← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 30

Sashe 15

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da haushin wannan abun ta wuni da yamma sai gashi ya shigo cikin part dinta yana sanye cikin farar shadda mai mutukar kyau da tsada dinkin tazarce sai jar hula da yasaka,hannunsa daure da agogon fata fari kafarshi kuma yasa farin takalmi half cover tsaf dashi fadin irin kyan da yayi abun ba acewa komai,ita bama tafiya ganinshi da dogayen kayaba sai dai idan ranar juma'a ce tayi wannan kam yanasa manyan kaya amma idan bahaka ba kullum cikin kananan kaya yake,

"Zanyi tafiya zanje America daga can zan wuce India saboda akwai likitan da zan gani acan,idan akwai abinda kike bukata ki duba cikin bedroom dina akwai kudi..." Yace da ita cikin muryarsa mai sanyi,

"Allah ya kiyaye hanya yadawo dakai lafiya"

Bai amsaba yajuya yafita,bayan tafiyarshi part dinshi taje ta shiga bedroom dinshi tahau binciki wai ko zataga wata alama wacce zata tabbatar mata da gaskiyar abinda take zargi amma babu abinda tagani haka ta hakura ta mayar da dakin ta gyara ta fita,

Washe garin tafiyarshi mami ta turo driver ya dauketa can ta zauna har tsawon sati 2 sai ana gobe zai dawo sannan takoma gidanta kuma sosai taji dadin zama tareda mami domin tana mutukar kaunarta tareda kulawa da ita,

Tunda yadawo take bibiyarsa tana fakonsa saboda so take sai tagane inda yake zuwa cikin dare da abinda yake yi, kullum bata bacci har tsawon kwana biyar da dawowarsa saida ta sakankance ranar da tayi bacci aranar ya fita daf da asuba kuma sai gashi yadawo,

Wani haushine ya cika mata ciki gashi kuma tun daga ranar bai kuma fitaba, duk da haka bata hakura ba haka taci gaba da saka masa ido,

A wata ranar lahdi har zata kwanta sai tajiyo motsinsa, tashi tayi ta sadada tafita har yabude motar zai shiga ko me ya tuna oho sai yafasa yanufi ciki amma dai yabar motar a bude, ganin haka yasata lallabawa tabude bayan motar tashiga ta makure ta buya,

Tafi mintuna talatin aciki bai dawoba, tana shirin fita sai taji alamun tahowarsa nan takoma tasake makalewa ta yadda bazai ganta ba,

Shiga cikin motar yayi yatadata ahankali ya murza ya doshi gate din fita.......

_Sakon fatan alkhairi ga yan group din Duniyar littattafan Hausa, tabbas kunfi kowa son alwashi..._

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

_Kuna ina? Members na zauren karatu group, wannan page din yau nakune ku kadai domin jin dadinku, soyayyarku gareni ta musamman ce, ina yinku kamar yadda kuke yina....!_

*26*

***Sake lafewa Hafsat tayi a lungun kunjerun baya wato wurinda ake ajiye kafa, tana jinsa yana driving din yana dan jan karamin tsaki, titin emirs palace yahau,

Gaba daya garin tsitt yake babu motsin kowa sai haushin karnuka wadanda idan sun ji motsi suke kaurewa da yi,

Wayarshi ce tadanyi kara nan taga ya dauka yakara a kunnensa, cikin sansanyar muryarshi taji yace,

"Am on my way...." Wani dan tsakin yaja bayan ya kammala wayar ya ajiye,

Haka yaci gaba da yin driving ahankali shi kadai atsakiyar titi domin hatta jami'an tsaro masu yin patrol sun gama aikinsu sun tafi,ita mamakinshi ma takeyi ganin ko tsoro bayaji shi kadai a titi kamar aljani,

Wata hadaddiyar atishawa ce ta tahowa Hafsat batare data shirya ba nan tayi hanzarin toshe bakinta da hancinta amma duk da haka saida yar kararta ta fita,

"Atshhh..."

Jin sautin yasa yusleem wanda ke yin driving dan juyowa nan tayi saurin sake kwantawa abayan kujerar, maida kallonsa titi yayi yaci gaba da tukinshi,

Jin alamun yatsaya yasata dan dago kanta domin ganin ko inane, bata san ko ina bane amma tana dan iya jiyo maganganun mutane, dukar da kanta tayi har saida taji fitarsa sannan ta dago tafara kallon wurin,

Wani babban hotel ne mai tsananin kyau wanda yakeda fiyeda hawa 20,harabar wurin kadai ta isheka nishadi da kallo domin itama kawace take da abubuwan saka nishadi, wurin haske ne tarwal kamar rana sannan ga mutane nan sunata hada hadarsu mata da maza,

Hango yusleem tayi ya nufi cikin hotel din nan tayi yunkurin binshi amma abin haushi ya kulle motar kuma babu yadda zatayi ta iya budeta domin motar tashi ba kamar sauran motoci bane, motarshi motace mai tsada wacce ta amsa sunanta domin ko a zagayen garin bata tunanin akwai wanda yake da irinta,

Dukan kujera tayi cikeda haushi, damuwa gamida bacin rai domin taso ace tabishi abaya taga karshen gudun ruwansa,

Tana nan zaune tana kallon yanda mata da maza ke zuwa suna shiga cikin hotel din kamar bazasu kareba domin maimakon ma su ragu sai sake karuwa suke,

Tagumi Hafsat tayi aranta tana tunanin ko mahukunta suna ina hakan take faruwa?,

Tana nan zaune tana jiran taga ta inda yusleem zai bullo amma shiru sai misalin karfe 5 saura sannan ta hangoshi yana fitowa daga cikin hotel din, saurin komawa maboyarta tayi ta lafe, saida yadan jima awaje bata san me yatsaya yiba sannan yabude motar yashiga ya tadata,

Tana jinsu suka hau titi suka nufi unguwarsu, karar bude gate taji alamun sun iso gida lokacin anfara shiga masallaci sallar asubah,

Kasancewar gidane yasa yusleem bai kulle motar ba fita kawai yayi yatura kofar yanufi ciki, saida yajima da fita sannan hafsat ta lallaba ta fita,

Ganin kamar giftawar mutum yusleem yayi lokacin da yake tsaye agaban window dinshi bayan yadauro alwala, da sauri yafita yabi ta kofar da zata sadashi da part din hafsat,

Bai taba shiga bedrooms dinta ba sai yau, wannan shine karo nafarko da yataba takawa zuwa dakunan barcinta,

Bedroom din farko yafara shiga nan babu kowa aciki har cikin toilet yaduba amma babu kowa, rufe dakin yayi yakarasa dayan yana shiga tana fitowa daga bathroom da alama alwala tayi,

Ganinta yasashi juyawa yafita, dan lekashi Hafsat tayi,

"Ohh Allah, Allah kasa dai ba ganewa yayiba.." Tafada acikin zuciyarta,

Tana idar da salla ta kwanta ramuwar baccin da bata samu tayiba tunda ta kwanta kuma ba ita ta tashiba sai misalin karfe 10 nasafe, wanka tayi tashirya tasaka wata doguwar riga ta leshi pink colour da stones ajiki, kitchen tashiga ta dora breakfast sannan ta dafawa yusleem tea tanayi tana addu'ar Allah yasa karya gwasaleta,

Saida ta kammala yin breakfast dinta taci sannan ta dauki nashi ta nufi part dinshi,

Yana kwance akan tsakiyar fankamemen gadonshi yana ta bacci, abisa dukkan alamu har yanzu bai tashiba,

Dan karamin stoll tajawo ta dora masa akai ta tsaya tana kallonsa,

"Menene kika tsaya min aka kina kallona??" Taji yafada batare da ya bude idonsa ba, ita tsorata ma tayi saboda ganin tun lokacin data shigo dakin idanuwanshi a rufe suke,

"Ahhh babu komai..., dama breakfast nakawo maka.."

Murmushi taga yayi akaro nafarko tsakaninta dashi domin tun ranar data fara ganinsa bata taba ganin murmushinsa ba sai yau,

"Shiga toilet ki hada min ruwan wanka.."

Taji yasake fada ahankali,

"Toh" bude bathroom dinshi tayi tashiga, saida tafara dauraye toilet din sannan ta hada mishi ruwa acikin bathtub tasaka salt nawanka da turaren wanka domin duk gasu nan tanade asaman wata yar madaidaiciyar kanta wacce ke daure ajikin bangon toilet din,

Lokacin da tafito atsakar dakin ta sameshi yana tsaye yana yin mika nan tabashi hanya yawuce yashiga ita kuma tasoma gyaran dakin tana yi tana yan kalle kalle ko Allah zaisa idanuwanta su gane mata wani abu, har kasan gado ta leka amma babu abinda tagani,

Tana kammala gyara dakin shi kuma yana fitowa fita tayi tabashi wuri domin yashirya, a falonshi ta zauna tana nan zaune har yafito,zama yayi ya dauki remote ya kunna tv,

Ita dai Hafsat tana zaune tana binsa da kallo duk inda ya motsa, har azahar tayi bata bar falonba saida taga yafita salla sannan taje takwashe kayan da ta kawo masa breakfast aciki takoma part dinta amma data kammala lunch ma can tasake komawa sukaci gaba da zaman kurame.

Abin mamaki tamkar yasan shirin da Hafsat keyi akansa ko kuma yanada masaniyar abinda take shirin yi sai ya canja taku, acikin kwanakin gaba daya baiyi fitar dareba sai dai amma idan yafita kafin sallar magrib baya dawowa sai 1 ko 12:30,kuma ranakun suna dan sassabawa domin wata ranama da rana yake fita to bazai dawoba sai 1 wata rana kuma tun safe idan yafita office baya dawowa sai 12 wata rana kuma sai yayi zamansa agida ko nan da kofar gida bazai fitaba sai dai idan time din salla yayi yafita yaje masallaci yadawo, gaba daya yasa Hafsat acikin wani yanayi domin takasa fahimtar ta inda zata gano abinda yake aikatawa aboye wanda abisa dukkan alamu babu Wanda yasani,

Yafi sati biyu yana wannan shifting din daga rana zuwa dare ko kuma daga yamma zuwa dare,

Ganin kamar idan aka cigaba da haka Hafsat bazata samu abinda takeso ba yasata yimasa dabara,

Tea ta dafa masa takai mishi ta zauna acan nesa dashi, saida yadawo daga sallar azahar sannan yasha, nan yaji duk kasala ta rufeshi, wannan dalilin ne ya hanashi fita gaba daya ranar domin har salla agida duk yayi,

Karfe 2 nadare daidai yayi shirin fita nan yaje wurin da yake ajiye keys din motocinshi yasoma dubawa, yayi neman duniya amma baiga na BMW dinshiba shikuma yafi son yaje da ita domin sabuwar motace dan haka ba kowa bane yasanshi da itaba sabanin sauran motocinshi,

Wani key din yadauka yafita, Hafsat da tun jimawa take cikin bayan motar a boye tasake gyara buyan da tayi ganin ya nufo parking space din amma abin haushi koda yazo sai taji ba motar da take ciki yashiga ba wata daban yabude yashiga yayi reverse zai fita haushi ne ya cika mata ciki domin fa saboda haka ta dauke key din BMW dinshi ta boye saboda kar taje yasake kulleta kamar yadda yayi mata rannan tanaji tana gani yafice daga gidan batare data bishiba,

Ciki takoma tana cizon yatsa wato duk shirin data dade tanayi Yatashi abanza kenan,tsabar takaici bata ma san lokacin da yadawo ba.

Ganin tarasa mafita yasata tambayarshi cewar zataje gidansu bai hanataba kamar yadda tayi tsammani dama, koda taje gidan acan tawuni amma yamma tanayi tacewa Ummi tafiya zatayi, nan ummin tayi tayi da ita akan tajira salisu driver yadawo yakaita amma taki,
Chapter 15 · 0% Book details