Sashe 20
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yusleem kayi gaggawar kashe wayarka domin su oga nemanka suke ido rufe, idan baka kashe wayarka ba zasuyi tracing wurinda kake..." Wannan shine abinda kunnuwan yusleem suka ji wanda bai gane ko muryar waye ba kitt yaji wayar takatse nan yakashe wayar gaba daya,
Sam baya son Hafsat taji bare hankalinta yatashi nan yaki fada mata gaskiyar abinda yake faruwa domin tun lokacin data fita suke fafatawa shida abokan harkar tasa domin sun ce mutukar yace yabar wannan harkar to sai dai wani bashi ba saboda sun san tona musu asiri zaiyi,
Jin baice komai ba yasa Hafsat bata Kawo komai acikin ranta ba daga karshema tashi tayi ta kunna candle tahau keken sakarta tafara saka kayan sanyi na yara, sai wurin 12 sannan ta hakura ta kwanta.
Washe gari dakyar da dabara yusleem yabarta tafita, wurin masu siyan kayan nan da sukayi alkawarin siyan kujerunta ta nufa daga can suka wuce gidan yusleem nada tabude musu sukaje suka gani, ganin kyawun kayan da irin tsaruwar gidan sai masu siyan kayan suka nemi fasawa domin gani suke kamar karya take banata bane ko kuma ba mallakinta bane dakyar tashawo kansu akayi cikini dubu 50 suka siya duk da kayan sun wuce haka,
Fita sukayi da kujerun tamayar gidan ta rufe ta nufi kasuwa da kudin, komai da tasan zasu bukata na kayan abinci saida ta siya musu, data gama siyayyar kuwa adaidaita sahu ta nema ta zuba kayan yakaita har kofar gida.
Yusleem na kwance agefen katifa bayan ya kammala dafa musu ruwan zafi wanda zasu sha tea sai gata tashigo niki niki da kaya, manyan idanuwanshi yazuba mata,
"Daga ina haka?"
"Ina zuwa yaya yusleem ai zan fada maka"
Tashi yayi ya taimaka mata suka karasa shigo da kayayyakin,
Kudin hannunta ta ajiye ta zare hijabin jikinta ta zauna,
"Yaya yusleem nagaji sosai gashi ina jin yunwa"
"Bari inhada miki tea.."
Kafada ta makale,
"Gaskiya ni bazan sha tea da wannan uban zafinba, tunda ga kayan abinci sai ka dafa min abinci inci"
"To ai baki fada min a inda kika samo wadannan kayan abincin ba.."
"Zan fada maka kafara bani abinci inci tukunna mana"
"Nifa ban iya girki ba sai dai kiyi guiding dina"
"To fara kunna risho din ka mayar da ruwan zafin can ka dora.."
Kamar yadda tace haka yayi, yanayi tana kwatanta mishi har yadafa musu farar taliya yasoya mai,
Acikin filet ya zuba musu yakai gabanta inda take kwance, hannunshi ya mika mata amma sai tayi kamar bata ganiba ta tashi zaune cikeda kunya,
Saida suka gama cin abincin sannan ta fada mishi duk yanda akayi,
"Yanzu ga 10 thousands din wannan alhajin cikon kudin hayarshi idan yazo sai abashi, wannan kuma 9 thousands din sai mu ajiye.."
Rasa abinda zaice yayi yatsaya kawai yana kallonta saboda yasan acikin mata dari dakyar za asamu irinta guda goma, Hafsat tayi masa halacci acikin rayuwarsa, ta rufa masa asiri, tayi sanadiyyar fitarshi daga cikin halaka, gashi tana zaune dashi a lokacin da bashida madafa har tana salwantar da abubuwan data mallaka saboda shi,
"Nanah banida bakin da zan gode miki illah..."
Tashi tayi tabar dakin ta wuce toilet saboda bata son yayi mata godiyar abinda tayi,
Cikin dare ta tasheshi tana makale da cikinta saboda wani irin ciwo mararta keyi mata, riketa yayi acikin duhun da suke yana tambayarta menene,
"Yaya yusleem cikina ne yake ciwo"
"Ciki kuma? Sannu to yi hakuri"
"Bani ruwa insha.."
Ruwa ya Kawo mata takarba tasha takwanta, candle ya kunna yajata jikinshi yadora kanta akirjinshi ya rungumeta yasoma rarrashinta hannunshi yakai kan cikin nata nan tayi saurin ture hannun,
Kwanciya luff tayi ajikinshi sakamakon duk gabobinta ciwo suke yimata, tambayar duniya yayi mata akan tafada mishi abinda yasa mata ciwon cikin amma tayi shiru saboda kunya takeji tace mishi period pain ne,
Ajikinshi ta kwana har asuba tayi sai lokacin tasamu saukin ciwon da marar tata keyi bacci yadan dauketa kwantar da ita yayi ya nufi toilet,
Sai wurin karfe 6 sannan tatashi daga baccin nan tarasa yadda zatayi tana son tafada mishi kuma tana kunya, komawa tayi ta kwanta ta kalleshi,
"Yaya yusleem kira min amir dan gidan maman amir.."
"Meya faru?"
"Aikenshi zanyi.."
"Toh bari naje"
Tashi yayi yafita ita kuma ta rakashi da ido...
*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*31*
****Bai wani jima da fitaba sai gashi yadawo, kusa da ita yakarasa ya tsugunna agabanta,
"Su maman amir din basu bude kofar su ba inaji basu tashiba.."
Gyada mishi kai tayi taja bargo zata lulluba, rike bargon yayi,
"Kitashi kiyi salla mana kafin kisake kwanciya"
Shiru tayi masa tasake yunkurin lulluba, kara maimaita maganarshi tafarko yayi,
"Ba yanzu ba.."
Ganin ta dage taki tashi yasashi rabuwa da ita tasake lulluba takoma barci, gefenta yaje ya kwanta,
K'arfe 8 tafarka ta kalli yusleem wanda ke gefenta akwance,
"Yaya yusleem dubo min ko su Maman amir din sun tashi.."
Tashi yayi yafita jim kadan sai gasu sun dawo tareda amir din,
"Yaya akwai biro awurinka?"
"A'a babu"
"Amir jeka wurin ummanka kace tabani aron biro da yar paper kaji"
Tafada tana ciccije lebenta, fitar amir tasa yusleem komawa wurinta,
"Har yanzu ciwon ne?"
Daga mishi kai tayi,
"To ko asibiti zamuje?"
"A'a"
Shigowar amir yasa sukayi shiru dukkaninsu, karbar takarda da biron tayi tana daga kwance ta rubuta mishi abinda zai siyo mata ta kalli yusleem,
"Yaya yusleem bashi dari biyu acikin kudin nan"
Tashi yusleem yayi yadauko kudin yabashi, sake gyara kwanciyarta tayi ta tukunkuna har amir yadawo kasancewar yusleem yana tsaye bakin kofa yasa amir bashi ledar pad din,karba yusleem yayi ya leka cikin ledar, sai yanzu ya fahimci abinda yake damunta,
Tana kokarin tashi domin yin wanka ya dakatar da ita,
"Tsaya indafa miki ruwan zafi sai kiyi wankan dashi zaki fi jin dadin jikinki"
Komawa tayi tasake kwantawa shikuma ya dora mata ruwan zafin bayan ya kunna risho,
Bathroom yashiga ya dauko bucket yazo ya juye mata ruwan aciki yakai mata cikin toilet tareda sirka mata shi,
"Ga ruwan wankan can nakai miki, tashi kije kiyi"
Dakyar ta tashi tajuya ta dan kalleshi ganin ba ita yake kalloba hankalinsa yana kan ruwan da zai sake maidawa ya tafasa yasata saurin tashi bayan taja zanin wankanta tashige cikin bathroom.
Bata dade sosai ba tafito lokacin har yusleem ya kammala hada musu abinda zasu karya dashi, kallonshi take kasa kasa saboda duk yau atakure take,shi kansa ya fahimci haka shiyasa ma yajuya mata baya bayan ya kwanta bisa katifa,
Ganin baya kallonta yasata dan sakewa tashirya tasaka wata blue din atamfa dinkin riga da skirt wanda dayane daga cikin irin dunkunan da mami tayiyyi mata,
Zama tayi abakin katifa wanda yayi sanadiyyar juyowar yusleem,
"Kin gama?"
"Uhm" tabashi amsa,
Tashi yayi ya debo mata tafasasshen ruwan zafi acikin cup,
"Kisha wannan ruwan zafin zai dan rage miki radadin ciwon da marar taki keyi"
"Ni ba ciwon Mara nakeba ciwon cikine"
Murmushi yayi ya mika mata cup din,
"Ashe dai ke dinma kin iya karya ban saniba, meye hadin period da ciwon ciki? Ai nazaci mahaifa a mara take ba acikin cikiba ko ke taki acikin ciki take?"
Karbar cup din tayi tasoma kurbar ruwan zafin batare da tayi magana ba har saida ta shanye,
"To ga abinci kuma taliya"
Girgiza masa kai tayi ta kwanta babu jimawa sai bacci, rasa abinda zaiyi yayi saboda dama idan tana ido biyu ne suke yin yar hira, shi dinma kwanciyar yayi tun yana yan tunane tunane har bacci ya daukeshi,
Hafsat ce tafara farkawa yanzu taji dadin jikin nata sannan kuma ciwon ma yaragu sosai sai kadan kadan, ganin yusleem din bacci yake yasata zuba abincin ita kadai ta danci tana gamawa yatashi, fita tayi tace mishi zataje wurin maman amir,
Dayake mata babu wuyar sabo tunda taje suke hira da maman amir din kasancewar itama mijinta baya nan dama kuma police ne,
Yau duk taki sakewa ta zauna wuri daya da yusleem saboda kawai yagane abinda ke damunta, da tashiga dakin zata fice takoma wurin maman amir shi kanshi yusleem din ya lura da ita,
Tun azahar da tashiga wurin maman amir sai yamma lis tadawo wannan dinma dan wanka zatayi ne, yana kwance ta shigo taki kallon inda yake tadauki abinda zata dauka tashiga wanka bakar ledar da tasaka pad din data cire da rana taga ya dauke yadora akan window din bathroom din, acikin toilet din tashirya dan haka koda tafito iya kaya kawai tasa tashafa dan mai tagama tafita.
Wasa wasa har karfe 8 nadare tana dakin maman amir saboda ita so take sai yusleem yayi bacci sannan zata koma dakin, shi kuma yau duk kadaici yakeji saboda bata cikin dakin ganin har 8 ta dan gota yasashi fita yanufi dakin maman amir daidai lokacin da aka dan fara yayyafi yif yif alamun ruwa yana daf da tsinkewa,
Abakin kofar dakin yatsaya,ahankali yayi magana,
"Nanah..!"
"Na'am"
Hafsat ta amsa tareda tashi, kallonta maman amir tayi,
"A'a keda wa? Banji magana ba sai ji nayi kawai kin amsa"
"Yaya yusleem ne yake kirana"
"Anya kuwa? Kodai kunnenki ne"
"Wallahi shine, bari inje"
Duk da haka maman amir bata yarda ba saida ta leka nan taga ashe shidinne kuwa yana tsaye akofar dakin,
"Lahh ashe dagaske shine, kinga kuwa ni banji maganarshi ba, mijin naki ne ma ni sai inga kamar baya magana"
"Dama ai nafada miki shine, bari inje, saida safe"
Fita tayi lokacin har ruwan yadan soma karfi, wucewa yayi tabishi abaya, suna shiga daki yajuya ya kalleta,
"Da ban kiraki ba sai yaushe zaki dawo?"
"Sai anjima"
"To ke haka akeyi mata da mijinta kije ki zauna musu adaki tun rana"
"Mijin nata fa baya nan"
"To amma ai ke naki mijin yana nan ko? Shine zaki kama hanya kitafi kibarshi"
Shiru tayi bata amsaba, maimakon ma tazauna sai kawai ta dauki kayan baccinta tanufi toilet, shi yau yarasa wacce irin kunya takeji sam taki sakewa dashi shikuma yafi son tasaki jiki dashi sosai tadaina jin kunyarshi,
Yana nan zaune tafito sanye da rigar bacci wacce tadora zani da hijab akai,
"Ga abinci nan ko zaki ci"
Girgiza masa kai tayi, "Allah nakoshi tun abincin da naci da rana"
Sam baya son Hafsat taji bare hankalinta yatashi nan yaki fada mata gaskiyar abinda yake faruwa domin tun lokacin data fita suke fafatawa shida abokan harkar tasa domin sun ce mutukar yace yabar wannan harkar to sai dai wani bashi ba saboda sun san tona musu asiri zaiyi,
Jin baice komai ba yasa Hafsat bata Kawo komai acikin ranta ba daga karshema tashi tayi ta kunna candle tahau keken sakarta tafara saka kayan sanyi na yara, sai wurin 12 sannan ta hakura ta kwanta.
Washe gari dakyar da dabara yusleem yabarta tafita, wurin masu siyan kayan nan da sukayi alkawarin siyan kujerunta ta nufa daga can suka wuce gidan yusleem nada tabude musu sukaje suka gani, ganin kyawun kayan da irin tsaruwar gidan sai masu siyan kayan suka nemi fasawa domin gani suke kamar karya take banata bane ko kuma ba mallakinta bane dakyar tashawo kansu akayi cikini dubu 50 suka siya duk da kayan sun wuce haka,
Fita sukayi da kujerun tamayar gidan ta rufe ta nufi kasuwa da kudin, komai da tasan zasu bukata na kayan abinci saida ta siya musu, data gama siyayyar kuwa adaidaita sahu ta nema ta zuba kayan yakaita har kofar gida.
Yusleem na kwance agefen katifa bayan ya kammala dafa musu ruwan zafi wanda zasu sha tea sai gata tashigo niki niki da kaya, manyan idanuwanshi yazuba mata,
"Daga ina haka?"
"Ina zuwa yaya yusleem ai zan fada maka"
Tashi yayi ya taimaka mata suka karasa shigo da kayayyakin,
Kudin hannunta ta ajiye ta zare hijabin jikinta ta zauna,
"Yaya yusleem nagaji sosai gashi ina jin yunwa"
"Bari inhada miki tea.."
Kafada ta makale,
"Gaskiya ni bazan sha tea da wannan uban zafinba, tunda ga kayan abinci sai ka dafa min abinci inci"
"To ai baki fada min a inda kika samo wadannan kayan abincin ba.."
"Zan fada maka kafara bani abinci inci tukunna mana"
"Nifa ban iya girki ba sai dai kiyi guiding dina"
"To fara kunna risho din ka mayar da ruwan zafin can ka dora.."
Kamar yadda tace haka yayi, yanayi tana kwatanta mishi har yadafa musu farar taliya yasoya mai,
Acikin filet ya zuba musu yakai gabanta inda take kwance, hannunshi ya mika mata amma sai tayi kamar bata ganiba ta tashi zaune cikeda kunya,
Saida suka gama cin abincin sannan ta fada mishi duk yanda akayi,
"Yanzu ga 10 thousands din wannan alhajin cikon kudin hayarshi idan yazo sai abashi, wannan kuma 9 thousands din sai mu ajiye.."
Rasa abinda zaice yayi yatsaya kawai yana kallonta saboda yasan acikin mata dari dakyar za asamu irinta guda goma, Hafsat tayi masa halacci acikin rayuwarsa, ta rufa masa asiri, tayi sanadiyyar fitarshi daga cikin halaka, gashi tana zaune dashi a lokacin da bashida madafa har tana salwantar da abubuwan data mallaka saboda shi,
"Nanah banida bakin da zan gode miki illah..."
Tashi tayi tabar dakin ta wuce toilet saboda bata son yayi mata godiyar abinda tayi,
Cikin dare ta tasheshi tana makale da cikinta saboda wani irin ciwo mararta keyi mata, riketa yayi acikin duhun da suke yana tambayarta menene,
"Yaya yusleem cikina ne yake ciwo"
"Ciki kuma? Sannu to yi hakuri"
"Bani ruwa insha.."
Ruwa ya Kawo mata takarba tasha takwanta, candle ya kunna yajata jikinshi yadora kanta akirjinshi ya rungumeta yasoma rarrashinta hannunshi yakai kan cikin nata nan tayi saurin ture hannun,
Kwanciya luff tayi ajikinshi sakamakon duk gabobinta ciwo suke yimata, tambayar duniya yayi mata akan tafada mishi abinda yasa mata ciwon cikin amma tayi shiru saboda kunya takeji tace mishi period pain ne,
Ajikinshi ta kwana har asuba tayi sai lokacin tasamu saukin ciwon da marar tata keyi bacci yadan dauketa kwantar da ita yayi ya nufi toilet,
Sai wurin karfe 6 sannan tatashi daga baccin nan tarasa yadda zatayi tana son tafada mishi kuma tana kunya, komawa tayi ta kwanta ta kalleshi,
"Yaya yusleem kira min amir dan gidan maman amir.."
"Meya faru?"
"Aikenshi zanyi.."
"Toh bari naje"
Tashi yayi yafita ita kuma ta rakashi da ido...
*_Ummi Shatu_*👌🏻© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*31*
****Bai wani jima da fitaba sai gashi yadawo, kusa da ita yakarasa ya tsugunna agabanta,
"Su maman amir din basu bude kofar su ba inaji basu tashiba.."
Gyada mishi kai tayi taja bargo zata lulluba, rike bargon yayi,
"Kitashi kiyi salla mana kafin kisake kwanciya"
Shiru tayi masa tasake yunkurin lulluba, kara maimaita maganarshi tafarko yayi,
"Ba yanzu ba.."
Ganin ta dage taki tashi yasashi rabuwa da ita tasake lulluba takoma barci, gefenta yaje ya kwanta,
K'arfe 8 tafarka ta kalli yusleem wanda ke gefenta akwance,
"Yaya yusleem dubo min ko su Maman amir din sun tashi.."
Tashi yayi yafita jim kadan sai gasu sun dawo tareda amir din,
"Yaya akwai biro awurinka?"
"A'a babu"
"Amir jeka wurin ummanka kace tabani aron biro da yar paper kaji"
Tafada tana ciccije lebenta, fitar amir tasa yusleem komawa wurinta,
"Har yanzu ciwon ne?"
Daga mishi kai tayi,
"To ko asibiti zamuje?"
"A'a"
Shigowar amir yasa sukayi shiru dukkaninsu, karbar takarda da biron tayi tana daga kwance ta rubuta mishi abinda zai siyo mata ta kalli yusleem,
"Yaya yusleem bashi dari biyu acikin kudin nan"
Tashi yusleem yayi yadauko kudin yabashi, sake gyara kwanciyarta tayi ta tukunkuna har amir yadawo kasancewar yusleem yana tsaye bakin kofa yasa amir bashi ledar pad din,karba yusleem yayi ya leka cikin ledar, sai yanzu ya fahimci abinda yake damunta,
Tana kokarin tashi domin yin wanka ya dakatar da ita,
"Tsaya indafa miki ruwan zafi sai kiyi wankan dashi zaki fi jin dadin jikinki"
Komawa tayi tasake kwantawa shikuma ya dora mata ruwan zafin bayan ya kunna risho,
Bathroom yashiga ya dauko bucket yazo ya juye mata ruwan aciki yakai mata cikin toilet tareda sirka mata shi,
"Ga ruwan wankan can nakai miki, tashi kije kiyi"
Dakyar ta tashi tajuya ta dan kalleshi ganin ba ita yake kalloba hankalinsa yana kan ruwan da zai sake maidawa ya tafasa yasata saurin tashi bayan taja zanin wankanta tashige cikin bathroom.
Bata dade sosai ba tafito lokacin har yusleem ya kammala hada musu abinda zasu karya dashi, kallonshi take kasa kasa saboda duk yau atakure take,shi kansa ya fahimci haka shiyasa ma yajuya mata baya bayan ya kwanta bisa katifa,
Ganin baya kallonta yasata dan sakewa tashirya tasaka wata blue din atamfa dinkin riga da skirt wanda dayane daga cikin irin dunkunan da mami tayiyyi mata,
Zama tayi abakin katifa wanda yayi sanadiyyar juyowar yusleem,
"Kin gama?"
"Uhm" tabashi amsa,
Tashi yayi ya debo mata tafasasshen ruwan zafi acikin cup,
"Kisha wannan ruwan zafin zai dan rage miki radadin ciwon da marar taki keyi"
"Ni ba ciwon Mara nakeba ciwon cikine"
Murmushi yayi ya mika mata cup din,
"Ashe dai ke dinma kin iya karya ban saniba, meye hadin period da ciwon ciki? Ai nazaci mahaifa a mara take ba acikin cikiba ko ke taki acikin ciki take?"
Karbar cup din tayi tasoma kurbar ruwan zafin batare da tayi magana ba har saida ta shanye,
"To ga abinci kuma taliya"
Girgiza masa kai tayi ta kwanta babu jimawa sai bacci, rasa abinda zaiyi yayi saboda dama idan tana ido biyu ne suke yin yar hira, shi dinma kwanciyar yayi tun yana yan tunane tunane har bacci ya daukeshi,
Hafsat ce tafara farkawa yanzu taji dadin jikin nata sannan kuma ciwon ma yaragu sosai sai kadan kadan, ganin yusleem din bacci yake yasata zuba abincin ita kadai ta danci tana gamawa yatashi, fita tayi tace mishi zataje wurin maman amir,
Dayake mata babu wuyar sabo tunda taje suke hira da maman amir din kasancewar itama mijinta baya nan dama kuma police ne,
Yau duk taki sakewa ta zauna wuri daya da yusleem saboda kawai yagane abinda ke damunta, da tashiga dakin zata fice takoma wurin maman amir shi kanshi yusleem din ya lura da ita,
Tun azahar da tashiga wurin maman amir sai yamma lis tadawo wannan dinma dan wanka zatayi ne, yana kwance ta shigo taki kallon inda yake tadauki abinda zata dauka tashiga wanka bakar ledar da tasaka pad din data cire da rana taga ya dauke yadora akan window din bathroom din, acikin toilet din tashirya dan haka koda tafito iya kaya kawai tasa tashafa dan mai tagama tafita.
Wasa wasa har karfe 8 nadare tana dakin maman amir saboda ita so take sai yusleem yayi bacci sannan zata koma dakin, shi kuma yau duk kadaici yakeji saboda bata cikin dakin ganin har 8 ta dan gota yasashi fita yanufi dakin maman amir daidai lokacin da aka dan fara yayyafi yif yif alamun ruwa yana daf da tsinkewa,
Abakin kofar dakin yatsaya,ahankali yayi magana,
"Nanah..!"
"Na'am"
Hafsat ta amsa tareda tashi, kallonta maman amir tayi,
"A'a keda wa? Banji magana ba sai ji nayi kawai kin amsa"
"Yaya yusleem ne yake kirana"
"Anya kuwa? Kodai kunnenki ne"
"Wallahi shine, bari inje"
Duk da haka maman amir bata yarda ba saida ta leka nan taga ashe shidinne kuwa yana tsaye akofar dakin,
"Lahh ashe dagaske shine, kinga kuwa ni banji maganarshi ba, mijin naki ne ma ni sai inga kamar baya magana"
"Dama ai nafada miki shine, bari inje, saida safe"
Fita tayi lokacin har ruwan yadan soma karfi, wucewa yayi tabishi abaya, suna shiga daki yajuya ya kalleta,
"Da ban kiraki ba sai yaushe zaki dawo?"
"Sai anjima"
"To ke haka akeyi mata da mijinta kije ki zauna musu adaki tun rana"
"Mijin nata fa baya nan"
"To amma ai ke naki mijin yana nan ko? Shine zaki kama hanya kitafi kibarshi"
Shiru tayi bata amsaba, maimakon ma tazauna sai kawai ta dauki kayan baccinta tanufi toilet, shi yau yarasa wacce irin kunya takeji sam taki sakewa dashi shikuma yafi son tasaki jiki dashi sosai tadaina jin kunyarshi,
Yana nan zaune tafito sanye da rigar bacci wacce tadora zani da hijab akai,
"Ga abinci nan ko zaki ci"
Girgiza masa kai tayi, "Allah nakoshi tun abincin da naci da rana"