Sashe 6
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko shakka babu badan rayuwarta agidan marayu tayita ba to da zata iya yarda da cewar wannan ta jikin hoton itace, sake kallon hoton tayi akaro na biyu wanda yarinyar jiki ke sanye da english wears pink din riga da farin wando, kanta sanye da hula pink colour,
"Ikon Allah..." Tafada ahankali tana mai sake dauko wani hoton tafara kallo, nan ta lalace wurin kallon hoton batare data kosa ba.
Kasa koda zama hajiya kubra tayi illah kaiwa da kawowa da take ta faman yi dan tsananin farin ciki, tabbas wannan wani al'amari ne daga Allah Wanda shi kadai yabarwa kansa sani,
Ganin zama yagagara yasata fita ta nufi part din alhaji, shima shigowarsa kenan daga masallacin dake kofar gidansa,
Zama tayi akan kujerar dake makotaka da tashi,
"Alhaji nidai kaganni tsabar farin ciki nakasa zaune nakasa tsaye.."
Murmushi alhaji sa'id yayi,
"To in banda abinki hajiya menene abin kasa tsaye da kasa zaune? Yanzu ina ita yarinyar take?"
"Alhaji dole inkasa zaune in kasa tsaye mana,ai farin cikin da nake ciki bazai barni inyi hakaba, tace min sunanta hafsat, tana can dakin amal nakaita tayi wanka ta shirya sai tafito muyi dinner.."
"Hakan yayi daidai hajiya kubra,nidai abinda nakeso dake shine dan Allah ki rike yarinyar nan bisa amana duk danasan zaiyi wuya ki gallaza mata tunda bata da maraba da amal to amma wani lokacin ku mata ana ganin kamar kunfi kowa tausayi da rauni sai dai akan gallazawa yaran da ba nakuba kunfi kowa nuna rashin tausayi da rashin rauni, dan Allah ki riketa amana tunda kinga daga gidan marayu na daukota wannan yana nuna cewar ita maraya ce..."
"Haba alhaji ai basai kayi min wannan nasihar ba domin ko wanine yakawo min wannan yarinyar wanda bakai ba wallahi zan kula da ita..."
"Nasani hajiya kubra, Allah yayi miki albarka, yanzu ina tunanin ai tagama ko?"
"Ehh to bari indubo ingani"
Tashi tayi tafita takoma part dinta, dakin amal ta tura tashiga nan ta iske hafsat zaune ta kurawa hotunan amal ido ko kifawa bata yi,
"Hafsat..." Ta kira sunanta bayan takarasa kusa da ita, dagowa hafsat tayi ta kalleta,
"Na'am"
"Ya bakiyi wanka kin canja kayan jikinki ba? Tashi ki shiga bathroom kiyi wanka indan kin fito ga drewar din kayan amal nan ki duba duk wanda yayi miki kisaka.." Ta karasa zancen tana nuna mata drewar din da dan yatsanta,
"To" hafsat ta amsa har lokacin tana cike da mamaki domin ganin abubuwan dake faruwa take yi tamkar acikin mafarki,
Fita hajiya kubra ta sake yi ganin haka yasa hafsat tashi ta shiga cikin bathroom din, komai wanda ake bukata akwaishi acikin bathroom din babu bata lokaci tayi wanka ta fito, man da zata dan shafawa fatarta ta shiga nema domin duk wadanda ke kan dressing mirror din lotion ne dan haka dakyar tasamu wani me dan kama da Vaseline tashafa,
Gaban drewar taje ta bude nanfa mamaki yacikata domin kayane iya ganinta shake acikin drewar din,
Wata doguwar riga kalar ruwan hanta ta zaro da dan kwalinta tasaka ta dauki hijabinta tayi salla,tana saman abin sallar azaune a inda aka kebe musamman domin yin salla hajiya kubra tasake shigowa fuskarta dauke da murmushi,
"Hafsa kin idar ne?" Tajiyo muryar hajiya kubra na tambayarta,
"Ehh na idar.." Tabata amsa tana kokarin mikewa,
"Yawwa to taso kizo muje wurin alhaji"
Bin bayanta tayi suka fita, tiryan tiryan tana biyeda ita har suka shiga falon alhaji sa'id Wanda ke zaune yana kallon labarai a tauraron dan adam,
Ganinsu yasashi rage volume din tv din ya fadada murmushinsa yana kallonsu domin sai yake ganin kamar hajiya kubra ce da amal suke dososhi kamar yadda suka saba akowanne dare domin yin hira,
"Alhaji...,labarai kake kallo?"
"Wallahi kuwa hajiya, keda 'yar takine?"
"Ehh amma har yanzu dai banga alamar zata sake ta saki jiki damu ba saboda ganinmu take baki agareta" hajiya kubra tafada fuskarta da yar damuwa,
"To wannan kuma dama ai sai ahankali,kin san ai yau tafara ganinmu,sai asannu ko Hafsat?" Yakarasa zancen cikin barkwanci,
Hafsat kam shiru tayi takasa koda kallonsu, sai dai wani lokacin ta dan saci kallonsu ahaka har lokacin sallar isha yayi nan alhaji sa'id yafita masallaci yabarsu a cikin falon nashi,
Anan Hafsat da hajiya kubra sukayi sallarsu,suna nan zaune har alhaji sa'id yadawo dan haka hajiya kubra ta mike domin gabatar musu da abincin dare,
"Hafsat zo muje kitchen.."
Mikewa Hafsat tayi suka fita zuwa cikin kitchen wanda kallo kawai Hafsat ta bude ido tanayi saboda ita ba taba ganin irin shi tayiba,
Akan babban faranti hajiya kubra ta jera flasks din abincin nan Hafsat din ta karba ita kuma hajiya kubra ta debi filet da sauran abubuwan da suka kamata,
Zama Hafsat tayi bayan ta ajiye farantin, acikin dan madaidaicin filet hajiya kubra ta zuba musu abincin, tuwon semo miyar danyar kubewa,
"Hafsat zo muci abincin.."
Matsawa hafsa tayi tasa hannu ita a zatonta iya ita da hajiya kubran ne kadai zasuci amma sai taga sabanin haka domin shima alhajin saka hannu yayi saboda al'adarsu tare suke cin abincin tare dashi da hajiya da amal, Hafsat ji tayi kaunarsu ta fara darsuwa acikin zuciyarta, duk da cewar taki dan sakin jiki dasu amma hajiya kubra sai sakota take acikin hirar tasu dahaka suka kammala cin abincin.
Suna falon alhaji sa'id azaune har misalin karfe 9 nadare lokacinne hajiya kubra ta mike ta kalli Hafsat,
"Hafsa taso muje ki kwanta naga kamar bacci kikeji ko?"
Dan murmushin yake Hafsat tayi ta tashi ta kalli alhaji sa'id,
Dan rissinawa tayi, "Alhaji saida safe"
Cikeda fara'a ya amsa tabi bayan hajiya kubra suka fita,
"Abba zaki rinka cewa alhaji kinji, nikuma ummi saboda haka amal ke kiranmu, kinga tunda yanzu kema mune iyayenki.."
Hajiya kubra tace da ita akan hanyarsu ta zuwa part dinta,
"Tohh Ummi.."
Dadi hajiya kubra taji jin Hafsat ta kirata da Ummi,
Sai da safe Hafsat tayiwa hajiya kubra tashiga daki,zama tayi akan gado tana mai bin dakin da kallo.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*13*
aishaummi.blogspot.com
***Kasa bacci Hafsat tayi illa tunanin rayuwarta da take ta faman yi,
Ji tayi kamar ta fashe da kuka a sakamakon fadowa ranta da kawarta Amina tayi,
Duk da tasan abin atayata farin cikine saboda canjin rayuwar data samu amma duk da haka tana jin radadi acikin zuciyarta na rabuwa da gidan marayu da tayi domin tariga da ta saba da mutanen ciki,
Wadannan tunane tunanen da tarinka yi sune suka hana idonta bacci har aka fara kiran assalatu, a kunnenta aka shiga sallar asubah nan ta tashi tashiga bathroom ta dauro alwala tafito, salla tayi tareda addu'o'i masu yawan gaske, anan inda tayi sallar anan bacci ya kwasheta.
Misalin karfe shida da rabi na safe hajiya kubra ta shiga cikin dakin ganinta kwance tana bacci yasata juyawa tafita batare data tasheta ba domin ta fahimci cewar tayi sallar asubah,
Hafsat dai bata samu damar tashi daga wannan baccin ba mai cikeda mafarkai iri iri wadanda takasa tuno koda guda daya daga ciki lokacin data farka, ba ita tatashi ba sai misalin karfe 10 zuwa da rabi, hajiya kubra kuwa ta leka dakin yafi sau akirga,
Zama tayi tana bin dakin da kallo kamar yanzu ne tashigo ciki, daga bisani ta sauke idonta kasa ta mike, fita tayi acikin falo ta hango hajiya kubra tasha kwalliya cikin wata shadda kamfala tana faman jejjera abin Karin kumallo akan dining table,
Sam hajiya kubra bataji fitowarta ba har saida tayi magana,
"Ummi ina kwana.."
Cikeda farin ciki hajiya kubra ta juyo ganin Hafsat atsugunne yasata kamo kafadunta ta tada ita tsaye tana murmushi,
"Lafiya lau Hafsat, sai yanzu aka tashi? Ai na shisshiga dakin kinata bacci"
Murmushin yake Hafsat tayi,
"Ummi akwai abinda za ayi ne?"
"Kamar mefa Hafsa na?"
"Na aikin gida.."
"A'a Hafsa babu abinda za ayi, har ankammala gyara gidan ai, inada ma'aikata na masu yimin komai da kika sani, girki ne kadai nake yin abuna dakaina, yanzu kije kiyi wanka ki shirya ki fito mu karya lokacin abbanku shima ya fito"
"Toh" ta amsa tareda juyawa takoma cikin daki, wanka tayi ta shirya ta fito zuciyarta cikeda mamaki na irin tarba da soyayyar da hajiya kubra ke nuna mata wadda abisa dukkan alamu zata riketa amana kamar itace ta haifeta,
Atamfa ta saka dinkin riga da zanine pieces kalar atamfar kalar ruwan hoda, hijabinta da tazo dashi tasa ta fita,
Lokacin data fita tuni har su hajiya kubra sun hau kan table suna jiranta, durkuwa tayi tagaida Alhaji sa'id,
Fuska asake ya amsa gaisuwarta yakare maganar da fadin,
"Tashi, tashi, zo ga kujera ki zauna"
Mikewa tayi taje ta zauna akusa da hajiya kubra wacce tafara kokarin hadawa Alhaji tea,
"Hafsa babu wasu hijaban ne akayan amal naga kinata saka wannan?"
"A'a ban duba ba"
"To ai kuwa inajin tabar hijabai dan bata tafi da komai nataba duk agida tabarsu..."
"Ashe yar uwarta tabarwa bata saniba" Alhaji sa'id ya karbe zancen,
Dariya hajiya kubra tayi,
"Ai so nake idan ta sai sim ta kira inyi mata albishir"
"To ai kuwa da dai nine naso inyi albishir dinnan amma naga kina nema ki rigani.."
Dariya sukayi dukkaninsu inbanda Hafsat wacce dan murmushi kawai tayi,
Abinsu gwanin sha'awa suna karyawa suna hirarsu har suka kammala nan Alhaji sa'id ya mike yana gyara babbar rigar dake jikinsa domin wurin aiki zai fita,
"Adawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya" Hafsat tace dashi tana rakube ajikin kujera,
"Amin Hafsat, nidai abinda nakeso dake shine ki saki jikinki ki dauka cewar nan gidanku ne sannan kuma mu iyayenki ne, kinji? Allah yayi miki albarka"
"Amin, amin..." Hajiya kubra ta amsa tana murmushi,
Juyawa yayi yafita hajiya kubra tana biye dashi ganin haka yasa hafsat tattare kayan da sukayi amfani dasu wurin karyawa ta nufi kitchen, tana tsaka da daurayesu hajiya kubra ta dawo daga rakiyar da ta yiwa alhaji,
"Ahh hafsat ai ban sakiba, waye yace ki wankesu? Nafada miki akwai masu aiki zasu yi har wanke wanken"
"Babu komai Ummi nima gani nayi babu abinda zanyi shiyasa nace bari in wanke.."
"Ikon Allah..." Tafada ahankali tana mai sake dauko wani hoton tafara kallo, nan ta lalace wurin kallon hoton batare data kosa ba.
Kasa koda zama hajiya kubra tayi illah kaiwa da kawowa da take ta faman yi dan tsananin farin ciki, tabbas wannan wani al'amari ne daga Allah Wanda shi kadai yabarwa kansa sani,
Ganin zama yagagara yasata fita ta nufi part din alhaji, shima shigowarsa kenan daga masallacin dake kofar gidansa,
Zama tayi akan kujerar dake makotaka da tashi,
"Alhaji nidai kaganni tsabar farin ciki nakasa zaune nakasa tsaye.."
Murmushi alhaji sa'id yayi,
"To in banda abinki hajiya menene abin kasa tsaye da kasa zaune? Yanzu ina ita yarinyar take?"
"Alhaji dole inkasa zaune in kasa tsaye mana,ai farin cikin da nake ciki bazai barni inyi hakaba, tace min sunanta hafsat, tana can dakin amal nakaita tayi wanka ta shirya sai tafito muyi dinner.."
"Hakan yayi daidai hajiya kubra,nidai abinda nakeso dake shine dan Allah ki rike yarinyar nan bisa amana duk danasan zaiyi wuya ki gallaza mata tunda bata da maraba da amal to amma wani lokacin ku mata ana ganin kamar kunfi kowa tausayi da rauni sai dai akan gallazawa yaran da ba nakuba kunfi kowa nuna rashin tausayi da rashin rauni, dan Allah ki riketa amana tunda kinga daga gidan marayu na daukota wannan yana nuna cewar ita maraya ce..."
"Haba alhaji ai basai kayi min wannan nasihar ba domin ko wanine yakawo min wannan yarinyar wanda bakai ba wallahi zan kula da ita..."
"Nasani hajiya kubra, Allah yayi miki albarka, yanzu ina tunanin ai tagama ko?"
"Ehh to bari indubo ingani"
Tashi tayi tafita takoma part dinta, dakin amal ta tura tashiga nan ta iske hafsat zaune ta kurawa hotunan amal ido ko kifawa bata yi,
"Hafsat..." Ta kira sunanta bayan takarasa kusa da ita, dagowa hafsat tayi ta kalleta,
"Na'am"
"Ya bakiyi wanka kin canja kayan jikinki ba? Tashi ki shiga bathroom kiyi wanka indan kin fito ga drewar din kayan amal nan ki duba duk wanda yayi miki kisaka.." Ta karasa zancen tana nuna mata drewar din da dan yatsanta,
"To" hafsat ta amsa har lokacin tana cike da mamaki domin ganin abubuwan dake faruwa take yi tamkar acikin mafarki,
Fita hajiya kubra ta sake yi ganin haka yasa hafsat tashi ta shiga cikin bathroom din, komai wanda ake bukata akwaishi acikin bathroom din babu bata lokaci tayi wanka ta fito, man da zata dan shafawa fatarta ta shiga nema domin duk wadanda ke kan dressing mirror din lotion ne dan haka dakyar tasamu wani me dan kama da Vaseline tashafa,
Gaban drewar taje ta bude nanfa mamaki yacikata domin kayane iya ganinta shake acikin drewar din,
Wata doguwar riga kalar ruwan hanta ta zaro da dan kwalinta tasaka ta dauki hijabinta tayi salla,tana saman abin sallar azaune a inda aka kebe musamman domin yin salla hajiya kubra tasake shigowa fuskarta dauke da murmushi,
"Hafsa kin idar ne?" Tajiyo muryar hajiya kubra na tambayarta,
"Ehh na idar.." Tabata amsa tana kokarin mikewa,
"Yawwa to taso kizo muje wurin alhaji"
Bin bayanta tayi suka fita, tiryan tiryan tana biyeda ita har suka shiga falon alhaji sa'id Wanda ke zaune yana kallon labarai a tauraron dan adam,
Ganinsu yasashi rage volume din tv din ya fadada murmushinsa yana kallonsu domin sai yake ganin kamar hajiya kubra ce da amal suke dososhi kamar yadda suka saba akowanne dare domin yin hira,
"Alhaji...,labarai kake kallo?"
"Wallahi kuwa hajiya, keda 'yar takine?"
"Ehh amma har yanzu dai banga alamar zata sake ta saki jiki damu ba saboda ganinmu take baki agareta" hajiya kubra tafada fuskarta da yar damuwa,
"To wannan kuma dama ai sai ahankali,kin san ai yau tafara ganinmu,sai asannu ko Hafsat?" Yakarasa zancen cikin barkwanci,
Hafsat kam shiru tayi takasa koda kallonsu, sai dai wani lokacin ta dan saci kallonsu ahaka har lokacin sallar isha yayi nan alhaji sa'id yafita masallaci yabarsu a cikin falon nashi,
Anan Hafsat da hajiya kubra sukayi sallarsu,suna nan zaune har alhaji sa'id yadawo dan haka hajiya kubra ta mike domin gabatar musu da abincin dare,
"Hafsat zo muje kitchen.."
Mikewa Hafsat tayi suka fita zuwa cikin kitchen wanda kallo kawai Hafsat ta bude ido tanayi saboda ita ba taba ganin irin shi tayiba,
Akan babban faranti hajiya kubra ta jera flasks din abincin nan Hafsat din ta karba ita kuma hajiya kubra ta debi filet da sauran abubuwan da suka kamata,
Zama Hafsat tayi bayan ta ajiye farantin, acikin dan madaidaicin filet hajiya kubra ta zuba musu abincin, tuwon semo miyar danyar kubewa,
"Hafsat zo muci abincin.."
Matsawa hafsa tayi tasa hannu ita a zatonta iya ita da hajiya kubran ne kadai zasuci amma sai taga sabanin haka domin shima alhajin saka hannu yayi saboda al'adarsu tare suke cin abincin tare dashi da hajiya da amal, Hafsat ji tayi kaunarsu ta fara darsuwa acikin zuciyarta, duk da cewar taki dan sakin jiki dasu amma hajiya kubra sai sakota take acikin hirar tasu dahaka suka kammala cin abincin.
Suna falon alhaji sa'id azaune har misalin karfe 9 nadare lokacinne hajiya kubra ta mike ta kalli Hafsat,
"Hafsa taso muje ki kwanta naga kamar bacci kikeji ko?"
Dan murmushin yake Hafsat tayi ta tashi ta kalli alhaji sa'id,
Dan rissinawa tayi, "Alhaji saida safe"
Cikeda fara'a ya amsa tabi bayan hajiya kubra suka fita,
"Abba zaki rinka cewa alhaji kinji, nikuma ummi saboda haka amal ke kiranmu, kinga tunda yanzu kema mune iyayenki.."
Hajiya kubra tace da ita akan hanyarsu ta zuwa part dinta,
"Tohh Ummi.."
Dadi hajiya kubra taji jin Hafsat ta kirata da Ummi,
Sai da safe Hafsat tayiwa hajiya kubra tashiga daki,zama tayi akan gado tana mai bin dakin da kallo.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*13*
aishaummi.blogspot.com
***Kasa bacci Hafsat tayi illa tunanin rayuwarta da take ta faman yi,
Ji tayi kamar ta fashe da kuka a sakamakon fadowa ranta da kawarta Amina tayi,
Duk da tasan abin atayata farin cikine saboda canjin rayuwar data samu amma duk da haka tana jin radadi acikin zuciyarta na rabuwa da gidan marayu da tayi domin tariga da ta saba da mutanen ciki,
Wadannan tunane tunanen da tarinka yi sune suka hana idonta bacci har aka fara kiran assalatu, a kunnenta aka shiga sallar asubah nan ta tashi tashiga bathroom ta dauro alwala tafito, salla tayi tareda addu'o'i masu yawan gaske, anan inda tayi sallar anan bacci ya kwasheta.
Misalin karfe shida da rabi na safe hajiya kubra ta shiga cikin dakin ganinta kwance tana bacci yasata juyawa tafita batare data tasheta ba domin ta fahimci cewar tayi sallar asubah,
Hafsat dai bata samu damar tashi daga wannan baccin ba mai cikeda mafarkai iri iri wadanda takasa tuno koda guda daya daga ciki lokacin data farka, ba ita tatashi ba sai misalin karfe 10 zuwa da rabi, hajiya kubra kuwa ta leka dakin yafi sau akirga,
Zama tayi tana bin dakin da kallo kamar yanzu ne tashigo ciki, daga bisani ta sauke idonta kasa ta mike, fita tayi acikin falo ta hango hajiya kubra tasha kwalliya cikin wata shadda kamfala tana faman jejjera abin Karin kumallo akan dining table,
Sam hajiya kubra bataji fitowarta ba har saida tayi magana,
"Ummi ina kwana.."
Cikeda farin ciki hajiya kubra ta juyo ganin Hafsat atsugunne yasata kamo kafadunta ta tada ita tsaye tana murmushi,
"Lafiya lau Hafsat, sai yanzu aka tashi? Ai na shisshiga dakin kinata bacci"
Murmushin yake Hafsat tayi,
"Ummi akwai abinda za ayi ne?"
"Kamar mefa Hafsa na?"
"Na aikin gida.."
"A'a Hafsa babu abinda za ayi, har ankammala gyara gidan ai, inada ma'aikata na masu yimin komai da kika sani, girki ne kadai nake yin abuna dakaina, yanzu kije kiyi wanka ki shirya ki fito mu karya lokacin abbanku shima ya fito"
"Toh" ta amsa tareda juyawa takoma cikin daki, wanka tayi ta shirya ta fito zuciyarta cikeda mamaki na irin tarba da soyayyar da hajiya kubra ke nuna mata wadda abisa dukkan alamu zata riketa amana kamar itace ta haifeta,
Atamfa ta saka dinkin riga da zanine pieces kalar atamfar kalar ruwan hoda, hijabinta da tazo dashi tasa ta fita,
Lokacin data fita tuni har su hajiya kubra sun hau kan table suna jiranta, durkuwa tayi tagaida Alhaji sa'id,
Fuska asake ya amsa gaisuwarta yakare maganar da fadin,
"Tashi, tashi, zo ga kujera ki zauna"
Mikewa tayi taje ta zauna akusa da hajiya kubra wacce tafara kokarin hadawa Alhaji tea,
"Hafsa babu wasu hijaban ne akayan amal naga kinata saka wannan?"
"A'a ban duba ba"
"To ai kuwa inajin tabar hijabai dan bata tafi da komai nataba duk agida tabarsu..."
"Ashe yar uwarta tabarwa bata saniba" Alhaji sa'id ya karbe zancen,
Dariya hajiya kubra tayi,
"Ai so nake idan ta sai sim ta kira inyi mata albishir"
"To ai kuwa da dai nine naso inyi albishir dinnan amma naga kina nema ki rigani.."
Dariya sukayi dukkaninsu inbanda Hafsat wacce dan murmushi kawai tayi,
Abinsu gwanin sha'awa suna karyawa suna hirarsu har suka kammala nan Alhaji sa'id ya mike yana gyara babbar rigar dake jikinsa domin wurin aiki zai fita,
"Adawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya" Hafsat tace dashi tana rakube ajikin kujera,
"Amin Hafsat, nidai abinda nakeso dake shine ki saki jikinki ki dauka cewar nan gidanku ne sannan kuma mu iyayenki ne, kinji? Allah yayi miki albarka"
"Amin, amin..." Hajiya kubra ta amsa tana murmushi,
Juyawa yayi yafita hajiya kubra tana biye dashi ganin haka yasa hafsat tattare kayan da sukayi amfani dasu wurin karyawa ta nufi kitchen, tana tsaka da daurayesu hajiya kubra ta dawo daga rakiyar da ta yiwa alhaji,
"Ahh hafsat ai ban sakiba, waye yace ki wankesu? Nafada miki akwai masu aiki zasu yi har wanke wanken"
"Babu komai Ummi nima gani nayi babu abinda zanyi shiyasa nace bari in wanke.."