← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 30

Sashe 2

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yusleem wai da me kake takama ne da har kadauki auri saki ba abakin komai ba?

Idan dan kyawun dakake dashi ne yasaka kake yin haka to ya kamata fa kasani akwai wadanda suka zartaka kyau amma basa yin haka,

Idan kuma dan arzikin dakake dashi ne to kasani akwai big millionaires suna nan ba irinkaba young millionaire ba kuma basa aikata wannan wulakancin dakake yi,

Inkuma kuruciyar da kake tare da itane yasaka yin wannan cin mutuncin to wallahi ka gaggauta farkawa daga wannan dogon baccin da kakeyi domin akullum shekarunka sake yawa suke bawai raguwa ba.."

Shiru mami tayi cikeda bacin rai tana huci saboda babatun da tagama yanzu,

Mikewa yayi sannan yayi magana ahankali,kamar mai ciwon baki yace,

"Kiyi hakuri mami.."

Ko amsa masa batayi ba yasaka kai yafice daga cikin falon, nan mami da surayya suka rakashi da idanu....

_*Ummi Shatu*_👌🏻[12/14, 9:21 PM] Ummu A'isha: ® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*4*

aishaummi.blogspot.com

***Tashi mami tayi tabi bayan hajiya fa'iza zuwa dakin da khadija ke kwance tagama cin kuka ta koshi dan tsabar kuka yanzu ko hawayen ma bata iyayi,

Zama mami tayi agefen gadon da khadijan ke zaune ta dafata jikinta asanyaye,

"Khadija kiyi hakuri kinji, insha Allah komai zai daidaita sannan zaki koma gidan mijinki"

D'aga jajayen idanuwanta wadanda suka rine tayi ta kalli mami,

"Mami bazan iya komawa gidansa ba, nahakura da aurenshi, bazan sake iya zaman aure dashi ba wallahi"

Gaban mami ne yashiga dukan tara tara saboda jin abinda khadija tafada,

"Khadija wani abu yayi miki?"

"Mami ni babu abinda yayi min kawai wulakancinshi ne bazan iya cigaba da jurewa ba"

Dafata mami tasake yi,cikin sigar lallashi tace,

"Nasani khadija, kuma nasan kinada hakuri amma daurewa zakiyi kisake yin wani hakurin ki koma dakinki..."

"Mami bazan iya komawa ba wallahi nidai nahakura"

"To kuma khadija idan Allah ya kaddaro da rabo a tsakaninku fa? Bana son ayi gaggawar yanke hukunci daga baya kuma azo ana dana sani"

Sai a lokacin hajiya fa'iza mahaifiyar khadija tayi magana,

"Ai hajiya siyama maganar rabo a tsakaninsu ma babu shi saboda tunda akayi auren bai taba shiga dakinta ba, ko kallo bata isheshi ba bare har ya kulata"

Tagumi mami ta rafka taci gaba da sauraron bayanin da hajiya fa'iza take yimata na irin zaman da yusleem yayi da khadija ta rufe maganar da cewa,

"Kawai dai muyi addu'a Allah yasa hakane mafi alkhairi, nanda sati biyu kuma zamuzo mu kwashe kayanta ki fada masa"

Ita dai mami jiki babu kwari ta mike bayan tagama bawa khadija da mahaifiyarta hakuri, jakarta ta dauka ta fita ranta babu dadi zuciyarta cike da bacin rai, wannan karon kam yazama dole ta nunawa yusleem fushinta akan abinda yajima yana aikatawa na sakin mata babu gaira bare dalili, babu laifin tsaye babu na zaune.

Har kofar gida hajiya fa'iza ta rakata suna cigaba da bawa juna hakuri musamman ma mami da take ganin laifin na yusleem ne domin shine yake nema yaja mata lalacewar zumuncinsu da matar da suka dade atare,

Mota Mamman driver ya bude mata tashiga ta zauna ya rufe suka tafi domin tuni hajiya fa'iza tajima da shigewa cikin gida.

Da tunani kala kala acikin zuciyarta suka karasa gida, cikeda damuwa take zayyanewa surayya abinda yafaru, suna tsaka da yin maganar sukaji shigowar yusleem,

Bai karaso cikin falon ba yatsaya a dining area, sanye yake da jar t shirt mai gajeren hannu sai black trouser, kamshin turaren lailatul abyad da na real oud ne yake tashi daga jikinsa, fuskarshi tayi fes sai annurin kyaune yake fita daga gareta,

D'aga murya Mami tayi tayadda tasan zai iya jiyota,

"Kai..."

"Na'am ma..." Ya amsa yana kokarin bude jeren flasks din dake ajiye asaman table din,

"Zo nan.." Mami tafada bayan ta daure fuskarta, fasa diban abincin yayi ya tasamma cikin falon inda su Mami suke.

***

Rayuwar Hafsat haka taci gaba da tafiya agidan marayu, yanzu haka ta maida hankali sosai wurin koyon sana'o'in hannu domin ana zuwa akoya musu, musamman aka ajiye musu wadanda zasu rinka koyar dasu,

Cikin lokutan da babu yawa ta kwarance wurin sak'a sannan tafara iya dinkin keke,haka kawarta Amina itama tana yi daidai gwargwado,

Kullum cikin yin sak'a suke itada Amina suna warwarewa sai su sake saka wani abun nadaban kamar hula, safa, ko riga,

Yau ma kamar kullum suna zaune a inda suka saba zama suna yar hirarsu kowaccensu tana rikeda koreshi tana yin saka,

Hirarsu ce ta katse saboda gano wasu manya manyan motoci da sukayi suna kokarin shigowa cikin harabar gidan,

Amina ce ta zunguri Hafsat da hannunta,

"Hafsat yauma da alama munyi baki, watakila mai girma governor ne yakawo mana ziyarar bazata.."

"Nima dai abinda nake tunani kenan Amina, koma dai menene kinga tashi muje ayi damu kin san bahaushe yace wai gani ya kori ji..."

Mikewa sukayi atare kowaccensu ta tukunkune zaren kulunta da koreshi suka nufi inda suka hango mutanen gidan suna tafiya....

*_Ummi Shatu_*👌🏻
[12/14, 9:21 PM] Ummu A'isha: ® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*5*

aishaummi.blogspot.com

***Ahankali yake ratsawa har zuwa cikin falon mami inda suke zaune itada surayya,

Tunda yaga fuskarta yasan tana cikeda bacin rai,

Zama yayi acikin daya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun dake girke acikin falon,

Tamkar basarake haka yajingina da jikin kujerar ya kishingide,

"Yusleem kana son inyi maka mugun baki..?"

Mami tafada ahasale cikin fada, shiru yayi bai amsa ba hakan yasake tunzurata, cikin tsawa tasake yin magana,

"Ba dakai nake yin magana ba?"

Dan kallonta yayi,

"Mami laifin me kuma nasake yi?"

"Ban saniba, ohhh watonma tambayata kake me kayi? Harma ka manta abinda kayi kenan..?"

Jijjiga kai mami tashiga yi ta maida dubanta ga surayya wacce ke zaune tana jinsu,

"Lallai surayya gaskiyarki ne dole sai an binciki kwakwalwarsa, kinji yanzu wai tambayata yake me yayi, watonma shi har ya manta, dole ka manta mana tunda ka cimin mutunci a idon duniya, sannan ka nunawa duniya ban isa dakaiba, ka cuci yar mutane ka mayar da ita bazawara.."

Nunashi da yatsa tayi,

"To wallahi kaji tsoron Allah yusleem, ina fada maka kaji tsoron Allah domin wallahi bazai barka ba indai kaci gaba da wannan mummunar dabi'ar taka ta auri saki"

"Mami yanzu shikenan anty khadijan tatafi bazata dawoba?" Surayya tayi tambayar tana kallon mami,

"Surayya ai babu macen da za ayiwa irin wannan wulakancin ta yarda tasake dawowa, yayanku bashida hali mai kyau mugun mutum ne.."

Da sauri ya kalli mami, sai lokacin yayi magana,

"Mami muguntar me nayi? Ita khadijan ce tace miki ni mugune?"

Kallonsa mami tayi cikeda masifa,

"Ai basai ta fada minba, kai yanzu acikin halayenka har sai wata tafada min? Acikin halayenka wanne ne bansani ba?

Kai cikakken mugune, miskili, mai shegen tinkahon tsiya da girman kai,

To bari kaji infada maka, komai tinkahon mutum da girman kansa idan yashiga wurin matarsa kaskantar da kansa yake komai sarautarsa da kudinsa, amma kai hatta matarka wannan shegen kasaitar taka da girman kai kake nuna mata.."

Shiru yayi bai sake maganaba, yayinda mami taci gaba da zuba masa fada har saida tayi mai isarta sannan ta sassauta,

"Yusleem nakasa gane damuwarka, tun kana karami kai mutumne mai zurfin ciki, amma ai bakada wanda zaka iya fadawa damuwarka sama dani da na haifeka, idan wani abune yake damunka kasanar dani.."

"Nifa lafiya lau nake mami, babu abinda yake damuna" yabata amsa,

"Karya kake, tayaya zan yarda dakai bayan kana yin abu irin na marassa lafiya, tunda bazaka fada minba to ya zama wajibi agareni inkaika adubaka, yanzu maganar zuwa chairo da nayi maka dazu to harda kai zamuje, zan kaika kaima su bincika min kwakwalwarka agani domin inajin kasamu tabin kwakwalwa a wannan accident din da kukayi da mahaifinku.."

Murmushi yadanyi saboda maganar ta mami dariya taso bashi,

"Mami tabin hankali kuma? Nidin?"

"Kai kuwa, ai ni har yanzu ban tabbatar da cewa kanada cikakken hankali ba har sai kikitoci sun tabbatar da hakan.."

Mikewa yayi domin yunwa yakeji, dining ya nufa nan mami tabishi abaya,

"Kullum kai kenan azuwa cin abinci gidan nan, yanzu da kanada matarka kuma ka riketa da daraja da ba kana can ta hada maka dinner mai ban sha'awa ba"

Baiyi magana ba yaja kujera ya zauna yafara bude flask din dake jere agabanshi,

Surayya ce ta kwaso da gudu,

"Yaya Karka taba wannan nawane.."

Daure fuska yayi yabude flask din, farfesun dankali ne da hanta da kwai da alayyahu yasha curry sai kamshi yake,

Kamar bazaiyi magana ba,daga ido yayi ya kalli surayya sannan ya mayar da dubanshi ga mami,

"Mami zan fasa bakin yarinyar nan.."

"Akan me? Abincinta fa ka taba, da kayi zuciya ka rike aure ka rike matarka hannu bibbiyu ai da duk ba akai ga hakaba" mami tace dashi tana kokarin zuba tuwon accah miyar egusi,

Bai tanka ba ya debi farfesun dankalin acikin flate ya fara tsakura yana ci,

Cigaba da yi masa gugar zana mami tayi shi dai bai kulaba, wannan yana daya daga cikin abinda yasa mami take ganin ba kowacce macece zata iya zama dashi ba domin ko zaka shekara kana yi masa magana sai ya gadama zai amsa idan bai gadama ba har kayi ka gama bazai amsa maka ba, yusleem miskili ne nagaske,ahaka ya karaci cakule cakulen abincin yagama yatashi ya nufi gidanshi wanda ke can wata unguwa daban bata su mami ba.

***

Daga can baya su Hafsat suka tsaya itada amina suna hangen bakin dake fitowa daga cikin motocin da suka zo yanzu,

Wata bakar jeep mai dauke da glasses masu duhu aka bude nan wani matashin saurayi ya fito, yana sanye da suit blue colour da bakin face idanuwanshi sakaye aciki wanda ya karawa fuskarshi haiba,ashekaru bazai wuce shekaru 30 ba zuwa 31,

Dan yatsina fuska yake kamar wani mace ko kuma kamar wanda yaga kashi,

Kallon hafsa amina tayi,

"Hafsat kalli wancan mutumin, yanzu dama aduniya akwai irinshi?"

"Uhm amina kenan, mu ai kinsan muna nan akumshe dan haka baza mu san me duniya take cikiba"

Jin anfara bayani akan bakin nasu da suka Kawo musu ziyara yasasu maida hankulansu can.
Chapter 2 · 0% Book details