Sashe 16
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A perfect guys & ladies hotel ta sauka ta biya mai adaidaita sahu kudinsa tatafi can cikin wasu shuke shuken flowers ta tsaya, har akayi magrib bataga alamun daya daga cikin motocin yusleem ba tana nan tsaye har akayi isha alokacin ne ta saddakar da bazai zoba,
Fitowa tayi takama hanya zata fita tana zuwa gate din hotel din tahango motarshi tana dosowa kamar a mafarki babu shiri tajuya tabi ta bayan wasu bishiyoyi ta nemi mafaka duk da tasan ba lallai ne yaganeta ba saboda bazai taba tsammanin ganinta awurinba,
Tana ganinshi yafito bayan ya rufe motarshi ya nufi ciki yana yin waya yana sanye cikin kananan kaya, lababawa tayi tasoma binsa abaya abaya har zuwa ciki, akofar wani daki taga yatsaya mintuna kadan aka bude masa yashiga,batayi kasa agwiwa ba tabishi har kofar wannan dakin,
Tsayawa tayi tana tunanin ta ina ya kamata tafara, tafi minti goma atsaye daga karshe kawai ta nufi kofar ta murda abin mamaki abude tajita nan tashiga ahankali, wani dan madaidaicin falone wanda yacika da sanyin air condition, leken cikin bedroom din tafara yi amma kuma bata iya hango komai nan tadan tura kofar ahankali ta zira kanta ta leka, abinda tagani shine yayi sanadiyar sulalewarta awurin ta suma bayan ta kwalla kara mai mutukar firgitarwa.....
_Tofa ko me Hafsat tagani? Nidai Ummi Shatu banida wannan amsar..._
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*27*
***Ahankali tafara bude idanuwanta wadanda suka yi mata nauyi ga wani irin ciwo da kanta ke faman yimata kamar zai tsage,
Dishi dishi take gani kafin daga bisani ta dan fara ganin dishi dishin yana washewa har ya b'ace gaba daya,
Mami ta hango zaune saman wata kujerar roba ganin ta bude idonta yasa mamin matsawa gareta,
"Sannu Hafsat..., sannu kinji, Allah yabaki lafiya..."
Runtse idanuwanta tayi take wasu zafafan hawaye suka gangaro daga cikin idanuwanta, ko kadan bata burin ta sake ganin yusleem ayanda taganshi dazu kuma ko tunawa bata son ta kara yi domin wannan shine mafi munin gani da idanuwanta suka taba yi tunda tazo duniya,
"Sannu Hafsat, kukan me kikeyi kuma?" Mami ta tambayeta tana dafata,
"Kukan ciwo mami, kukan ciwo nakeyi mami ba kukan komai ba domin kaina wani nauyi naji yayi min banda azabar ciwon dake addabata..."
"Sannu, sannu Allah yabaki lafiya, ina zuwa bari inkirawo likita saboda yace idan kin bude idanuwanki inkirashi.."
Fita mami tayi daga cikin dakin nan Hafsat tasake mayar da idanuwanta ta rufe tana hawaye, a hakikanin gaskiya abinda tagani ne yasata wannan kukan bawai ciwon kan da take tareda shi yanzu bane,
Tana nan kwance tana hawaye taji shigowar mami da dr,
Gaban gadonta likitan yakarasa yakai hannunsa kan goshinta ya taba,
"Sannu, yanzu me kikeji yafi damunki?"
"Dr ciwon kai ne kadai ke damuna.."
"To insha Allah shima zai daina nan da dan wani lokaci.."
Dukufa likitan yayi yafara rubutu ajikin wani dan madaidaicin file saida ya kammala sannan yadago ya mikawa mami takardar,
"Ga magungunan da za asamo mata tasha bayan taci abinci, Allah yakara bata lafiya.."
Karbar takardar mami tayi shikuma likitan yasaka kai yafice daga cikin dakin,
Wayar yusleem mami tasoma nema ringing biyu zuwa uku ya dauka,
"Kana inane? Kai nake jirafa.."
Kashe wayar tayi batare da Hafsat tajiyo abinda yusleem din yafada ba,
Ba afi mintuna biyar da gama wayarsu da mami ba sai gashi ya turo kofa yashigo, kawar da kanta hafsat tayi daga gefen da yake ta mayar zuwa wani gefen,
"Wannan shine mijin kaddara..." Tafada acikin zuciyarta,
"Wai kai me yasameta? Inata tambayarka abinda yasameta harta suma haka amma kaki yimin bayani.."
"Yanzu dai mami ai ba lokacin yin wannan maganar bane, abinda kuke bukata nake son ji"
"To kaga dai magungunan da dr yace asiyo tasha bayan ta ci abinci amma gaskiya ni ina ganin idan har takara kwana biyar bataji sauki ba gara ka kaita chairo..."
Dan sajenshi ya shafa ya karbi takardar dake hannu mami,
"To shikenan bari nasamo drugs din indawo.."
Yana fita hajiya kubra na shigowa hannayenta dauke da babban basket din abinci,
"Hajiya siyama ya mai jikin? Nifa kalau muka rabu da ita saida ma nayi nayi da ita tajira salisu yadawo yakaita amma furr taki ashe tsautsayi ke janta.."
"Ehh haka Allah yake ikonsa ai, nima wallahi sai waya kawai yusleem yamin wai yakaita asibiti..."
Ajiye kayan hannunta hajiya kubra tayi ta matsa wurin Hafsat tana yimata sannu,
"Wai ya akayi haka tafaru? Hafsat garin yaya..?"
"Ummi kaddara da tsautsayi, nima ban san abinda ya sameni ba kawai jina nayi nafadi,shi lokacin da abin yafaru ma yana office inajin sai wayata aka dauka aka kirashi..." Ta karashe maganar hawaye na bin kuncinta,
"To Allah ya rufa asiri ya kiyaye gaba.."
"Amin summa amin, Allah yatashi kafadunta yabata lafiya..." Inji mami,
"Tashi kici abincin to, tuwon shinkafa ne miyar zogale.."
Dakyar Hafsat ta iya tashi ta zauna saboda irin yanda kanta ke tsananin sarawa, tafara cin abincin kenan yusleem ya shigo dauke da magungunan da likita ya rubuta mata,
"Mami gashi..."
"Yawwa ansamo, to bari tagama cin abincin sai tasha, ashe kaima baka gida lokacin da abun yafaru? Tace kana office sai awaya aka kiraka.."
Kallonshi Hafsat tayi domin taga irin yanda zai karbi maganar,
Shiru yayi baiyi magana ba saima bude kofa da yayi yafita,
Tunda yafita bata sake jin motsinshi ba,ita kanta tasan daren ranar bazata iya bacciba ba don Allah ya taimaka anhada mata da magungunan bacci ba acikin maganin da aka bata,
Tareda mami suka kwana a asibitin ita kuma ummi tatafi sai da safe ta dawo takawo musu abincin karyawa,
Kwananta uku a asibitin dr yace zasu iya tafiya gida, duk da ta dan samu saukin ciwon kan dake addabarta amma ta gagara daina kukan da takeyi wannan kam yazame mata kamar ibada wani lokacin sai suna zaune kalau sai kawai aga tana hawaye gashi daga mamin har Ummi sunyi tambayar duniya amma taki fada musu damuwarta wacce ke sata kukan,
Yanzun ma da zasu bar asibitin hawaye ne ke faman bin kuncinta ganin haka sai mami tace kawai hajiya kubra tatafi da ita gida ta dan sake warwarewa,
Tunda suka koma ummi ta tisata agaba tana yimata tambayoyi,
"Hafsat kin dai san yanzu aduniyar nan bakida wanda yafini daga ni sai Alhaji, ki sanar dani abinda yake damunki, idan baki fada minba wa kike dashi wanda zaki fadawa?"
Murmushin karfin hali Hafsat tayi,
"Ummi wallahi bafa kukan wani abu nakeyiba, kawai wani abin mamaki da ban tausayi nagani ranar da nabar gidan nan..."
"Me kika gani?"
"Ummi wata matace suke tafiya da yarta, tana rike da hannun yar fa yarinyar ta kwace ta ruga da gudu zata dauko wani abin wasa da ta hango ashe tsautsayi ne saiga mota tabi takanta gaba daya ta tanitseta, wannan abun shinefa ya hadda samin wannan suman da nayi..."
Dafata hajiya kubra tayi,
"Allah sarki Hafsat to ai dama idan ajali yayi kira ba makawa sai antafi, Allah yajikanta mukuma yasa mucika da kalmar shahada.."
"Amin Ummi"
Tashi hajiya kubra tayi tafita, tana fita Hafsat ta kifa kanta ajikin pillow tasoma kuka mai sauti domin da duk kukan zuci take yi wanda yafi nafili ciwo,
Kwananta biyu agida amma kullum sai mami tazo dubata yusleem ne kadai bai taba zuwa ba, aranar da tayi kwana uku mami tace tashirya su tafi inyaso idan takarasa warwarewa awurinta sai takoma gidanta, shiryawa tayi suka tafi gidan mamin nan mami tasoma bata dukkan kulawa domin dakin surayya tabata ta zauna aciki wanda yake dauke da dukkan abubuwan jin dadi irin wadanda ba agidan kowa ake samuba sai gidan wadanda suka amsa sunansu masu naira,
Dukkan abinda take so shi ake Kawo mata domin ga ma'aikata nan agidan kashi kashi ita kanta mamin babu abinda takeyi sai dai idan tana bukatar abu tayi waya kawai akawo mata shiyasa koda yaushe cikin ado zaka sameta tasha kwalliyarta ta zubawa jikinta gwala gwalai,
Dawowarta gidan mamin ma bai hanata daina kukan da ya zame mata jiki ba domin kullum cikin yinsa take,
Kwananta biyar agidan mamin amma bataga yusleem ba nan tafara tunanin to kodai tafiya yayi ne?
Tana cikin wannan tunanin tajiyo maganar mami a falo kuma da alamu yusleem dinne yazo, runtse idonta tayi tafara zubar da hawaye wanda har mami tashigo bata san tashigo ba,
"Hafsat, wai me yake damunki ne, kukan nan naki yayi yawa kuma nasoma zargin cewar akwai abinda ke saki kukan, ki fada min gaskiya karki boye min.."
"Mami babu komai, wallahi babu abinda ke damuna, wannan kukan ni kaina ban san meyasa nake yinsa amma nasan bazai rasa nasaba ba da accident din da naga anyi rannan ba"
"To hafsat ai sai hakuri, haka rayuwar take sai dai Allah yasa mucika da imani, ki shirya anjima mijinki zai zo ya daukeki ku tafi.."
"To mami.."
Ai mami nafita hafsat ta rushe da kuka saboda yanzu ita bata son ganin yusleem kwata kwata kuma da alama shima yagane haka domin tun rannan bai sake rab'ar inda takeba.
Misalin karfe 8 nadare yazo daukarta, kuka mami ta sameta tanayi nan hankalinta yatashi ta fara tambayarta,
"Hafsat ko wani abun yusleem din yake yi miki?"
Jijjiga kai tayi, "a'a mami babu abinda yake min"
"To ko bakya son komawa gidan nashi ne yabarki anan?"
"A'a mami zan koma"
Zama mami tayi agefenta,
"Hafsat kar muyi haka dake, ki fada min gaskiya idan har akwai abinda yusleem yake yimiki karki boye min"
"Wallahi mami babu komai, ni babu abinda ya taba yimin muna zaune lafiya dashi,kukan rabuwa dake kawai nakeyi mami da kuma irin soyayyar da kike nuna min nasan duk duniya nafi kowa yin sa'ar surika tagari mai sona"
Rungumeta mami tayi tasoma shafa kanta,
"To hafsat ai kema surakace tagari shiyasa dole in kaunaceki kuma wallahi ina sonki irin soyayyar da nake yiwa 'yayan da na haifa,yanzu dai shikenan tashi kizo muje dan yazo yana jiranki share hawayenki daina kukan"
Akwatin kayanta tadauka tareda yin karfin halin tsayar da hawayen dake zuba a idonta tafito suka fita da mami domin shi har yajima acikin motarsa,kasancewar ranar juma'a ne shiyasa yake sanye da dogayen kaya na ash colour din shadda mai tsadar gaske,
Fitowa tayi takama hanya zata fita tana zuwa gate din hotel din tahango motarshi tana dosowa kamar a mafarki babu shiri tajuya tabi ta bayan wasu bishiyoyi ta nemi mafaka duk da tasan ba lallai ne yaganeta ba saboda bazai taba tsammanin ganinta awurinba,
Tana ganinshi yafito bayan ya rufe motarshi ya nufi ciki yana yin waya yana sanye cikin kananan kaya, lababawa tayi tasoma binsa abaya abaya har zuwa ciki, akofar wani daki taga yatsaya mintuna kadan aka bude masa yashiga,batayi kasa agwiwa ba tabishi har kofar wannan dakin,
Tsayawa tayi tana tunanin ta ina ya kamata tafara, tafi minti goma atsaye daga karshe kawai ta nufi kofar ta murda abin mamaki abude tajita nan tashiga ahankali, wani dan madaidaicin falone wanda yacika da sanyin air condition, leken cikin bedroom din tafara yi amma kuma bata iya hango komai nan tadan tura kofar ahankali ta zira kanta ta leka, abinda tagani shine yayi sanadiyar sulalewarta awurin ta suma bayan ta kwalla kara mai mutukar firgitarwa.....
_Tofa ko me Hafsat tagani? Nidai Ummi Shatu banida wannan amsar..._
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*27*
***Ahankali tafara bude idanuwanta wadanda suka yi mata nauyi ga wani irin ciwo da kanta ke faman yimata kamar zai tsage,
Dishi dishi take gani kafin daga bisani ta dan fara ganin dishi dishin yana washewa har ya b'ace gaba daya,
Mami ta hango zaune saman wata kujerar roba ganin ta bude idonta yasa mamin matsawa gareta,
"Sannu Hafsat..., sannu kinji, Allah yabaki lafiya..."
Runtse idanuwanta tayi take wasu zafafan hawaye suka gangaro daga cikin idanuwanta, ko kadan bata burin ta sake ganin yusleem ayanda taganshi dazu kuma ko tunawa bata son ta kara yi domin wannan shine mafi munin gani da idanuwanta suka taba yi tunda tazo duniya,
"Sannu Hafsat, kukan me kikeyi kuma?" Mami ta tambayeta tana dafata,
"Kukan ciwo mami, kukan ciwo nakeyi mami ba kukan komai ba domin kaina wani nauyi naji yayi min banda azabar ciwon dake addabata..."
"Sannu, sannu Allah yabaki lafiya, ina zuwa bari inkirawo likita saboda yace idan kin bude idanuwanki inkirashi.."
Fita mami tayi daga cikin dakin nan Hafsat tasake mayar da idanuwanta ta rufe tana hawaye, a hakikanin gaskiya abinda tagani ne yasata wannan kukan bawai ciwon kan da take tareda shi yanzu bane,
Tana nan kwance tana hawaye taji shigowar mami da dr,
Gaban gadonta likitan yakarasa yakai hannunsa kan goshinta ya taba,
"Sannu, yanzu me kikeji yafi damunki?"
"Dr ciwon kai ne kadai ke damuna.."
"To insha Allah shima zai daina nan da dan wani lokaci.."
Dukufa likitan yayi yafara rubutu ajikin wani dan madaidaicin file saida ya kammala sannan yadago ya mikawa mami takardar,
"Ga magungunan da za asamo mata tasha bayan taci abinci, Allah yakara bata lafiya.."
Karbar takardar mami tayi shikuma likitan yasaka kai yafice daga cikin dakin,
Wayar yusleem mami tasoma nema ringing biyu zuwa uku ya dauka,
"Kana inane? Kai nake jirafa.."
Kashe wayar tayi batare da Hafsat tajiyo abinda yusleem din yafada ba,
Ba afi mintuna biyar da gama wayarsu da mami ba sai gashi ya turo kofa yashigo, kawar da kanta hafsat tayi daga gefen da yake ta mayar zuwa wani gefen,
"Wannan shine mijin kaddara..." Tafada acikin zuciyarta,
"Wai kai me yasameta? Inata tambayarka abinda yasameta harta suma haka amma kaki yimin bayani.."
"Yanzu dai mami ai ba lokacin yin wannan maganar bane, abinda kuke bukata nake son ji"
"To kaga dai magungunan da dr yace asiyo tasha bayan ta ci abinci amma gaskiya ni ina ganin idan har takara kwana biyar bataji sauki ba gara ka kaita chairo..."
Dan sajenshi ya shafa ya karbi takardar dake hannu mami,
"To shikenan bari nasamo drugs din indawo.."
Yana fita hajiya kubra na shigowa hannayenta dauke da babban basket din abinci,
"Hajiya siyama ya mai jikin? Nifa kalau muka rabu da ita saida ma nayi nayi da ita tajira salisu yadawo yakaita amma furr taki ashe tsautsayi ke janta.."
"Ehh haka Allah yake ikonsa ai, nima wallahi sai waya kawai yusleem yamin wai yakaita asibiti..."
Ajiye kayan hannunta hajiya kubra tayi ta matsa wurin Hafsat tana yimata sannu,
"Wai ya akayi haka tafaru? Hafsat garin yaya..?"
"Ummi kaddara da tsautsayi, nima ban san abinda ya sameni ba kawai jina nayi nafadi,shi lokacin da abin yafaru ma yana office inajin sai wayata aka dauka aka kirashi..." Ta karashe maganar hawaye na bin kuncinta,
"To Allah ya rufa asiri ya kiyaye gaba.."
"Amin summa amin, Allah yatashi kafadunta yabata lafiya..." Inji mami,
"Tashi kici abincin to, tuwon shinkafa ne miyar zogale.."
Dakyar Hafsat ta iya tashi ta zauna saboda irin yanda kanta ke tsananin sarawa, tafara cin abincin kenan yusleem ya shigo dauke da magungunan da likita ya rubuta mata,
"Mami gashi..."
"Yawwa ansamo, to bari tagama cin abincin sai tasha, ashe kaima baka gida lokacin da abun yafaru? Tace kana office sai awaya aka kiraka.."
Kallonshi Hafsat tayi domin taga irin yanda zai karbi maganar,
Shiru yayi baiyi magana ba saima bude kofa da yayi yafita,
Tunda yafita bata sake jin motsinshi ba,ita kanta tasan daren ranar bazata iya bacciba ba don Allah ya taimaka anhada mata da magungunan bacci ba acikin maganin da aka bata,
Tareda mami suka kwana a asibitin ita kuma ummi tatafi sai da safe ta dawo takawo musu abincin karyawa,
Kwananta uku a asibitin dr yace zasu iya tafiya gida, duk da ta dan samu saukin ciwon kan dake addabarta amma ta gagara daina kukan da takeyi wannan kam yazame mata kamar ibada wani lokacin sai suna zaune kalau sai kawai aga tana hawaye gashi daga mamin har Ummi sunyi tambayar duniya amma taki fada musu damuwarta wacce ke sata kukan,
Yanzun ma da zasu bar asibitin hawaye ne ke faman bin kuncinta ganin haka sai mami tace kawai hajiya kubra tatafi da ita gida ta dan sake warwarewa,
Tunda suka koma ummi ta tisata agaba tana yimata tambayoyi,
"Hafsat kin dai san yanzu aduniyar nan bakida wanda yafini daga ni sai Alhaji, ki sanar dani abinda yake damunki, idan baki fada minba wa kike dashi wanda zaki fadawa?"
Murmushin karfin hali Hafsat tayi,
"Ummi wallahi bafa kukan wani abu nakeyiba, kawai wani abin mamaki da ban tausayi nagani ranar da nabar gidan nan..."
"Me kika gani?"
"Ummi wata matace suke tafiya da yarta, tana rike da hannun yar fa yarinyar ta kwace ta ruga da gudu zata dauko wani abin wasa da ta hango ashe tsautsayi ne saiga mota tabi takanta gaba daya ta tanitseta, wannan abun shinefa ya hadda samin wannan suman da nayi..."
Dafata hajiya kubra tayi,
"Allah sarki Hafsat to ai dama idan ajali yayi kira ba makawa sai antafi, Allah yajikanta mukuma yasa mucika da kalmar shahada.."
"Amin Ummi"
Tashi hajiya kubra tayi tafita, tana fita Hafsat ta kifa kanta ajikin pillow tasoma kuka mai sauti domin da duk kukan zuci take yi wanda yafi nafili ciwo,
Kwananta biyu agida amma kullum sai mami tazo dubata yusleem ne kadai bai taba zuwa ba, aranar da tayi kwana uku mami tace tashirya su tafi inyaso idan takarasa warwarewa awurinta sai takoma gidanta, shiryawa tayi suka tafi gidan mamin nan mami tasoma bata dukkan kulawa domin dakin surayya tabata ta zauna aciki wanda yake dauke da dukkan abubuwan jin dadi irin wadanda ba agidan kowa ake samuba sai gidan wadanda suka amsa sunansu masu naira,
Dukkan abinda take so shi ake Kawo mata domin ga ma'aikata nan agidan kashi kashi ita kanta mamin babu abinda takeyi sai dai idan tana bukatar abu tayi waya kawai akawo mata shiyasa koda yaushe cikin ado zaka sameta tasha kwalliyarta ta zubawa jikinta gwala gwalai,
Dawowarta gidan mamin ma bai hanata daina kukan da ya zame mata jiki ba domin kullum cikin yinsa take,
Kwananta biyar agidan mamin amma bataga yusleem ba nan tafara tunanin to kodai tafiya yayi ne?
Tana cikin wannan tunanin tajiyo maganar mami a falo kuma da alamu yusleem dinne yazo, runtse idonta tayi tafara zubar da hawaye wanda har mami tashigo bata san tashigo ba,
"Hafsat, wai me yake damunki ne, kukan nan naki yayi yawa kuma nasoma zargin cewar akwai abinda ke saki kukan, ki fada min gaskiya karki boye min.."
"Mami babu komai, wallahi babu abinda ke damuna, wannan kukan ni kaina ban san meyasa nake yinsa amma nasan bazai rasa nasaba ba da accident din da naga anyi rannan ba"
"To hafsat ai sai hakuri, haka rayuwar take sai dai Allah yasa mucika da imani, ki shirya anjima mijinki zai zo ya daukeki ku tafi.."
"To mami.."
Ai mami nafita hafsat ta rushe da kuka saboda yanzu ita bata son ganin yusleem kwata kwata kuma da alama shima yagane haka domin tun rannan bai sake rab'ar inda takeba.
Misalin karfe 8 nadare yazo daukarta, kuka mami ta sameta tanayi nan hankalinta yatashi ta fara tambayarta,
"Hafsat ko wani abun yusleem din yake yi miki?"
Jijjiga kai tayi, "a'a mami babu abinda yake min"
"To ko bakya son komawa gidan nashi ne yabarki anan?"
"A'a mami zan koma"
Zama mami tayi agefenta,
"Hafsat kar muyi haka dake, ki fada min gaskiya idan har akwai abinda yusleem yake yimiki karki boye min"
"Wallahi mami babu komai, ni babu abinda ya taba yimin muna zaune lafiya dashi,kukan rabuwa dake kawai nakeyi mami da kuma irin soyayyar da kike nuna min nasan duk duniya nafi kowa yin sa'ar surika tagari mai sona"
Rungumeta mami tayi tasoma shafa kanta,
"To hafsat ai kema surakace tagari shiyasa dole in kaunaceki kuma wallahi ina sonki irin soyayyar da nake yiwa 'yayan da na haifa,yanzu dai shikenan tashi kizo muje dan yazo yana jiranki share hawayenki daina kukan"
Akwatin kayanta tadauka tareda yin karfin halin tsayar da hawayen dake zuba a idonta tafito suka fita da mami domin shi har yajima acikin motarsa,kasancewar ranar juma'a ne shiyasa yake sanye da dogayen kaya na ash colour din shadda mai tsadar gaske,