiga, daga karshe danaga narasa yanda zanyi inganka sai narinka tara maka albashinka ina ajiye maka kuma ina juya maka acikin kudadena na kasuwanci wanda yanzu haka duk dukiyata tamuce nida kai, kayi hakuri yusleem ka yafe min domin na danne maka hakkinka kuma na cutar dakai..."
Jin maganar yusleem yayi kamar acikin mafarki, bashi kadaiba hatta su mami abin yabasu mamaki mutuka amma kuma duba da irin zamanin da muke ciki yanzu sai mamakin nasu baiyi yawa ba domin yanzu zalunci awurin mutane ba abune mai wahala ba,
"To ai alhaji ni banma san me zance ba domin gaba daya kaina yagama daurewa.." Yusleem yayi maganar yana kallon mami wadda ita dinma shi take kallo zuciyarta kamar kankara dan farin ciki domin arzikin danta da alama yakusa dawowa,
"yanzu tashi zakayi kazo muje inkaika kamfanoninmu da gidajenmu da kuma shagunanmu wadanda ake sayar mana da kayayyakin da kamfanin mu yake sarrafawa, yusleem wallahi kullum da kai nake kwana acikin raina inata addu'ar Allah yasa sai mun hadu nabaka hakkinka kafin na amsa kiran ubangijina, gashi yau burina yacika, zan sauke babban nauyi, zan baka albashinka na shekaru shida sannan kuma zan raba dukiyata gida biyu inbaka taka, haka kuma zamuje can ministry of information domin abaka office dinka wanda yake can yana jiranka.., yanzu tashi mu hanzarta mu tafi"
Farin cikine ya lullube Hafsa nan tasoma yiwa ubangiji godiya acikin zuciyarta, ji take kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan farin ciki,
Alhaji musa mori bai bar yusleem yasake wata magana ba yasashi agaba suka fita yace zaije ya sauke nauyi,
Har tsakar gida mami da hafsat suka rakasu saida suka ga fitarsu sannan suka koma ciki cikeda farin ciki da murna, dan murna ko abincin rana kasa ci sukayi suna jiran suga dawowar yusleem amma har dare bai dawoba gashi kuma washe gari da safe zai tafi kasar Cairo,
Yusleem kuwa tunda suka fita basu samu zamaba suna can sunata yawo ana nunnuna masa filayensa da gidaje da shaguna da kamfanoni, basu suka samu Kansu ba sai karfe 9 nadare nan alhaji musa yagayyaceshi suje gidanshi suci abinci amma yusleem yaki yace gida zaije domin gobe da safe zai tafi kasar Cairo nan suka rabu da alhaji musa akan sai bayan yadawo sannan zasu karasa duk wasu abubuwa wadanda suka dace, suka kawoshi gida suka ajiyeshi.
Afalo yasamu su mami zaune suna sauraron zuwanshi kowannensu da gani babu tambaya yana cikin walwala da farin ciki, zama yayi agajiye kusa da hafsat yana murmushi,
"Wallahi yau nasha wahala mami, munyi tafiya sosai har wasu yan kauyuka mukaje.."
"Ikon Allah, Allah mai yadda yaso, Allah yasanya alkhairi dai" inji mami,
"Amin" ya amsa mata tareda kwashewa yadda akayi yasanar da ita, murna dukkansu suka rinka yi sai lokacin suka iya cin abinci, faten wake da kifi yaji albasa da manja, acikin faranti babba hafsat ta zuba musu suka hadu gaba dayansu sukaci harda mami,
Mamince tafara tashi tawuce bedroom dinta tabarsu awurin, kallon hafsat din yakeyi yanda taketa wani sussunne kai ita adole kunyarshi takeji, bai kulata ba yatashi yafita, wanka yaje yayi ya duba kayanshi yasa domin har hafsat ta hada masa yan kayan da zai tafi dasu,
Saida yashirya tsaf sannan yanufi part din mami, dakin da hafsat take ciki yatura yashiga, tana tsaye gaban mirror tana shafe jikinta da turare mai dan karen kamshi da dadi,
Abayanta yatsaya yana kallonta yana shakar kamshinta wanda yatasamma rikita masa kwakwalwa,
"Ashe nidinma dan gatane tunda gashi nan ana shirin yimin tarba ta musamman" yafada cikin tsokana,
Shiru tayi bata tanka ba, ji tayi yadauketa yayi saman gado da ita, rungumeta yayi yana bata labarin abinda yafaru tun daga fitarsa har Kawo dawowarsa,
"Yaya yusleem ai Allah yaga sadaukarwar da kayi kuma yaga irin tuban da kayi shiyasa bazai taba barinka katabe ba.."
"To ai da taimakonki hakan yafaru madam, Allah yayi miki albarka.."
Kasa amsawa tayi domin tuni taji yasoma yunkurin irin wasannin da yayi mata adaren jiya,
Duk da yanata maganar yagaji yagaji yau amma hakan bai sashi yayi barci ba, yanda sukaga rana haka sukaga dare har asuba tayi, saida sukayi salla sannan suka kwanta bacci.
Itace tafara tashi lokacin karfe 9 nasafe tayi wanka tafita wurin mami, bayan sun gama breakfast tana shirin taje ta tasoshi sai gashi yafito, kamar ta nitse dan kunya duk da tasan yanzu mami tagama gane adakin yake kwana, tagefen ido ta kalleshi lokacin da yana gaida mami,
"Yusleem karfe 11 fa zaku tashi, kayi sauri kashirya muje mu rakaka" mami tayi maganar tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, tea kawai yasha yatafi shiryawa,
10:30 daidai yafito tsaf cikin shirinsa natafiya, yasha kananan kaya, iya hafsat ce kadai acikin falon tana jiran mami tafito tana tsaye gaban wani console tana ganin fuskarta, abayanta ya tsaya, yariko kugunta nan tayi saurin juyowa,
Murmushi yayi yakai mata kiss saman bakinta tayi saurin gocewa, hannunta yariko,
"Jiya baki ki ba yau kuma tsabar gulma ce tasaki kin yarda?"
Hannu tasa tarufe fuskarta, jin mami na kokarin fitowa yasashi sakinta nan suka dunguma suka tafi, motar mami suka shiga driver yaja suka fita daidai lokacin motar khadija ta Kawo kai nan tayi reverse tabi bayansu.....
_Gaisuwar fatan alkhairi ga Anty A'isha (mama 4),Anty Aisha (maman minal),Maman sultan, & Hawy yanmata_
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*45*
***Ta cikin mirror din saitinshi yake hango fuskar hafsat wacce ke kunshe da abubuwa guda biyu wato farin ciki da kuma sabanin haka,
Mami kuwa tamkar tafi kowa farin cikin wannan tafiyar ta yusleem domin zaka gane hakan idan har ka kalli fuskarta,
Tafiyar mintuna 15 zuwa 20 ne yakaisu airport din suna yin packing saiga khadija itama tayi packing din tata motar akusa dasu dan haka kusan atare suka firfito,
Cikeda fara'a ta karaso wurinsu tasoma gaisar da mami, cikin fara'a mami ta amsa domin acikin farin ciki take, dan kallon yusleem tayi taga hankalinsa ai bama anan yakeba domin yana tsaye shida hafsat suna yin magana,
Tsayawa dukkaninsu sukayi ajikin mota suna jiran su,
Hawayene suke kokarin zuba a idon hafsat yusleem yayi saurin kama hannunta suka bar wajen, can dan nesa dasu mami sukaje yafara rarrashinta,
Hannuwanta duka biyu yarike yana kallon fuskarta,
"Haba nanah karki zama raguwa, kiyi hakuri kinga da ace tun farko kudin nan sun fito dawuri to da tare dake zan tafi..."
Hawayen da taketa kokarin hana zubowarsu ne suka zubo sharr nan yakai hannunshi ya goge mata,
"Daina kuka, me kike so inkawo miki idan zan dawo..?"
Shiru tayi idanuwanta na kallon kasa,
"Abin dadi?, ko kayan kwalliya?", taji yasake tambayarta, girgiza masa kai tayi alamun a'a,
"To me kikeso?"
Nunashi tayi da dan yatsa,
"Ni kaina...?" Yayi maganar murya kasa kasa,
Kai ta daga masa,
Hannuwanta taji ya matse tareda janta zuwa kirjinsa bata fargaba tajita rungume ajikinshi,
"Yaya yusleem su mami..." Tafada tana kokarin zamewa, sassauta rikon da yayi mata yayi yana murmushi,
"Ki kwantar da hankalinki idan nadawo zaki sameni har sai ma kin gaji dani"
Murmushi tayi ta zame jikinta tana kallonshi, shi dinma kallon fuskarta yake yana murmushi, wurinsu mami suka koma yayi musu sallama ya dauki yar jakar kayanshi yawuce,
Akan kujera ta hango yusleem kwance yana kallon tv ita kuma mami tana zaune tana hada ruwan zafi,
Kin kallon yusleem tayi taje kusa da mami ta zauna itama tasoma hada ruwan zafin,
"Kai yusleem bazaka yi breakfast din bane?"
"Mami sai zuwa anjima yanzu ruwan zafi kadai zan Sha"
"To bari akawo maka"
Hada masa tea din hafsat tayi ta dauka takai mishi, zaune yatashi yana kallon fuskarta amma saita kawar da tata fuskar,
"Yaya wankan safe...?" Yafadi lokacin da zai karbi cup din, shiru tayi masa tayi hanzarin barin wurin aranta tana tunanin yanda akayi yazama marar kunya tsakanin daren jiya zuwa yau,
Misalin karfe 10 nasafe suna zazzaune acikin falon sai ga khadija tashigo, tana sanye da orange colour din atamfa da mayafi kalar atamfar da yar karamar hand bag,
Duba yusleem tayi tatafi bayan sun gaggaisa, bayan tafiyar khadija mai gadi yashigo yace anyi baki wai masu siyan gidane suka zo, mamice tafita bayan ta dauki wasu takardu,
Wasu mutane guda biyu tasamu tsaye a compound din gidan suna jiranta amma yau babu dr sufyan,
"Sannu alhaji, wadannan sune takardun gidan gashi.."
Karbar takardun wani dan dattijon mutum yayi yafara dubawa, yajima yana nazarin takardun kafin ya dago yana kallon mami,
"Hajiya wannan wanda sunansa yake jiki shine mai gidan?"
Jijjiga kai mami tayi,
"Ehh shine yarona ne"
"Yana ina yanzu?"
"Yana ciki"
"Zan iya ganinsa?"
"Me zai hana, bisimillah zo mu karasa"
Yusleem yana zaune a falo ya tisa Hafsa agaba yana tsokanarta sai gasu mami sun shigo tashi yayi daga kusa da Hafsa yakoma wata kujerar ya zauna,
"Yusleem ga bakinka" inji mami, cikeda mamaki ya kalli mutanen nan yaga babu wanda yasani acikinsu, zama wannan dattijon yayi ya kalli yusleem,
"Yusleem baka ganeni ba ko?"
Daga kai yusleem yayi alamun eh,
"Zaka iya tunawa shekaru shida da suka wuce kaje neman aiki a wata ma'aikata ta yada labarai? A lokacin anyi maka interview daga baya kadawo akace maka baka samu aikinba"
Murmushi yusleem yayi alamun ya tuna,
"Ok sai yanzu natuna ai dayake shekarun an dan kwana biyu"
"To yusleem tun lokacin da kayi interview kasamu wannan aikin kuma abangarena wato department dina, nine nan nahanaka aikinka nace baka samuba amma gwamnati ta daukeka sannan duk watan duniya tana biyanka albashi na naira dubu hamsin da biyar banda allowances d sauran alkhairan da baza arasaba, nine na rinka rike kudin ina harkokin gabana dasu har lokacin da zaka samu promotion daga grade level 9 zuwa grade level 12,haka na rinka ninke kudinka ina kasafin gabana har saida naji wani malami yayi wa'azi akan mutane masu aikata laifi irin nawa, to tun daga nan nasoma binciken hanyar da zanbi insadu dakai inbaka hakkinka da aikinka amma kuma duk lokacin da nakira wayarka bata shiga, daga karshe danaga narasa yanda zanyi inganka sai narinka tara maka albashinka ina ajiye maka kuma ina juya maka acikin kudadena na kasuwanci wanda yanzu haka duk dukiyata tamuce nida kai, kayi hakuri yusleem ka yafe min domin na danne maka hakkinka kuma na cutar dakai..."
Jin maganar yusleem yayi kamar acikin mafarki, bashi kadaiba hatta su mami abin yabasu mamaki mutuka amma kuma duba da irin zamanin da muke ciki yanzu sai mamakin nasu baiyi yawa ba domin yanzu zalunci awurin mutane ba abune mai wahala ba,
"To ai alhaji ni banma san me zance ba domin gaba daya kaina yagama daurewa.." Yusleem yayi maganar yana kallon mami wadda ita dinma shi take kallo zuciyarta kamar kankara dan farin ciki domin arzikin danta da alama yakusa dawowa,
"yanzu tashi zakayi kazo muje inkaika kamfanoninmu da gidajenmu da kuma shagunanmu wadanda ake sayar mana da kayayyakin da kamfanin mu yake sarrafawa, yusleem wallahi kullum da kai nake kwana acikin raina inata addu'ar Allah yasa sai mun hadu nabaka hakkinka kafin na amsa kiran ubangijina, gashi yau burina yacika, zan sauke babban nauyi, zan baka albashinka na shekaru shida sannan kuma zan raba dukiyata gida biyu inbaka taka, haka kuma zamuje can ministry of information domin abaka office dinka wanda yake can yana jiranka.., yanzu tashi mu hanzarta mu tafi"
Farin cikine ya lullube Hafsa nan tasoma yiwa ubangiji godiya acikin zuciyarta, ji take kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan farin ciki,
Alhaji musa mori bai bar yusleem yasake wata magana ba yasashi agaba suka fita yace zaije ya sauke nauyi,
Har tsakar gida mami da hafsat suka rakasu saida suka ga fitarsu sannan suka koma ciki cikeda farin ciki da murna, dan murna ko abincin rana kasa ci sukayi suna jiran suga dawowar yusleem amma har dare bai dawoba gashi kuma washe gari da safe zai tafi kasar Cairo,
Yusleem kuwa tunda suka fita basu samu zamaba suna can sunata yawo ana nunnuna masa filayensa da gidaje da shaguna da kamfanoni, basu suka samu Kansu ba sai karfe 9 nadare nan alhaji musa yagayyaceshi suje gidanshi suci abinci amma yusleem yaki yace gida zaije domin gobe da safe zai tafi kasar Cairo nan suka rabu da alhaji musa akan sai bayan yadawo sannan zasu karasa duk wasu abubuwa wadanda suka dace, suka kawoshi gida suka ajiyeshi.
Afalo yasamu su mami zaune suna sauraron zuwanshi kowannensu da gani babu tambaya yana cikin walwala da farin ciki, zama yayi agajiye kusa da hafsat yana murmushi,
"Wallahi yau nasha wahala mami, munyi tafiya sosai har wasu yan kauyuka mukaje.."
"Ikon Allah, Allah mai yadda yaso, Allah yasanya alkhairi dai" inji mami,
"Amin" ya amsa mata tareda kwashewa yadda akayi yasanar da ita, murna dukkansu suka rinka yi sai lokacin suka iya cin abinci, faten wake da kifi yaji albasa da manja, acikin faranti babba hafsat ta zuba musu suka hadu gaba dayansu sukaci harda mami,
Mamince tafara tashi tawuce bedroom dinta tabarsu awurin, kallon hafsat din yakeyi yanda taketa wani sussunne kai ita adole kunyarshi takeji, bai kulata ba yatashi yafita, wanka yaje yayi ya duba kayanshi yasa domin har hafsat ta hada masa yan kayan da zai tafi dasu,
Saida yashirya tsaf sannan yanufi part din mami, dakin da hafsat take ciki yatura yashiga, tana tsaye gaban mirror tana shafe jikinta da turare mai dan karen kamshi da dadi,
Abayanta yatsaya yana kallonta yana shakar kamshinta wanda yatasamma rikita masa kwakwalwa,
"Ashe nidinma dan gatane tunda gashi nan ana shirin yimin tarba ta musamman" yafada cikin tsokana,
Shiru tayi bata tanka ba, ji tayi yadauketa yayi saman gado da ita, rungumeta yayi yana bata labarin abinda yafaru tun daga fitarsa har Kawo dawowarsa,
"Yaya yusleem ai Allah yaga sadaukarwar da kayi kuma yaga irin tuban da kayi shiyasa bazai taba barinka katabe ba.."
"To ai da taimakonki hakan yafaru madam, Allah yayi miki albarka.."
Kasa amsawa tayi domin tuni taji yasoma yunkurin irin wasannin da yayi mata adaren jiya,
Duk da yanata maganar yagaji yagaji yau amma hakan bai sashi yayi barci ba, yanda sukaga rana haka sukaga dare har asuba tayi, saida sukayi salla sannan suka kwanta bacci.
Itace tafara tashi lokacin karfe 9 nasafe tayi wanka tafita wurin mami, bayan sun gama breakfast tana shirin taje ta tasoshi sai gashi yafito, kamar ta nitse dan kunya duk da tasan yanzu mami tagama gane adakin yake kwana, tagefen ido ta kalleshi lokacin da yana gaida mami,
"Yusleem karfe 11 fa zaku tashi, kayi sauri kashirya muje mu rakaka" mami tayi maganar tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, tea kawai yasha yatafi shiryawa,
10:30 daidai yafito tsaf cikin shirinsa natafiya, yasha kananan kaya, iya hafsat ce kadai acikin falon tana jiran mami tafito tana tsaye gaban wani console tana ganin fuskarta, abayanta ya tsaya, yariko kugunta nan tayi saurin juyowa,
Murmushi yayi yakai mata kiss saman bakinta tayi saurin gocewa, hannunta yariko,
"Jiya baki ki ba yau kuma tsabar gulma ce tasaki kin yarda?"
Hannu tasa tarufe fuskarta, jin mami na kokarin fitowa yasashi sakinta nan suka dunguma suka tafi, motar mami suka shiga driver yaja suka fita daidai lokacin motar khadija ta Kawo kai nan tayi reverse tabi bayansu.....
_Gaisuwar fatan alkhairi ga Anty A'isha (mama 4),Anty Aisha (maman minal),Maman sultan, & Hawy yanmata_
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*45*
***Ta cikin mirror din saitinshi yake hango fuskar hafsat wacce ke kunshe da abubuwa guda biyu wato farin ciki da kuma sabanin haka,
Mami kuwa tamkar tafi kowa farin cikin wannan tafiyar ta yusleem domin zaka gane hakan idan har ka kalli fuskarta,
Tafiyar mintuna 15 zuwa 20 ne yakaisu airport din suna yin packing saiga khadija itama tayi packing din tata motar akusa dasu dan haka kusan atare suka firfito,
Cikeda fara'a ta karaso wurinsu tasoma gaisar da mami, cikin fara'a mami ta amsa domin acikin farin ciki take, dan kallon yusleem tayi taga hankalinsa ai bama anan yakeba domin yana tsaye shida hafsat suna yin magana,
Tsayawa dukkaninsu sukayi ajikin mota suna jiran su,
Hawayene suke kokarin zuba a idon hafsat yusleem yayi saurin kama hannunta suka bar wajen, can dan nesa dasu mami sukaje yafara rarrashinta,
Hannuwanta duka biyu yarike yana kallon fuskarta,
"Haba nanah karki zama raguwa, kiyi hakuri kinga da ace tun farko kudin nan sun fito dawuri to da tare dake zan tafi..."
Hawayen da taketa kokarin hana zubowarsu ne suka zubo sharr nan yakai hannunshi ya goge mata,
"Daina kuka, me kike so inkawo miki idan zan dawo..?"
Shiru tayi idanuwanta na kallon kasa,
"Abin dadi?, ko kayan kwalliya?", taji yasake tambayarta, girgiza masa kai tayi alamun a'a,
"To me kikeso?"
Nunashi tayi da dan yatsa,
"Ni kaina...?" Yayi maganar murya kasa kasa,
Kai ta daga masa,
Hannuwanta taji ya matse tareda janta zuwa kirjinsa bata fargaba tajita rungume ajikinshi,
"Yaya yusleem su mami..." Tafada tana kokarin zamewa, sassauta rikon da yayi mata yayi yana murmushi,
"Ki kwantar da hankalinki idan nadawo zaki sameni har sai ma kin gaji dani"
Murmushi tayi ta zame jikinta tana kallonshi, shi dinma kallon fuskarta yake yana murmushi, wurinsu mami suka koma yayi musu sallama ya dauki yar jakar kayanshi yawuce,