← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 30

Sashe 11

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari da safe misalin karfe 11 daidai nasafe mami tayiwa gidan sammako lokacin Alhaji sa'id na nan ko fita baiyiba,

Jin zuwanta yasa Hafsat jin wata irin faduwar gaba duk sai taji jikinta yayi sanyi dan dakyar ma ta iya zuwa suka gaisa daga nan ta koma daki ta kule bayan ta gabatar mata da ruwa,

"Hajiya kubra yau dai zuwana yasha banban da wanda nakeyi ada domin dalilin zuwana yau shine neman auren yata nazo.. Wato Hafsat"

Murmushi hajiya kubra tayi ta kalli mami,

"To ai bakiyi min gwari gwari yanda zan ganeba"

"Kamar yadda nafada miki nazone in nemarwa dana yusleem auren yarki Hafsat idan har babu alkawarin wani akanta domin wallahi ina mutukar kaunarta kuma ina son inhada jini da ku.."

Murmushi hajiya kubra tayi,

"To ai kema yarkice, amma yanzu abinda nake ganin za ayi shine abbanta yana nan bai fitaba bari inje insanar masa"

"To shikenan"

Tashi hajiya kubra tayi tafita zuwa part din Alhaji sa'id mintuna Kadan sai gata tadawo,

"Hajiya to bismillah zo mu karasa wurin alhajin"

Tare suka shiga suka iskeshi zaune kan kujera hannunsa rikeda jaridar weekly trust,

Gaisawa sukayi da mami tayi masa bayani kamar yanda tayiwa Ummi nan Alhaji sa'id yace babu komai indai har Hafsat din ta amince domin ba za ayi mata doleba kawai abinda za ayi shine suje su daidaita ita da yaron,

Cikeda farin ciki mami tayiwa Alhaji sa'id godiya ta mike tafita acikin ranta tana ganin yanzu saura abu daya yarage shine tashawo kan yusleem....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*21*

***Falon hajiya kubra mami takoma tazauna tana jiranta zuciyarta cikeda farin ciki wanda kana iya gane hakan karara idan har ka kalli kan fuskarta,

Tana nan zaune har ummi tafito daga sashen alhaji nan sukayi sallama ta rakata tatafi, saida Hafsat taji fitar mami sannan tafito daga daki tazauna akusa da ummin tana dan kallonta domin jin karin bayani amma kuma sai dai kunya takeji,

"Mamin naku tatafi yanzu nakaita wurin abbanku sunyi magana akanki keda danta, abbanki yace yaron yazo ku daidaita mutukar kun amince kuna son juna to shi bashida wata matsala..."

Shiru Hafsat tayi ta dan sunkuyar da kanta kasa tana murmushi,

"Nida naso kema kiyi karatu kamar yar uwarki amal to amma kin san kowa da yadda Allah yake tsara masa rayuwarsa.., sai dai muyi fatan Allah yasa hakan shine yafi alkhairi"

Har dai ummi tayi maganarta tagama Hafsat bata iya cemata ko uffan ba.

Cikin farin ciki marar misaltuwa mami taje gida tana shiga ta nemi wurin zama ta zauna tafara lissafin abubuwan da ya kamata ta siyo ko ta hado domin bata bukatar bikin nan yawuce watanni biyu masu zuwa kacal,

Paper da pen ta dauko ta zauna tana rubuta abubuwan da takeso tasiyo da adadinsu,

Yusleem ne yaturo kofar falon ya shigo yana sanye da farar riga jersey da blue din trouser hannunshi rike da key din motarshi,

A kusa da mamin ya zauna ya jingina kamar yadda yasaba domin shi haka dabi'arshi take kamar wani mai sarauta akoda yaushe cikin iko yake,

"Mami ina kwana..?"

Dagowa tayi ta kalleshi bayan tacire farin medical glass din dake kan fuskarta,

"Sai yanzu katashi ko? In ba hakaba yaushe za akira karfe 12 da safiya..." Takarasa maganar tana murmushi,

"To ai mami weekend ne.."

"Ehhh tunda weekend ne sannan kuma kai kadaine baka da mata ai dole kayita bacci har rana ta fito"

Murmushi yayi yana shafa kasumbar dake fuskarshi,

"Mami yunwa nakeji wallahi dan yunwar ce ma tafito dani daga gida"

"To me zakaci?"

"Abani tea banda bread, soyayyiyar agada da dankali amma banda egg"

Murmushi Mami tayi tana kallonsa,

"Ai matarka zata sha tsaraba kai idan katashi karyawa baka karyawa da abu guda biyu kuma abin haushinma idan anbaka ba na kirki zakaci ba"

"Mami wallahi nima ina son infara cin abinci dayawa amma narasa meyasa bana iyawa, but ina tunanin nanda 2 weeks zanje london so zan biya ta chairo naga dr dina"

"Da dai yafi maka amma mutum yarinka cin abinci kamar wani karamin yaro..."

Bai kara maganaba yaciro wayarshi daga aljihu yasoma latsawa, mikewa mami tayi tafita takira kuku ta fada masa aikin da zaiyi tadawo wurin yusleem tazauna,

"Wai mami rubuce rubucen me kikeyi ne haka?"

"Ai zan fada maka, kwantar da hankalinka.."

Murmushi yayi yatashi yakoma kan 3 sitter ya kwanta,

Mintuna kadan kuku yashigo dauke da faranti wanda ya dorowa yusleem kayan breakfast din akai,

Akan center table ya dora mishi yajuya yafita, tashi yusleem yayi yaja table din gabanshi ya hada tea yasoma karyawa yanayi yana kallon mami wacce ta dukufa akan rubutun da takeyi,

Saida ya kammala sannan mami ta dago ta kalleshi,

"Yusleem ya maganar auren da nace ka nemo, har yanzu baka samo yarinyar da tayi maka ba ko kuma yaya?"

Dama tun shigowarshi saida jikinsa yabashi maganar aure mami zatayi masa,

Sai da yadan ja lokaci sannan yace,

"Mami meya faru kuma?"

"Babu abinda yafaru inaso ne inji idan har kasamo sai afara maganar auren idan kuma baka samoba to ni nasamo maka..."

Sunkuyar dakanshi yayi yana nazari batare da yace komai ba, tabbas shikam yanada farin jinin yanmata domin babu wahala yanzun nan budurwa tace tana sonshi sai dai kuma sam shi baya bukatar auren ne,

"Yanaji kayi shiru?"

"To mami ai nazaci mun gama maganar nan"

"Dawa? A'a bamu gamaba, nidai ina son kasani nasamo maka yarinyar da zaka aura nanda watanni biyu dan haka saika fara dukkan shirye shiryen da yadace amma wannan karon kasani banyi maka aure dan ka sakar musu yarinya ba,

Sannan kuma inaso ka sama mana visa mutafi umarah domin muje inyi maka addu'a akan Allah yarabaka da wannan aljanar da take tareda kai kuma yasa ayi auren nan cikin sa'a yasaka albarka aciki"

Tunda mami tafara maganar baice uffan ba har tagama,

"Ina fata kaji maganganun da nayi maka kuma sun shiga cikin kunnenka?"

"Ehh naji"

"Yawwa to Allah yayi maka albarka Allah yasa ayi cikin nasara"

Bai amsaba yatashi yafita mami tarakashi da ido,

Kamar yadda mamin tafada acikin lokaci kankani yasamo musu visa suka tafi umarah addu'a sosai mami tayi masa kan auren da zatayi masa bayan sun kammala umarah ne yawuce London yabarta anan bayan tafiyarshi da kwana uku itama tawuce dubai domin karasa hada lefenshi da siyan sauran abubuwan da za ayi amfani dasu abikin dan hatta kayan da amarya zata saka duk saida tasai mata,

Saida ta kammala siyayyarta tsaf sannan tadawo Nigeria shikuwa yusleem har lokacin bai dawoba, dawowarta babu jimawa tatura wakilan yusleem sukaje nemar masa auren Hafsat agidan Alhaji sa'id wanda basu tahoba saida ranarsu, domin Alhaji sa'id ya yanke ranar aure saboda ya fahimci cewar Hafsat din tana son yusleem,

Wannan abu ba karamin dadi yayiwa mami ba dan tsananin dadi aranar da daddare taje gidan tayi godiya,

Aminanta da kawayenta ta gayyato suka kai lefen Hafsat wanda tsayawa fadar kayan ciki bata lokaci ne, domin mami ta yiwa Hafsat lefe na alfarma irin lefen da tunda yusleem yake aure ba ataba yin irinshi ba,

Yanzu gidajen guda biyu ko ina shirin biki sukeyi gadan gadan, Alhaji sa'id ya sakarwa ummi kudi domin yiwa yartata siyayya, ita dai Hafsat bata katabus saboda har yau bataga angonba kuma shima bai gantaba tana jin tsoron kar yaganta ya rainata yace batayi masa ba domin tasan dama auren hadin mami ne,amma shikam bata tunanin akwai wata ya macen da zata ce baiyi mataba,

Yusleem kuwa tunda ya Lula yatafi bai dawoba gyaran gidanshi ma wanda za ayi sai yaronshi na office yasa yatsaya akai akayi aka gama aka gyara gidan tsafa aka sake fenti,

Saida biki yarage saura kwana takwas sannan yadawo lokacin hatta kannenshi su Abdul da surayya har sun zazzo daga makaranta, mami taso tayi masa fada amma kuma dayake acikin farin ciki take sai ta shareshi taci gaba da harkokinta,

Surayya kam kanwar yusleem tattarawa tayi takoma gidansu Hafsat saboda acewarta ita abangaren amarya take ba bangaren ango ba, Hafsat ba karamin dadi tajiba domin dama ita kadaici kwal agidan take harkokinta domin Alhaji sa'id bai bar amal tazo ba duk da tayi niyyar zuwa amma yahana,

Surayya ce taraka Hafsat akayi mata komai kama tun daga kunshi gyaran jiki da gyaran kai wanda duk mami ce tadauki nauyin yin hakan,

Ana igobe daurin aure yusleem yaje gidansu Hafsat din wanda wannan dinma mamice ta tilastashi, kamar zaiyi kuka yashirya yatafi bayan sallar isha,

Surayya yayiwa waya tana dauka taji yace,

"Ke turo min wannan yarinyar"

Sarai surayya tagane abinda yake nufi amma sai tayi fuska tace,

"Uhm yaya wafa?"

"Oho miki" yafadi tareda katse wayar,

Kallon Hafsat tayi tana murmushi,

"Angonki ne yazo yana waje yana jiranki"

Saida gaban hafsa yafadi saboda jin abinda surayya tace,hijabi tadauka ta kalli surayya,

"Zo ki rakani dan Allah"

"Zan dai kaiki amma ina zuwa dawowa zanyi"

"Nayarda"

Fita sukayi gaba dayansu, afalo suka iske su ummi ita da jama'arta wadanda sukazo suna yan aikace aikace,

Kanshi yana durkushe akasa yana latsa wayarsa dan haka ko fitowarsu bai ganiba bare yaga zuwansu, surayya ce ta kwankwasa masa glass din dake saitinshi hakan yasashi yin kasa da glass din yana kallonta, gaban Hafsat ne yashiga dukan tara tara haka kawai domin gani tayi yusleem yafi kyau afili kuma tabbas shine mutumin da yake taimaka musu lokacin da tana gidan marayu domin yataba zuwar musu sau daya sun ganshi,

"Ina wuni.." Hafsat tace dashi tana kallon kasa,

Ko kallonta baiyiba ya amsa da "lafiya"

Daga haka babu wanda yakara magana acikinsu ganin haka yasa surayya tajuya zata tafi dominated tabasu wuri nan yadakatar da ita yadauko rafar yan dubu dubu guda daya ya mika mata yaja motarshi yayi gaba,

Hafsat ji tayi ko ajikinta balle abin ya dameta,

Washe gari aka daura auren Hafsat da yusleem da misalin karfe 2 narana akan sadaki naira dubu hamsin.

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*22*
Chapter 11 · 0% Book details