Sashe 19
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Gaskiya yaya yusleem muyi sallar nan muje mu samo abinda zamu ci daga nan sai mu taho da maganin sauro.."
Suna idar da sallar suka fita, gasasshiyar kaza Hafsat tace asiya nan yusleem ya kalleta,
"Yanzu fa ba lokacin cin abin dadi bane, kibar kazar nan muje shagon can mu sai gari da sugar.."
"A'a yaya yusleem, gaskiya gari bazai shiga ba wallahi, mudai siyi kazar.."
Son ranta yabi suka siyo gasasshiyar kazar daga nan suka karasa shago suka siyi maganin sauro da candle guda biyu da ashana sai sabulun wanka give sinki daya da soson wanka da brush da maclean sai man shafawa Vaseline,
Gida suka koma ya kunna candle din ya ajiye sannan ya kunna musu maganin sauro,
Kasancewar yunwar tasu taci ta cinye yasa baifi rabi suka ci kazar ba, Hafsat ce tafara tashi ta bude trolley dinta ta dauki zani tadauki soso da sabulun wanka da brushes dinsu da maclean ta shiga bathroom, wanka tayi tafito ta dauki kayan baccinta takoma cikin bathroom din,Riga da wando ne red colour masu santsi, rigar tana da dan guntun hannu yayinda wandon yake dogo,doro hijabinta tayi akan kayan tafito tahau kan katifa ta kwanta,
"Bari nima inje inyi wankan tunda kin fito" yusleem yafada tareda tashi tsaye ya shiga cikin toilet din, yajima aciki kamar wanda zai sake fata dama Hafsat tasan dadewarshi a wanka shiyasa tafara shiga,
Saida yayi kusan minti 30 sannan yafito yana rikeda rigarshi yana tsane ruwan kanshi,
Gaban kayansu ya karasa ya bude trolley dinshi yaciro yar t shirt da boxer,
Ta dan hasken candle din da suka kunna Hafsat take kallonshi lokacin da yake kokarin sauya kayan jikinshi,
Rufe idanuwanta tayi saboda wannan shine karo nafarko da zata kwana dashi akan katifa guda daya,
Juyowa yayi ya kalleta bayan yaje ya dauke kakkauran labulen kofar dakin yabar mai shara sharan,
"Ko ke bakya jin zafin ne?"
"Inaji mana yaya yusleem, wallahi akwai zafi kila hadari ne agarin"
Candle ya dauka yakarasa gefen katifar yazauna,
"Bama kila bane ga gari nan anata yin walkiya, kalli waje ki gani"
Sai lokacin talura da ashe asaitin kofar daki ta kwanta nan ta mirgina takoma barin da yake,
"Anan zan kwanta, kai kakoma can barin"
Tashi yayi yakoma bayan yakashe candle din,duhu didim dakin yayi,
"Shine ni kika turo ni kofar daki ko inyaso abin tsoron idan yazo ni ya kamani"
Murmushi tayi ta zare hijabin dake jikinta,tana jinshi ya kwanta agefenta bayan ya matso da filonshi jikin nata filon sabanin da dayake ajiye acan karshen katifa.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*30*
***Dukkaninsu shiru sukayi kowa da abinda yake tunani acikin zuciyarsa,
"Nanah..." Taji yusleem yakirata, dan juyawa tayi acikin duhun ta kalleshi,
"Yaya yusleem menene?"
"Babu komai dama nayi zaton ko kinyi bacci ne"
Juyawa tayi ta dan gyara kwanciyarta,
"A'a banyi ba"
"To kiyi.."
Lumshe idanuwanta tayi,
"Saida safe"
"Allah ya tashemu lafiya"
Shiru suka sakeyi wanda har bacci ya dauke Hafsat amma shi yusleem sam yakasa baccin inbanda sake sake babu abinda zuciyarshi keyi masa, yasaka wancen ya kunce yasaka wancan har garin yayi tsit dare ya raba bai iya yin bacci ba,
Hafsat kuwa cikin barcin da takeyi tafara wani mafarki marar dadi domin wasu manyan mutane tagani suna bin yusleem aguje kowannensu rikeda katuwar wuka mai kaifi sai kyalli take zuwa can yusleem din ya fadi daya daga cikinsu ne ya cimmasa ya daga wukar zai daba masa tayi firgigit ta farka,
Cikin duhun tafara lalubenshi akan katifar amma bata jishiba hakan yasata rudewa,
"Yaya yusleem,yaya yusleem...!"
Shiru tayi sakamakon jin ya amsa daga bakin kofa inda yaje domin saukar da labulen dakin domin yanzu garin yadauki sanyi duk da ba ayi ruwa ba amma wata iska mai sanyi ake kadawa,
Karasowa yayi kan katifar, tun kafin yakarasa hawowa taje ta rirrikeshi,
"Yaya yusleem babu abinda yasameka...?"
Riketa yayi ya kwantar da ita awurinda take kwance dafarko,
"Menene yafaru nanah? Lafiya lau nake.. Mafarki kikayi?"
Hannuwanshi ta makalkale cikin nata,
"Yaya yusleem wani mummunan mafarki nayi wallahi..."
"To ai mafarki ba gaskiya bane nanah, ki koma kiyi baccinki kinji..."
D'aga mishi kai tayi kamar yana ganinta tareda tallafe kumatunta da hannunshi guda daya,
Duk da taga azahiri babu abinda ya sameshi amma sai takasa komawa baccin, shi kanshi yusleem din shima yakasa yin barcin,
"Yaya yusleem.."
"Na'am..."
"Tunda mun kasa yin bacci katashi muyi alwala muyi sallar nafila watakila sai Allah ya amsa ya rangwanta mana masifun da suke tunkaro mu..."
"To nanah, bari natashi naje.."
Saurin rikeshi tayi, "yaya yusleem mu tafi tare"
Taren suka shiga toilet din kasancewar duhu ne alwala sukayi suka fito suka fara sallolin nafila wanda har saida suka yi sallar asuba sannan suka kwanta bacci, bacci sukayi sosai sai 12 saura sannan Hafsat ta farka, yusleem takalla wanda ta rirrikeshi yana kwance agefenta,
Tashi tayi tashiga wanka har tafito ta shirya bai tashiba tunanin abinda zasu karya dashi tafara, mikewa tayi tashiga bathroom ta dauko bucket domin debowa yusleem ruwan wanka,
"Nanah ina zaki..?" Taji yace da ita idanuwanshi suna rufe,
"Ruwan wanka zan debo maka..."
Tashi zaune yayi,
"Dauko wani bucket din inbiki mu debo tare"
"Kabarshi zan debo"
Tashi yayi dakanshi yaje yadauko bucket din yabita domin ita tuni tajima da fita, kamar jiya yauma matan gidan suna zazzaune akofar dakin daya daga cikinsu, ganin Hafsat tafito duk sai suka maida kallonsu gareta, gaishesu tayi kamar jiya sannan takarasa bakin rijiyar,
Gugar yusleem ya karba daga hannunta,
"Kawo inzuba miki.." Yayi maganar ahankali duk da dama maganarshi bawai cika karfi tayiba,sakar mishi tayi yafara janyo ruwan yana zuba mata acikin bucket din,
Ganin hankalin matan ya komo garesu yasa duk taji ta tsargu musamman ma dataga kamar sunfi karkata ga kallon yusleem, saida ta jirashi ya cika nasa bucket din sannan suka dauka suka tafi,
Acikin bathroom din tabarshi bayan ta ajiye ruwan tafito,
Keken sakarta ta kinkimo ta zauna agefen katifa tasoma saitashi domin so take tafara yin sakar kayan sanyi, jin tafiyar yusleem yasata juyawa ganinshi tayi babu riga sai iya boxer dan haka tayi saurin maida kanta ta sunkuyar,
Kanta yana sunkuye har yagama shiryawa yasaka kayanshi yadawo kan katifar ya Zauna,
"Yaya yusleem ga guntun naman jiya can bari indauko mana.."
Kafin yabata amsa har tatashi taje ta dauko,
"Kaga cewa nayi ko inje insaida kujeru na sai insiyo zaren bulu da sauran kayan da zamu bukata, kaga dole sai mun siyo risho da kayan abinci.."
Shiru taji yayi baice komai ba, dagowa tayi ta kalleshi,
"Yaya yusleem bakace komai ba"
"Nanah gaskiya akaina bazaki rabu da kayanki ba, karki saida ko cokali naki"
Murmushi tayi,
"To ai ba saboda kai zan siyarba, saboda nida kai zan siyar"
"To ban goyi baya ba"
"Shikenan tunda baka amince ba"
"Ba amincewa ne banyiba kawai dai idan narabaki da kayanki ne banyi miki adalci ba"
"To magana tawuce,yanzu kasan me? Kafadawa mami cewar zakayi tafiya ta gaggawa zuwa wani state din mai nisa saboda kasan zata nemeka idan kuma har ta nemeka bata sameka ba hankalinta tashi zaiyi, idan tayi maka maganata kace tare zamu tafi kaga hankalinta zaifi kwanciya sannan tunaninta bazai taba Kawo mata cewar da akwai matsala ba.."
"To amma iyayenki fa? Sukuma me zan fada musu"
"Sudinma hakan zan cemusu munyi tafiya zuwa wani gari mai nisa, koma kawai muce Niger muka tafi.."
Hadaddun wayoyinshi dake ajiye akasan trolley dinshi hadeda laptop dinshi yadauko ya kunna,
Number mami yayi dialing babu bata lokaci ta dauka, dakyar ya saita nutsuwarshi yayi mata bayani bayan sun gaisa, fatan alkhairi tayi musu daga nan sukayi sallama,
"Nima bari inkira Ummi infada mata kaga shikenan daga nan mun gama da matsalar gida sai mu fuskanci wata rayuwar kuma"
Tata wayar itama ta dauka ta kira Ummi ta sanar mata daga nan takashe wayar amma shi yusleem tashi wayar abude yabarta saboda yasan abokan harkarshi zasu nemeshi.
Misalin karfe 2 narana ta dauki dan madaidaicin food flask, fita tayi domin yusleem bacci yakeyi, tsakar gida taje inda matan nan ke zazzaune ta tambayesu inda ake sayar da abinci,
"Me kike so? Kawo amir yasiyo miki" inji wata mata wacce ahaife da alama bazata girmeta ba,
"Yawwa nagode dan wanke nakeso"
Naira dari tabayar yaron yatafi siyo mata, daki takoma tazauna tana lissafi domin kudin da yayi saura yanzu baifi dubu goma sha daya da yan canji ba gashi kuma bukatunsu nada yawa domin basuda kayan abinci kuma zasu cikawa mai gidan haya kudinsa gashi tana son ta siyo zaren saka,
Yanke hukuncin zata sayar da kujerunta kawai tayi batareda yusleem yasaniba, jin muryar amir yana sallama yasata tashi taje ta karbo abincin ta danka mishi naira goma,
Bata tashi yusleem ba saboda tasan daren jiya bai samu bacci ba har saida ya tashi dan kanshi lokacin karfe 3:32 na yamma,
Dan waken tasa musu suka ci bayan sun gama tace mishi zata fita kasuwa domin siyo zaren kulu da dan abubuwan da ba arasa ba, acikin dakin tabarshi tafita,
Direct wurin wasu kafintoci tawuce tayi musu tallen kujerunta sukace zasu siya amma sai sun gansu nan tace to zuwa gobe zatazo suje sai sugani,
Daga nan kasuwa tawuce tasiyo zarirrukan kulu kala kala sannan ta siyo musu dan karamin risho ta hado musu kayan tea da babban bread guda daya,
Ana kokarin yin sallar magrib tadawo gida, akan katifa tasamu yusleem yana zaune,
"Sannu nanah.."
"Yawwa yaya yusleem sannu nabarka kai kadai ko"
Murmushi yayi, "ai kece da sannu"
"Kaga abubuwan da nasiyo, ga risho amma kalanzir dinne na dari biyu kawai nasiyo nasan zai ishemu mu rinka dan dafa ruwan zafi"
Tausayinta yaji yakamashi saboda irin rayuwar da suka samu kansu aciki yanzu wacce yasan shine silar jefata aciki,
"Allah yayi miki sakayya da gidan aljanna.." Shine abinda yafada kawai ya mike yashiga toilet domin yin alwala,
Tea tadafa musu da daddaren suka sha suka kwanta, wayarshi ce ta hau vibrating nan yadaga,
Suna idar da sallar suka fita, gasasshiyar kaza Hafsat tace asiya nan yusleem ya kalleta,
"Yanzu fa ba lokacin cin abin dadi bane, kibar kazar nan muje shagon can mu sai gari da sugar.."
"A'a yaya yusleem, gaskiya gari bazai shiga ba wallahi, mudai siyi kazar.."
Son ranta yabi suka siyo gasasshiyar kazar daga nan suka karasa shago suka siyi maganin sauro da candle guda biyu da ashana sai sabulun wanka give sinki daya da soson wanka da brush da maclean sai man shafawa Vaseline,
Gida suka koma ya kunna candle din ya ajiye sannan ya kunna musu maganin sauro,
Kasancewar yunwar tasu taci ta cinye yasa baifi rabi suka ci kazar ba, Hafsat ce tafara tashi ta bude trolley dinta ta dauki zani tadauki soso da sabulun wanka da brushes dinsu da maclean ta shiga bathroom, wanka tayi tafito ta dauki kayan baccinta takoma cikin bathroom din,Riga da wando ne red colour masu santsi, rigar tana da dan guntun hannu yayinda wandon yake dogo,doro hijabinta tayi akan kayan tafito tahau kan katifa ta kwanta,
"Bari nima inje inyi wankan tunda kin fito" yusleem yafada tareda tashi tsaye ya shiga cikin toilet din, yajima aciki kamar wanda zai sake fata dama Hafsat tasan dadewarshi a wanka shiyasa tafara shiga,
Saida yayi kusan minti 30 sannan yafito yana rikeda rigarshi yana tsane ruwan kanshi,
Gaban kayansu ya karasa ya bude trolley dinshi yaciro yar t shirt da boxer,
Ta dan hasken candle din da suka kunna Hafsat take kallonshi lokacin da yake kokarin sauya kayan jikinshi,
Rufe idanuwanta tayi saboda wannan shine karo nafarko da zata kwana dashi akan katifa guda daya,
Juyowa yayi ya kalleta bayan yaje ya dauke kakkauran labulen kofar dakin yabar mai shara sharan,
"Ko ke bakya jin zafin ne?"
"Inaji mana yaya yusleem, wallahi akwai zafi kila hadari ne agarin"
Candle ya dauka yakarasa gefen katifar yazauna,
"Bama kila bane ga gari nan anata yin walkiya, kalli waje ki gani"
Sai lokacin talura da ashe asaitin kofar daki ta kwanta nan ta mirgina takoma barin da yake,
"Anan zan kwanta, kai kakoma can barin"
Tashi yayi yakoma bayan yakashe candle din,duhu didim dakin yayi,
"Shine ni kika turo ni kofar daki ko inyaso abin tsoron idan yazo ni ya kamani"
Murmushi tayi ta zare hijabin dake jikinta,tana jinshi ya kwanta agefenta bayan ya matso da filonshi jikin nata filon sabanin da dayake ajiye acan karshen katifa.....
*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*30*
***Dukkaninsu shiru sukayi kowa da abinda yake tunani acikin zuciyarsa,
"Nanah..." Taji yusleem yakirata, dan juyawa tayi acikin duhun ta kalleshi,
"Yaya yusleem menene?"
"Babu komai dama nayi zaton ko kinyi bacci ne"
Juyawa tayi ta dan gyara kwanciyarta,
"A'a banyi ba"
"To kiyi.."
Lumshe idanuwanta tayi,
"Saida safe"
"Allah ya tashemu lafiya"
Shiru suka sakeyi wanda har bacci ya dauke Hafsat amma shi yusleem sam yakasa baccin inbanda sake sake babu abinda zuciyarshi keyi masa, yasaka wancen ya kunce yasaka wancan har garin yayi tsit dare ya raba bai iya yin bacci ba,
Hafsat kuwa cikin barcin da takeyi tafara wani mafarki marar dadi domin wasu manyan mutane tagani suna bin yusleem aguje kowannensu rikeda katuwar wuka mai kaifi sai kyalli take zuwa can yusleem din ya fadi daya daga cikinsu ne ya cimmasa ya daga wukar zai daba masa tayi firgigit ta farka,
Cikin duhun tafara lalubenshi akan katifar amma bata jishiba hakan yasata rudewa,
"Yaya yusleem,yaya yusleem...!"
Shiru tayi sakamakon jin ya amsa daga bakin kofa inda yaje domin saukar da labulen dakin domin yanzu garin yadauki sanyi duk da ba ayi ruwa ba amma wata iska mai sanyi ake kadawa,
Karasowa yayi kan katifar, tun kafin yakarasa hawowa taje ta rirrikeshi,
"Yaya yusleem babu abinda yasameka...?"
Riketa yayi ya kwantar da ita awurinda take kwance dafarko,
"Menene yafaru nanah? Lafiya lau nake.. Mafarki kikayi?"
Hannuwanshi ta makalkale cikin nata,
"Yaya yusleem wani mummunan mafarki nayi wallahi..."
"To ai mafarki ba gaskiya bane nanah, ki koma kiyi baccinki kinji..."
D'aga mishi kai tayi kamar yana ganinta tareda tallafe kumatunta da hannunshi guda daya,
Duk da taga azahiri babu abinda ya sameshi amma sai takasa komawa baccin, shi kanshi yusleem din shima yakasa yin barcin,
"Yaya yusleem.."
"Na'am..."
"Tunda mun kasa yin bacci katashi muyi alwala muyi sallar nafila watakila sai Allah ya amsa ya rangwanta mana masifun da suke tunkaro mu..."
"To nanah, bari natashi naje.."
Saurin rikeshi tayi, "yaya yusleem mu tafi tare"
Taren suka shiga toilet din kasancewar duhu ne alwala sukayi suka fito suka fara sallolin nafila wanda har saida suka yi sallar asuba sannan suka kwanta bacci, bacci sukayi sosai sai 12 saura sannan Hafsat ta farka, yusleem takalla wanda ta rirrikeshi yana kwance agefenta,
Tashi tayi tashiga wanka har tafito ta shirya bai tashiba tunanin abinda zasu karya dashi tafara, mikewa tayi tashiga bathroom ta dauko bucket domin debowa yusleem ruwan wanka,
"Nanah ina zaki..?" Taji yace da ita idanuwanshi suna rufe,
"Ruwan wanka zan debo maka..."
Tashi zaune yayi,
"Dauko wani bucket din inbiki mu debo tare"
"Kabarshi zan debo"
Tashi yayi dakanshi yaje yadauko bucket din yabita domin ita tuni tajima da fita, kamar jiya yauma matan gidan suna zazzaune akofar dakin daya daga cikinsu, ganin Hafsat tafito duk sai suka maida kallonsu gareta, gaishesu tayi kamar jiya sannan takarasa bakin rijiyar,
Gugar yusleem ya karba daga hannunta,
"Kawo inzuba miki.." Yayi maganar ahankali duk da dama maganarshi bawai cika karfi tayiba,sakar mishi tayi yafara janyo ruwan yana zuba mata acikin bucket din,
Ganin hankalin matan ya komo garesu yasa duk taji ta tsargu musamman ma dataga kamar sunfi karkata ga kallon yusleem, saida ta jirashi ya cika nasa bucket din sannan suka dauka suka tafi,
Acikin bathroom din tabarshi bayan ta ajiye ruwan tafito,
Keken sakarta ta kinkimo ta zauna agefen katifa tasoma saitashi domin so take tafara yin sakar kayan sanyi, jin tafiyar yusleem yasata juyawa ganinshi tayi babu riga sai iya boxer dan haka tayi saurin maida kanta ta sunkuyar,
Kanta yana sunkuye har yagama shiryawa yasaka kayanshi yadawo kan katifar ya Zauna,
"Yaya yusleem ga guntun naman jiya can bari indauko mana.."
Kafin yabata amsa har tatashi taje ta dauko,
"Kaga cewa nayi ko inje insaida kujeru na sai insiyo zaren bulu da sauran kayan da zamu bukata, kaga dole sai mun siyo risho da kayan abinci.."
Shiru taji yayi baice komai ba, dagowa tayi ta kalleshi,
"Yaya yusleem bakace komai ba"
"Nanah gaskiya akaina bazaki rabu da kayanki ba, karki saida ko cokali naki"
Murmushi tayi,
"To ai ba saboda kai zan siyarba, saboda nida kai zan siyar"
"To ban goyi baya ba"
"Shikenan tunda baka amince ba"
"Ba amincewa ne banyiba kawai dai idan narabaki da kayanki ne banyi miki adalci ba"
"To magana tawuce,yanzu kasan me? Kafadawa mami cewar zakayi tafiya ta gaggawa zuwa wani state din mai nisa saboda kasan zata nemeka idan kuma har ta nemeka bata sameka ba hankalinta tashi zaiyi, idan tayi maka maganata kace tare zamu tafi kaga hankalinta zaifi kwanciya sannan tunaninta bazai taba Kawo mata cewar da akwai matsala ba.."
"To amma iyayenki fa? Sukuma me zan fada musu"
"Sudinma hakan zan cemusu munyi tafiya zuwa wani gari mai nisa, koma kawai muce Niger muka tafi.."
Hadaddun wayoyinshi dake ajiye akasan trolley dinshi hadeda laptop dinshi yadauko ya kunna,
Number mami yayi dialing babu bata lokaci ta dauka, dakyar ya saita nutsuwarshi yayi mata bayani bayan sun gaisa, fatan alkhairi tayi musu daga nan sukayi sallama,
"Nima bari inkira Ummi infada mata kaga shikenan daga nan mun gama da matsalar gida sai mu fuskanci wata rayuwar kuma"
Tata wayar itama ta dauka ta kira Ummi ta sanar mata daga nan takashe wayar amma shi yusleem tashi wayar abude yabarta saboda yasan abokan harkarshi zasu nemeshi.
Misalin karfe 2 narana ta dauki dan madaidaicin food flask, fita tayi domin yusleem bacci yakeyi, tsakar gida taje inda matan nan ke zazzaune ta tambayesu inda ake sayar da abinci,
"Me kike so? Kawo amir yasiyo miki" inji wata mata wacce ahaife da alama bazata girmeta ba,
"Yawwa nagode dan wanke nakeso"
Naira dari tabayar yaron yatafi siyo mata, daki takoma tazauna tana lissafi domin kudin da yayi saura yanzu baifi dubu goma sha daya da yan canji ba gashi kuma bukatunsu nada yawa domin basuda kayan abinci kuma zasu cikawa mai gidan haya kudinsa gashi tana son ta siyo zaren saka,
Yanke hukuncin zata sayar da kujerunta kawai tayi batareda yusleem yasaniba, jin muryar amir yana sallama yasata tashi taje ta karbo abincin ta danka mishi naira goma,
Bata tashi yusleem ba saboda tasan daren jiya bai samu bacci ba har saida ya tashi dan kanshi lokacin karfe 3:32 na yamma,
Dan waken tasa musu suka ci bayan sun gama tace mishi zata fita kasuwa domin siyo zaren kulu da dan abubuwan da ba arasa ba, acikin dakin tabarshi tafita,
Direct wurin wasu kafintoci tawuce tayi musu tallen kujerunta sukace zasu siya amma sai sun gansu nan tace to zuwa gobe zatazo suje sai sugani,
Daga nan kasuwa tawuce tasiyo zarirrukan kulu kala kala sannan ta siyo musu dan karamin risho ta hado musu kayan tea da babban bread guda daya,
Ana kokarin yin sallar magrib tadawo gida, akan katifa tasamu yusleem yana zaune,
"Sannu nanah.."
"Yawwa yaya yusleem sannu nabarka kai kadai ko"
Murmushi yayi, "ai kece da sannu"
"Kaga abubuwan da nasiyo, ga risho amma kalanzir dinne na dari biyu kawai nasiyo nasan zai ishemu mu rinka dan dafa ruwan zafi"
Tausayinta yaji yakamashi saboda irin rayuwar da suka samu kansu aciki yanzu wacce yasan shine silar jefata aciki,
"Allah yayi miki sakayya da gidan aljanna.." Shine abinda yafada kawai ya mike yashiga toilet domin yin alwala,
Tea tadafa musu da daddaren suka sha suka kwanta, wayarshi ce ta hau vibrating nan yadaga,