Sashe 14
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi tayi taje ta zubo abincin tadawo ta zauna tana cin abincin tana kallo, tun da yafita kuma shikenan bata sake jin duriyarsa ba har akayi kwana biyu,
Jin shirun yayi yawa yasata nufar part dinshi domin dubashi,
Lokacin da ta shiga atsaye taganshi gaban mirror yana gyara necktie din da yasaka da alama shirin fita yakeyi domin lokacin karfe 9:30 nasafe,
Sallama tayi ya amsa mata aciki ciki batare da ya kalleta ba,
"Ina kwana yaya.."
"Lafiya" yabata amsa,
Shiru tayi ta tsaya tana kallonshi, sanye yake cikin bakaken suit yasaka blue din t shirt mai kwala ta ciki,
Agogon azurfa na Gucci yadauka ya daura ahannunshi yafesa turare ya zo ya raba ta gefenta yawuce batare da yayi mata magana ba,
"Adawo lafiya..." Tafada ganin yayi hanyar fita,
Bata fita daga cikin dakinba saida ta gyarashi ta wanke toilet ta goge ko ina sannan ta rufe tafita,
A falonta tasamu surayya baje tana jiranta,
"A'a saukar yaushe?"
"Jiyan nan nadawo shine naga bazan iya zamaba har sai nazo naganki"
"Sannu da dawowa, kin jima da zuwane?"
"Ehh to nadai fi 20 minutes amma abinda yasa ban damuba shine naga kina turakar mai gida..."
Murmushi Hafsat tayi mai ciwo,
"Surayya yaya yusleem narasa wanne irin mutum ne shi wanda sam bai damu da iyalinsa ba..."
Katseta surayya tayi,
"Da jira kikeyi yadamu dake? Tab ai bari kiji wallahi garama ki tashi daga wannan dogon barcin da kikeyi domin yaya yusleem yanada manyan matsaloli,
Bafa akanki yafara aureba kuma wallahi sakin mata yake, auri saki gareshi dan babu wacce ya taba aura tayi shekara agidansa shiyasa nake son ki zage ki kamashi ahannu dumu dumu kuma wallahi karki raga masa ki azabtar dashi idan kika tsaya jin tausayinsa kika raga masa sunanki sorry domin shi azabtar dake zaiyi..."
Jin abinda surayya tace ai Hafsat bata San lokacin data zamo daga kan kujerar da take zaune ba tadawo kasa,
"Auri saki fa kikace?"
"Tabbas domin ya auri mata sunfi goma sha..."
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un.."
"A'a nifa ba fada miki nayi dan ki tada hankalinki ba, kawai fada miki nayi dan ki tashi atsaye kisan duk yanda zakiyi ki karkato da hankalinsa gareki"
Tagumi Hafsat tayi tana lazimi acikin zuciyarta......
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*25*
***Tagumi Hafsat tayi tai shiru tama rasa abin cewa domin bata san ta inda zata faraba,
"Baiwar Allah karki tashi hankalinki, nidai kawai abinda nakeso kisani shine yaya yusleem fa ba dutse bane mutum ne dan haka duk taurin kansa wata rana dole ya bukaci mace, dan haka daurewa zakiyi ki zage kiyita shisshige masa har yazo hannu kin gane ai?
'Yar rangwadar nan, kwalliyar nan, tsabtar nan..." Surayya tafada tana dariya,
Kallonta Hafsat tayi idanuwanta har sunyi ja,
"Surayya kenan da alama baki gama fahimtar yayan naki ba, yaushe ma ya zauna agidan bare har insamu damar yi masa wadannan abubuwan? Kedai kawai Allah yabani mafita"
"Amin, zaima baki cikin ikonsa"
Haka suka cigaba da tattauna maganar har tsawon wani lokaci,yauma kamar koda yaushe saida da daddare sannan surayya taja motarta ta tafi,
Tafiyarta yasa Hafsat jin gidan yayi mata tsittt, part din yusleem ta shiga baya cikin falon dan haka ta nufi bedroom dinshi nan dinma baya ciki, har zata fita tajiyo motsin ruwa acikin toilet alamun wanka yake nan tajuya tafita,
Bata kara sashi a idonta ba tun daga ranar,dan haka kullum wunin kadaici takeyi wannan dalilin ne yasa tayiwa Ummi waya tace a Kawo mata keken sakarta domin ko babu komai zai rinka dan debe mata kewa idan babu abinda takeyi sai tarinka hawa tanayi,
Washe gari hajiya kubra taje gidan takai mata keken da sauran kayan da zatayi amfani dasu wurin sakar, wannan shine karo nafarko da ummin taje gidan nata shiyasa murnarta takasa boyuwa,
Ita ason ranta ma ummin ta zauna ta wuni amma fur taki ko minti talatin batayi ba tatashi zata tafi,
Bin bayanta Hafsat tayi ta rakata anan hajiya kubran ke fada mata cewar ai yusleem sau biyu yana zuwa gida gaishesu bayan bikin, mamaki ne ya kama hafsa saboda bata zaci zai iya zuwaba duk da tafi zaton cewar mami ce zata tilasta shi yaje, sallama sukayi da ummin tatafi ita kuma takoma cikin gida.
Samun keken sakar nan akusa da ita shine dalilinta yanzu na rage zaman tunani duk da wani lokacin tana ganin anya kuwa rayuwarsu ita da yusleem zata yiyu ahaka? A matsayinsu na mata da miji ace sai suyi kwana 3 basu ga junaba, sannan bai damu da yaci abincinta ba balle har magana ta shiga tsakaninsu,
Gama wannan tunanin keda wuya ta mike ta nufi falonshi, baya ciki dan haka takarasa dakin baccinsa can dinma baya nan amma ga laptop dinshi nan a ajiye akan gado, karasawa tayi ta dauke laptop din ta gyara gadon daga nan ta zarce da gyara dakin gaba daya,
Bathroom tashiga nan taga ya jika kananan kayanshi acikin bocket da dukkan alamu so yake su jiku yasa acikin washing machine yawanke domin tasan bazai taba yin wanki da kansa ba tunda itama da ba kowan kowaba an ajiye mata injin wankin sai dai ita bata ma fiya amfani dashiba tafi ganewa tayi abinta da kanta,
Tsayawa tayi ta wanke masa kayan tass tadauka tafita ta shanya, tana cikin shanyawa yadawo yana sanye da kananan kaya jeans da t shirt,
Binshi cikin falon tayi bayan ta kammala shanyar kayan,
"Sannu da zuwa..."
"Yawwa..." Ya amsa mata aciki ciki daga nan bai kara koda kallon bangaren da takeba bare tasa ran zaiyi mata sannu na aikin da tayi masa,dan haka tawuce takoma part dinta,
Wadannan abubuwan dake faruwa sune suka hanata bacci adaren yau har misalin karfe daya idonta biyu, tanata juyi tajiyo kamar alamun tafiya atsakar gida a tsorace ta tashi taje gaban window ta daga labule tafara lekawa ahankali, kasancewar tsakar gidan akwai haske tal kamar rana shiyasa tasamu damar hango yusleem din wanda ke kokarin bude kofar motarshi,
"Ina yaya yusleem zaije acikin daren nan?" Ta tambayi kanta,
Kafin ta iya bawa kanta amsa tuni har yashiga motar mai gadi ya bude masa yafice, ita tsoro ne ma ya kamata domin duk atunaninta agidan mami ne wani abu yafaru nan takoma ta zauna jugum tanata nazari amma motsi kadan sai tatashi ta leka ko yadawo amma shiru,
Haka takasa bacci sai sake sake da haka har asubah tayi a lokacin ne taji dawowarshi da kamar taje wurinshi taji abinda yafaru sai dai tafasa,alwala taje ta dauro tazo ta tada salla.
Misalin karfe 8 tashiga falonshi bayan taci kwalliya cikin wata dark purple din shadda,
Kwance ta sameshi yana bacci akan doguwar kujera yana sanye da farar t shirt da bakin boxer, karasawa dakinshi tayi ta gyara masa tafito, lokacin da ta fito kuma yana zaune yana danna wayarshi, gaisheshi tayi ya amsa daga nan yaci gaba da abinda yake yi, jin baice mata komai ba yasata fita takoma falonta taci gaba da harkokinta,
Tana kan kekenta tana karasa hada rigar data fara jiya taji sallamar Amina kawarta, da murna ta tari aminan wacce ke daga kafa dakyar domin cikinta yadan fara tsufa,
Ba karamin dadin ganin aminan tajiba nan suka baje a falonta suka hau hirar yaushe gamo, wuni cur Amina tayi mata sai yamma ta tafi,
Haka taci gaba da zaman kadaici agidan domin surayya ma takoma makaranta kuma bazata sake dawowa ba har saita kammala, yau watanta biyu da wani abu agidan kuma tunda tazo bata taba fitaba shiyasa yau ta kuduri niyyar tambayarshi zuwa ganin gida,
Yana kokarin fita tayi gaggawar tsayar dashi, tsayawa yayi batare da yajiyo ba,
"Yaya dama yau ina son zuwa gidanmu ne"
"Allah kiyaye hanya, idan kin shirya akwai driver"
Daga haka yayi gaba abinshi, shiryawa taje tayi tafito tana dauke da rigunan jariran da ta saka wanda zata tafi dasu takaiwa Ummi domin asayar mata,
Kamar yadda yusleem yace haka ta tarar da driver yana zaman jiranta nan ya dauketa yakaita gida, murna wurin hajiya kubra abin ba acewa komai nan tashiga yin nan nan da ita, Hafsat ba ita tabaro gidanba sai dare domin saida tajira alhaji sa'id yadawo suka gaisa,
Daren yauma kamar rannan kasa bacci tayi can taji fitar yusleem daga gidan agogo ta kalla karfe 2 saura na dare,
"To wai shi wannan ina yake zuwa cikin talatainin dare haka?"
Sake saken zuci tayita yi har saida asuba takawo kai, awannan lokacin ne taji dawowarsa azamar sauka daga kan gadonta tayi tanufi part dinshi da sauri domin tana son taga awanne yanayi yake,
Acikin falonshi ta buya a bayan labule, ahankali taji ya bude kofa yashigo, lekashi tayi nan taganshi acikin nutsuwarshi yake ita tayi zaton zata ganshi cikin maye ko makamancin haka, zama yayi ya bude wani dan karamin akwati nan taga kudi fall kuma duk daloli ne ba naira ba,
Mayarwa yayi ya rufe ya tashi yashiga bedroom dinshi, sadadadawa tayi tafita takoma dakinta tana tambayar kanta to daga ina yaya yusleem yake?
Wasa wasa kullum cikin dare sai taji fitarsa kuma bashi zai dawoba sai aubah ashe dama can haka yakeyi sanine batayi ba saboda lokacin da zai fita tayi bacci shiyasa har yaje yadawo bata saniba, kasa gane inda yake zuwa tayi domin fitar tasa kusan kullum ne tamkar ibada kuma baya tashi fita sai tsakiyar dare,
Yau kam ta daura aniyar binshi taga inda yake zuwa domin tunaninta yanzu yafara bata cewar ko yaya yusleem dan fashi ne?
Hana idonta bacci tayi har karfe dayan dare tana jira taji motsin fitowarsa amma shiru, karfe biyu shiru har da rabi duk shiru, hakura tayi ta kwanta nan bacci ya dauketa can cikin baccinta taji dirin motarshi agigice ta tashi ta leka abin haushi wai sai ganinshi tayi yafito daga cikin mota alamun yadawo daga wurinda yaje,
Jin shirun yayi yawa yasata nufar part dinshi domin dubashi,
Lokacin da ta shiga atsaye taganshi gaban mirror yana gyara necktie din da yasaka da alama shirin fita yakeyi domin lokacin karfe 9:30 nasafe,
Sallama tayi ya amsa mata aciki ciki batare da ya kalleta ba,
"Ina kwana yaya.."
"Lafiya" yabata amsa,
Shiru tayi ta tsaya tana kallonshi, sanye yake cikin bakaken suit yasaka blue din t shirt mai kwala ta ciki,
Agogon azurfa na Gucci yadauka ya daura ahannunshi yafesa turare ya zo ya raba ta gefenta yawuce batare da yayi mata magana ba,
"Adawo lafiya..." Tafada ganin yayi hanyar fita,
Bata fita daga cikin dakinba saida ta gyarashi ta wanke toilet ta goge ko ina sannan ta rufe tafita,
A falonta tasamu surayya baje tana jiranta,
"A'a saukar yaushe?"
"Jiyan nan nadawo shine naga bazan iya zamaba har sai nazo naganki"
"Sannu da dawowa, kin jima da zuwane?"
"Ehh to nadai fi 20 minutes amma abinda yasa ban damuba shine naga kina turakar mai gida..."
Murmushi Hafsat tayi mai ciwo,
"Surayya yaya yusleem narasa wanne irin mutum ne shi wanda sam bai damu da iyalinsa ba..."
Katseta surayya tayi,
"Da jira kikeyi yadamu dake? Tab ai bari kiji wallahi garama ki tashi daga wannan dogon barcin da kikeyi domin yaya yusleem yanada manyan matsaloli,
Bafa akanki yafara aureba kuma wallahi sakin mata yake, auri saki gareshi dan babu wacce ya taba aura tayi shekara agidansa shiyasa nake son ki zage ki kamashi ahannu dumu dumu kuma wallahi karki raga masa ki azabtar dashi idan kika tsaya jin tausayinsa kika raga masa sunanki sorry domin shi azabtar dake zaiyi..."
Jin abinda surayya tace ai Hafsat bata San lokacin data zamo daga kan kujerar da take zaune ba tadawo kasa,
"Auri saki fa kikace?"
"Tabbas domin ya auri mata sunfi goma sha..."
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un.."
"A'a nifa ba fada miki nayi dan ki tada hankalinki ba, kawai fada miki nayi dan ki tashi atsaye kisan duk yanda zakiyi ki karkato da hankalinsa gareki"
Tagumi Hafsat tayi tana lazimi acikin zuciyarta......
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*25*
***Tagumi Hafsat tayi tai shiru tama rasa abin cewa domin bata san ta inda zata faraba,
"Baiwar Allah karki tashi hankalinki, nidai kawai abinda nakeso kisani shine yaya yusleem fa ba dutse bane mutum ne dan haka duk taurin kansa wata rana dole ya bukaci mace, dan haka daurewa zakiyi ki zage kiyita shisshige masa har yazo hannu kin gane ai?
'Yar rangwadar nan, kwalliyar nan, tsabtar nan..." Surayya tafada tana dariya,
Kallonta Hafsat tayi idanuwanta har sunyi ja,
"Surayya kenan da alama baki gama fahimtar yayan naki ba, yaushe ma ya zauna agidan bare har insamu damar yi masa wadannan abubuwan? Kedai kawai Allah yabani mafita"
"Amin, zaima baki cikin ikonsa"
Haka suka cigaba da tattauna maganar har tsawon wani lokaci,yauma kamar koda yaushe saida da daddare sannan surayya taja motarta ta tafi,
Tafiyarta yasa Hafsat jin gidan yayi mata tsittt, part din yusleem ta shiga baya cikin falon dan haka ta nufi bedroom dinshi nan dinma baya ciki, har zata fita tajiyo motsin ruwa acikin toilet alamun wanka yake nan tajuya tafita,
Bata kara sashi a idonta ba tun daga ranar,dan haka kullum wunin kadaici takeyi wannan dalilin ne yasa tayiwa Ummi waya tace a Kawo mata keken sakarta domin ko babu komai zai rinka dan debe mata kewa idan babu abinda takeyi sai tarinka hawa tanayi,
Washe gari hajiya kubra taje gidan takai mata keken da sauran kayan da zatayi amfani dasu wurin sakar, wannan shine karo nafarko da ummin taje gidan nata shiyasa murnarta takasa boyuwa,
Ita ason ranta ma ummin ta zauna ta wuni amma fur taki ko minti talatin batayi ba tatashi zata tafi,
Bin bayanta Hafsat tayi ta rakata anan hajiya kubran ke fada mata cewar ai yusleem sau biyu yana zuwa gida gaishesu bayan bikin, mamaki ne ya kama hafsa saboda bata zaci zai iya zuwaba duk da tafi zaton cewar mami ce zata tilasta shi yaje, sallama sukayi da ummin tatafi ita kuma takoma cikin gida.
Samun keken sakar nan akusa da ita shine dalilinta yanzu na rage zaman tunani duk da wani lokacin tana ganin anya kuwa rayuwarsu ita da yusleem zata yiyu ahaka? A matsayinsu na mata da miji ace sai suyi kwana 3 basu ga junaba, sannan bai damu da yaci abincinta ba balle har magana ta shiga tsakaninsu,
Gama wannan tunanin keda wuya ta mike ta nufi falonshi, baya ciki dan haka takarasa dakin baccinsa can dinma baya nan amma ga laptop dinshi nan a ajiye akan gado, karasawa tayi ta dauke laptop din ta gyara gadon daga nan ta zarce da gyara dakin gaba daya,
Bathroom tashiga nan taga ya jika kananan kayanshi acikin bocket da dukkan alamu so yake su jiku yasa acikin washing machine yawanke domin tasan bazai taba yin wanki da kansa ba tunda itama da ba kowan kowaba an ajiye mata injin wankin sai dai ita bata ma fiya amfani dashiba tafi ganewa tayi abinta da kanta,
Tsayawa tayi ta wanke masa kayan tass tadauka tafita ta shanya, tana cikin shanyawa yadawo yana sanye da kananan kaya jeans da t shirt,
Binshi cikin falon tayi bayan ta kammala shanyar kayan,
"Sannu da zuwa..."
"Yawwa..." Ya amsa mata aciki ciki daga nan bai kara koda kallon bangaren da takeba bare tasa ran zaiyi mata sannu na aikin da tayi masa,dan haka tawuce takoma part dinta,
Wadannan abubuwan dake faruwa sune suka hanata bacci adaren yau har misalin karfe daya idonta biyu, tanata juyi tajiyo kamar alamun tafiya atsakar gida a tsorace ta tashi taje gaban window ta daga labule tafara lekawa ahankali, kasancewar tsakar gidan akwai haske tal kamar rana shiyasa tasamu damar hango yusleem din wanda ke kokarin bude kofar motarshi,
"Ina yaya yusleem zaije acikin daren nan?" Ta tambayi kanta,
Kafin ta iya bawa kanta amsa tuni har yashiga motar mai gadi ya bude masa yafice, ita tsoro ne ma ya kamata domin duk atunaninta agidan mami ne wani abu yafaru nan takoma ta zauna jugum tanata nazari amma motsi kadan sai tatashi ta leka ko yadawo amma shiru,
Haka takasa bacci sai sake sake da haka har asubah tayi a lokacin ne taji dawowarshi da kamar taje wurinshi taji abinda yafaru sai dai tafasa,alwala taje ta dauro tazo ta tada salla.
Misalin karfe 8 tashiga falonshi bayan taci kwalliya cikin wata dark purple din shadda,
Kwance ta sameshi yana bacci akan doguwar kujera yana sanye da farar t shirt da bakin boxer, karasawa dakinshi tayi ta gyara masa tafito, lokacin da ta fito kuma yana zaune yana danna wayarshi, gaisheshi tayi ya amsa daga nan yaci gaba da abinda yake yi, jin baice mata komai ba yasata fita takoma falonta taci gaba da harkokinta,
Tana kan kekenta tana karasa hada rigar data fara jiya taji sallamar Amina kawarta, da murna ta tari aminan wacce ke daga kafa dakyar domin cikinta yadan fara tsufa,
Ba karamin dadin ganin aminan tajiba nan suka baje a falonta suka hau hirar yaushe gamo, wuni cur Amina tayi mata sai yamma ta tafi,
Haka taci gaba da zaman kadaici agidan domin surayya ma takoma makaranta kuma bazata sake dawowa ba har saita kammala, yau watanta biyu da wani abu agidan kuma tunda tazo bata taba fitaba shiyasa yau ta kuduri niyyar tambayarshi zuwa ganin gida,
Yana kokarin fita tayi gaggawar tsayar dashi, tsayawa yayi batare da yajiyo ba,
"Yaya dama yau ina son zuwa gidanmu ne"
"Allah kiyaye hanya, idan kin shirya akwai driver"
Daga haka yayi gaba abinshi, shiryawa taje tayi tafito tana dauke da rigunan jariran da ta saka wanda zata tafi dasu takaiwa Ummi domin asayar mata,
Kamar yadda yusleem yace haka ta tarar da driver yana zaman jiranta nan ya dauketa yakaita gida, murna wurin hajiya kubra abin ba acewa komai nan tashiga yin nan nan da ita, Hafsat ba ita tabaro gidanba sai dare domin saida tajira alhaji sa'id yadawo suka gaisa,
Daren yauma kamar rannan kasa bacci tayi can taji fitar yusleem daga gidan agogo ta kalla karfe 2 saura na dare,
"To wai shi wannan ina yake zuwa cikin talatainin dare haka?"
Sake saken zuci tayita yi har saida asuba takawo kai, awannan lokacin ne taji dawowarsa azamar sauka daga kan gadonta tayi tanufi part dinshi da sauri domin tana son taga awanne yanayi yake,
Acikin falonshi ta buya a bayan labule, ahankali taji ya bude kofa yashigo, lekashi tayi nan taganshi acikin nutsuwarshi yake ita tayi zaton zata ganshi cikin maye ko makamancin haka, zama yayi ya bude wani dan karamin akwati nan taga kudi fall kuma duk daloli ne ba naira ba,
Mayarwa yayi ya rufe ya tashi yashiga bedroom dinshi, sadadadawa tayi tafita takoma dakinta tana tambayar kanta to daga ina yaya yusleem yake?
Wasa wasa kullum cikin dare sai taji fitarsa kuma bashi zai dawoba sai aubah ashe dama can haka yakeyi sanine batayi ba saboda lokacin da zai fita tayi bacci shiyasa har yaje yadawo bata saniba, kasa gane inda yake zuwa tayi domin fitar tasa kusan kullum ne tamkar ibada kuma baya tashi fita sai tsakiyar dare,
Yau kam ta daura aniyar binshi taga inda yake zuwa domin tunaninta yanzu yafara bata cewar ko yaya yusleem dan fashi ne?
Hana idonta bacci tayi har karfe dayan dare tana jira taji motsin fitowarsa amma shiru, karfe biyu shiru har da rabi duk shiru, hakura tayi ta kwanta nan bacci ya dauketa can cikin baccinta taji dirin motarshi agigice ta tashi ta leka abin haushi wai sai ganinshi tayi yafito daga cikin mota alamun yadawo daga wurinda yaje,