Sashe 29
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida sukaga tashinsu sannan suka bar airport din suka dunguma suka koma gida har khadija.
Bayan komawarsu gida harkokinsu sukai tayi amma da zarar hafsat tashiga daki sai taga kamar zataga yusleem, haka taitajin kewarsa har dare yayi, duk irin baccin da yacika mata ido amma lokacin da tazo ta kwanta sai taji ta kasa baccin kwata kwata, sai uban juyi data rinka yi tana tuno mijinta, dakyar tasamu bacci ya dauketa bayan dare ya raba.
Washe gari da safe bata samu damar fitowa da wuri ba sai wurin misalin karfe 11 lokacin da ta fito mami na shiri fita dama ita take jira,
"Hafsa ga breakfast can ni fita zanyi, ina son zanje gidan hajiya Sarah amma ba dadewa zanyi ba"
"To mami Allah ya kiyaye hanya sai kin dawo"
Fita mami tayi tatafi ita kuma ta nufi dining area, zama tayi ta karya duk da abincin bawani mai yawa taciba, falo tadawo tazauna ta kamo tashar b4u tana kalla domin zaman shiru babu dadi,
Har bacci yadan fara daukarta sama sama taji sallamar khadija wacce abisa dukkan alamu yanzu ta mayar da zuwa gidan kullum tamkar ibada,
Tashi zaune hafsat tayi tana murmushi,
"Sannu da zuwa.."
"Yawwa hafsa, ko mamin bata nan" inji khadija wacce ke sanye cikin wata doguwar riga ta atamfa,
"Ehh mami ta dan fita wallahi" hafsa tabata amsa bayan tatashi zaune,
Zama khadija tayi, bayan sun gaisa suka dan fara hira kadan kadan,
"Hafsa kowa yayi mamakin yadda akayi kika samu kan yusleem har kuka kai wannan lokacin tare, saboda yusleem baya iya zama da mace.."
Murmushi hafsa tayi,
"Baya zama da mace kamar ya? Aini ban san wannan labarinba ko a mafarki"
"To kuwa a lissafi kece mace ta fiyeda goma da ya aura, kuma saida ya sakeni sannan ya aureki, ni kinga bamufi wata biyarba tare"
Jijjiga kai hafsa tayi alamun tausayawa,
"Allah sarki, Allah yarufa asiri kin san ai dama lamarin aure sai hakuri domin shima rai gareshi..."
"Hakane amma nida ina zargin ko aljanu gareshi ko kuma da saninsa tsabar cin mutunci ne, shiyasa ma ni yanzu wallahi auren yagama fitar min daga raina domin kin san naji dadi shine gari bawai nasaba ba.."
"To ai ba duk aka taru aka zama dayaba khadija, sai kiga nan gaba kin samu inda zakiji dadin hankalinki ya kwanta..."
"Kayya hafsa, kin san ai duk wanda miciji ya sareshi to idan yaga tsumma gudu yake, hafsa arayuwar aurena tafarko ban tsinci komai ba face bakin ciki da bacin rai da takaici, shiyasa ko zan kara wani auren gaskiya ba yanzu ba sai zuciyata ta nutsu tukunna"
"Ubangiji Allah yazabi abinda yafi alkhairi, babu komai ai jarrabawa ce daga Allah"
"Amin.."
Haka sukaci gaba da yin hirarsu har azahar tayi sai lokacin khadija tatafi, tun daga wannan rana kuma kullum zatazo susha hirarsu da hafsat wani lokacin ma harda mami, ita hafsa tausayin khadija takeji domin irin labaran da take bata na kuncin rayuwa da rashin samun farin ciki wanda ta rinka fuskanta agidan aurenta nafarko, shiyasa take tausayinta domin tasan irin wannan rayuwar tunda itama tashiga makamanciyarta abaya, koda yaushe yanzu khadija tana gidan haka kuma idan bataje da safe ba to zataje da rana ko da yamma wani lokacin harda daddare ma zuwa take tamaida gidan mami kamar gidansu haka ta dauki hafsat a matsayin yar uwa kuma abokiyar shawara domin ko sabon bazawari tayi saita fada mata,
Yauma kamar kullum hafsa tana zaune tana tsifar kai ita kuma mami tana gyaran farcenta saiga khadijan tashigo da alama daga sch take domin karfe 2 saura narana,
Da mami kawai suka gaisa tahaye dining ta zubo tuwon shinkafa miyar zogale tadawo wurin hafsat ta zauna,
"To inbanda abinku kuma ga tsifar gashi ga abinci?" Mami tafada tana murmushi,
Dan kwali hafsat ta dauka ta rufe kanta, "bari inbarshi anjima na karasa idan tagama"
Tashi mami tayi ta shiga kitchen domin tajiyo buruntun kuku aciki,
Mami natashi khadija ta dubi hafsa dama da labari tazo mata,
"Hafsa inata son inbaki labarin wani guy Al'amin, saurayi ne fa amma yadage sai ya aureni duk da nace masa nataba aure"
Murmushi hafsat tayi, "to kibashi dama mana kigani, wallahi khadija kiyarda indai kinga baida problem"
Murmushi khadija tayi ta yanko laumar tuwo tasa abakinta,
"Shikenan zan gwada ingani, bari inyi sauri ma domin munyi dashi zaizo da yamma"
"To Allah ya tabbatar da alkhairi"
Saida khadija taji tayi nak sannan ta hada nata yanata tatafi, kullum hakace take faruwa domin acewarta dama gidan mami gidansu ne domin dama aminiyar mahaifiyarta ce.
Tunda yusleem yatafi basuji duriyarsa ba saida yayi sati biyu sannan yakira su murna ranar awurin mami da hafsa ba acewa komai, sun jima suna hira dashi yana yimusu bayanin abubuwan dake faruwa sannan sukayi sallama,
Haka da daddare ma saida ya kuma kira suka kwashe awanni shida hafsat suna hira, yanzu har tasan lokacin kiranshi domin kullum sai yakirasu da safe da daddare,
Satinshi 7 acan yafara shirye shiryen dawowa amma idan yadawo bayan wani lokaci zai sake komawa,
Hafsat tunda taji zai dawo tarasa inda zata cusa kanta dan murna wanda hatta mami saida ta fahimta, saloon mami takaita aka wanke mata gashinta aka gyarashi, bayan sun dawo gida mai kunshin dake yiwa mami tazo ta zane mata kafafunta da hannaye da bakin lallai mai adon ja,
Tarba ta musamman mami da hafsat suka shiryawa yusleem,karfe 3:30 jirginsu yasauka nan mami da driver suka tafi daukoshi banda hafsa wacce tazauna domin karasa girke girken da aka dora sabodayau tace itace zatayi girkin da yusleem zaici.....
_Gaisuwa da fatan alkhairi ga takwarata A'isha D/sabo..._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*46*
***Lokacin dasu mami suka dawo gidan hafsat tana cikin daki tana shiryawa, saida ta kammala sannan tayi sallar la'asar domin lokaci yayi,
Tana tsaye gaban mirror tana gyara fuskarta bayan ta idar da sallar ta hango wulgawar mutum ta cikin mirror atsorace ta juya amma abun mamaki bataga kowa ba, tsorata tayi takama hanya zata fita daga dakin taje falo wurinsu mami,
Ji tayi anyi mata wata irin damka, tuni numfashinta yafara neman daukewa, ajikin mutum tajita anrugumeta tabaya tayadda bazata iya ganin fuskar mutumin ba, kara taso fasawa amma ina bata samu zarafin yin hakanba domin ji tayi anrufe mata baki da abinda bata san ko menene ba sai daga baya sannan ta fahimci cewar da bakinshi ne,
Wani sanyayyen kamshi ne mai dadi yake ratsa kofofin hancinta gaba daya,
Sassauta rikon da yayi mata yayi ya dago da fuskarta yana kallonta,
"Nanah hafsat..."
Firgigit tayi tabude idanuwanta akan fuskarsa ganinshi yasata daka tsalle ta rungumeshi na tsawon wasu mintuna,
Riketa yayi yana dan juyi da ita ahankali, dago da fuskarta tayi ta kalleshi, tabbas yaya yusleem dintane amma kuma tamkar wanda aka canjashi domin farar fatarshi tasake haskawa farin yakaru, gashi fatar tashi tasake laushi lubus kamar ta jarirai, kyakkyawar fuskarshi kuma tasake cika da kyau, annuri, da farin ciki,
Ji tayi gaba daya tagama raina kanta saboda yusleem yafita tako ina ita sai take ganinma ayanzu haka ai bata da wani abu atare da ita wanda take ganin zata iya jan ra'ayinshi domin yafita kyau yafita komai na rayuwa,
Hancinta taji yaja domin har lokacin tana dale ajikinshi hannayenta sakale awuyanshi,
Bude idanuwanta tayi daga dogon tunanin data lula ta kalleshi, ji tayi ya rike fuskarta yana kokarin sake saita bakinshi akan nata, shi kansa bakin nashi da lips din dake jiki da fararen hakoran dake jere aciki tasan abin kallone, lumshe idonta tayi tana jiran taji saukar lips dinshi akan nata amma sai taji sabanin haka maimakon yayi kissing din bakinta sai tajishi asaman kirjinta, saurin tureshi tayi tasoma kokarin kwacewa tana dariya,
Riketa yayi shidinma yana yin dariyar kasa kasa,
"Bakiyi min ko sannu da zuwa ba.."
Tana shirin yin magana suka jiyo maganar mami tana nufo kofar dakin,
"Hafsa har yanzu baki idar da sallar bane? Idan kin idar kifito ki hada salad din saboda nace kuku yahada yace kece kika ce karya taba sai kin fito..."
Bude baki tayi zata amsawa mami amma takasa saboda shakewar da muryarta tayi, rufe mata baki da hannunshi yayi yabawa mami amsa da,
"Mami har yanzu fa bata idar da sallar ba.."
"To idan ta idar kafada mata, sannan ku fito muci abincin..."
"To mami..."
Saida ta tabbatar da cewar mami tatafi sannan ta kalleshi,
"Kuma da tashigo taganmu fa gashi kace mata wai salla nake yi.."
Murmushi yayi ya lakuce mata hanci,
"Ai bazata ma shigo ba saboda tasan nidake yau tamkar tif da taya zamu kasance...."
"To kazo muje kar taga mun dade tayi zargin ko wani abu muke yi.."
Murmushi yayi ya dauketa nan tasoma mutsu mutsu, ajiyeta yayi ta fice shikuma yashiga toilet yayi alwala yafito yayi salla,
A falo ya samesu ita da mami sun baje girke girken da aka wuni anayi saboda shi, akusa da mami ya zauna yana kallon hafsa wacce ke tsugunne tana hada salad wanda zasu ci abincin dashi,sai lokacin wai ya lura da kunshin dake hannunta duk hidimar dazu idonshi bai kai kan kunshin ba,
Tashi mami tayi zuwa kan dining domin debo wasu kwanuka,
Hannunshi yakai kan na hafsa,
"Ya akayi dazu banga kunshin nan ba sai yanzu? Koda yake ai ni yau dinne gaba daya amaryar tawa tagama rudani, ta dauke hankalina"
Murmushi hafsat tayi saboda jin abinda yace, janye hannunta tayi daga jikin nashi saboda taga mami na kokarin fitowa ganin haka shikuma ya wayance da lakuto salad din yakai bakinsa,
Kamar koda yaushe a cikin babban faranti yauma suka zuba abincin suka hadu suna ci, idan yusleem yafaki idon mami sai ya kwace abincin hafsa ya kai bakinsa,
Tun daga yanayin cin abincinsa mami da hafsa suka gane cewar lafiya ta samu domin yau yaci abinci sosai wanda rabon da yaci irinshi har anmanta,
Komai da suka girka saida yaci, kallonshi kurum hafsa keyi saboda ganin yanda ya bude ciki ya narki abinci,
Kan kujera yaje ya mike, mami na zaune kusa dashi suna dan yar hira dangane da tafiyarsa da dawowar tashi yana sanar da ita abubuwan da suka wakana,
Bayan komawarsu gida harkokinsu sukai tayi amma da zarar hafsat tashiga daki sai taga kamar zataga yusleem, haka taitajin kewarsa har dare yayi, duk irin baccin da yacika mata ido amma lokacin da tazo ta kwanta sai taji ta kasa baccin kwata kwata, sai uban juyi data rinka yi tana tuno mijinta, dakyar tasamu bacci ya dauketa bayan dare ya raba.
Washe gari da safe bata samu damar fitowa da wuri ba sai wurin misalin karfe 11 lokacin da ta fito mami na shiri fita dama ita take jira,
"Hafsa ga breakfast can ni fita zanyi, ina son zanje gidan hajiya Sarah amma ba dadewa zanyi ba"
"To mami Allah ya kiyaye hanya sai kin dawo"
Fita mami tayi tatafi ita kuma ta nufi dining area, zama tayi ta karya duk da abincin bawani mai yawa taciba, falo tadawo tazauna ta kamo tashar b4u tana kalla domin zaman shiru babu dadi,
Har bacci yadan fara daukarta sama sama taji sallamar khadija wacce abisa dukkan alamu yanzu ta mayar da zuwa gidan kullum tamkar ibada,
Tashi zaune hafsat tayi tana murmushi,
"Sannu da zuwa.."
"Yawwa hafsa, ko mamin bata nan" inji khadija wacce ke sanye cikin wata doguwar riga ta atamfa,
"Ehh mami ta dan fita wallahi" hafsa tabata amsa bayan tatashi zaune,
Zama khadija tayi, bayan sun gaisa suka dan fara hira kadan kadan,
"Hafsa kowa yayi mamakin yadda akayi kika samu kan yusleem har kuka kai wannan lokacin tare, saboda yusleem baya iya zama da mace.."
Murmushi hafsa tayi,
"Baya zama da mace kamar ya? Aini ban san wannan labarinba ko a mafarki"
"To kuwa a lissafi kece mace ta fiyeda goma da ya aura, kuma saida ya sakeni sannan ya aureki, ni kinga bamufi wata biyarba tare"
Jijjiga kai hafsa tayi alamun tausayawa,
"Allah sarki, Allah yarufa asiri kin san ai dama lamarin aure sai hakuri domin shima rai gareshi..."
"Hakane amma nida ina zargin ko aljanu gareshi ko kuma da saninsa tsabar cin mutunci ne, shiyasa ma ni yanzu wallahi auren yagama fitar min daga raina domin kin san naji dadi shine gari bawai nasaba ba.."
"To ai ba duk aka taru aka zama dayaba khadija, sai kiga nan gaba kin samu inda zakiji dadin hankalinki ya kwanta..."
"Kayya hafsa, kin san ai duk wanda miciji ya sareshi to idan yaga tsumma gudu yake, hafsa arayuwar aurena tafarko ban tsinci komai ba face bakin ciki da bacin rai da takaici, shiyasa ko zan kara wani auren gaskiya ba yanzu ba sai zuciyata ta nutsu tukunna"
"Ubangiji Allah yazabi abinda yafi alkhairi, babu komai ai jarrabawa ce daga Allah"
"Amin.."
Haka sukaci gaba da yin hirarsu har azahar tayi sai lokacin khadija tatafi, tun daga wannan rana kuma kullum zatazo susha hirarsu da hafsat wani lokacin ma harda mami, ita hafsa tausayin khadija takeji domin irin labaran da take bata na kuncin rayuwa da rashin samun farin ciki wanda ta rinka fuskanta agidan aurenta nafarko, shiyasa take tausayinta domin tasan irin wannan rayuwar tunda itama tashiga makamanciyarta abaya, koda yaushe yanzu khadija tana gidan haka kuma idan bataje da safe ba to zataje da rana ko da yamma wani lokacin harda daddare ma zuwa take tamaida gidan mami kamar gidansu haka ta dauki hafsat a matsayin yar uwa kuma abokiyar shawara domin ko sabon bazawari tayi saita fada mata,
Yauma kamar kullum hafsa tana zaune tana tsifar kai ita kuma mami tana gyaran farcenta saiga khadijan tashigo da alama daga sch take domin karfe 2 saura narana,
Da mami kawai suka gaisa tahaye dining ta zubo tuwon shinkafa miyar zogale tadawo wurin hafsat ta zauna,
"To inbanda abinku kuma ga tsifar gashi ga abinci?" Mami tafada tana murmushi,
Dan kwali hafsat ta dauka ta rufe kanta, "bari inbarshi anjima na karasa idan tagama"
Tashi mami tayi ta shiga kitchen domin tajiyo buruntun kuku aciki,
Mami natashi khadija ta dubi hafsa dama da labari tazo mata,
"Hafsa inata son inbaki labarin wani guy Al'amin, saurayi ne fa amma yadage sai ya aureni duk da nace masa nataba aure"
Murmushi hafsat tayi, "to kibashi dama mana kigani, wallahi khadija kiyarda indai kinga baida problem"
Murmushi khadija tayi ta yanko laumar tuwo tasa abakinta,
"Shikenan zan gwada ingani, bari inyi sauri ma domin munyi dashi zaizo da yamma"
"To Allah ya tabbatar da alkhairi"
Saida khadija taji tayi nak sannan ta hada nata yanata tatafi, kullum hakace take faruwa domin acewarta dama gidan mami gidansu ne domin dama aminiyar mahaifiyarta ce.
Tunda yusleem yatafi basuji duriyarsa ba saida yayi sati biyu sannan yakira su murna ranar awurin mami da hafsa ba acewa komai, sun jima suna hira dashi yana yimusu bayanin abubuwan dake faruwa sannan sukayi sallama,
Haka da daddare ma saida ya kuma kira suka kwashe awanni shida hafsat suna hira, yanzu har tasan lokacin kiranshi domin kullum sai yakirasu da safe da daddare,
Satinshi 7 acan yafara shirye shiryen dawowa amma idan yadawo bayan wani lokaci zai sake komawa,
Hafsat tunda taji zai dawo tarasa inda zata cusa kanta dan murna wanda hatta mami saida ta fahimta, saloon mami takaita aka wanke mata gashinta aka gyarashi, bayan sun dawo gida mai kunshin dake yiwa mami tazo ta zane mata kafafunta da hannaye da bakin lallai mai adon ja,
Tarba ta musamman mami da hafsat suka shiryawa yusleem,karfe 3:30 jirginsu yasauka nan mami da driver suka tafi daukoshi banda hafsa wacce tazauna domin karasa girke girken da aka dora sabodayau tace itace zatayi girkin da yusleem zaici.....
_Gaisuwa da fatan alkhairi ga takwarata A'isha D/sabo..._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*46*
***Lokacin dasu mami suka dawo gidan hafsat tana cikin daki tana shiryawa, saida ta kammala sannan tayi sallar la'asar domin lokaci yayi,
Tana tsaye gaban mirror tana gyara fuskarta bayan ta idar da sallar ta hango wulgawar mutum ta cikin mirror atsorace ta juya amma abun mamaki bataga kowa ba, tsorata tayi takama hanya zata fita daga dakin taje falo wurinsu mami,
Ji tayi anyi mata wata irin damka, tuni numfashinta yafara neman daukewa, ajikin mutum tajita anrugumeta tabaya tayadda bazata iya ganin fuskar mutumin ba, kara taso fasawa amma ina bata samu zarafin yin hakanba domin ji tayi anrufe mata baki da abinda bata san ko menene ba sai daga baya sannan ta fahimci cewar da bakinshi ne,
Wani sanyayyen kamshi ne mai dadi yake ratsa kofofin hancinta gaba daya,
Sassauta rikon da yayi mata yayi ya dago da fuskarta yana kallonta,
"Nanah hafsat..."
Firgigit tayi tabude idanuwanta akan fuskarsa ganinshi yasata daka tsalle ta rungumeshi na tsawon wasu mintuna,
Riketa yayi yana dan juyi da ita ahankali, dago da fuskarta tayi ta kalleshi, tabbas yaya yusleem dintane amma kuma tamkar wanda aka canjashi domin farar fatarshi tasake haskawa farin yakaru, gashi fatar tashi tasake laushi lubus kamar ta jarirai, kyakkyawar fuskarshi kuma tasake cika da kyau, annuri, da farin ciki,
Ji tayi gaba daya tagama raina kanta saboda yusleem yafita tako ina ita sai take ganinma ayanzu haka ai bata da wani abu atare da ita wanda take ganin zata iya jan ra'ayinshi domin yafita kyau yafita komai na rayuwa,
Hancinta taji yaja domin har lokacin tana dale ajikinshi hannayenta sakale awuyanshi,
Bude idanuwanta tayi daga dogon tunanin data lula ta kalleshi, ji tayi ya rike fuskarta yana kokarin sake saita bakinshi akan nata, shi kansa bakin nashi da lips din dake jiki da fararen hakoran dake jere aciki tasan abin kallone, lumshe idonta tayi tana jiran taji saukar lips dinshi akan nata amma sai taji sabanin haka maimakon yayi kissing din bakinta sai tajishi asaman kirjinta, saurin tureshi tayi tasoma kokarin kwacewa tana dariya,
Riketa yayi shidinma yana yin dariyar kasa kasa,
"Bakiyi min ko sannu da zuwa ba.."
Tana shirin yin magana suka jiyo maganar mami tana nufo kofar dakin,
"Hafsa har yanzu baki idar da sallar bane? Idan kin idar kifito ki hada salad din saboda nace kuku yahada yace kece kika ce karya taba sai kin fito..."
Bude baki tayi zata amsawa mami amma takasa saboda shakewar da muryarta tayi, rufe mata baki da hannunshi yayi yabawa mami amsa da,
"Mami har yanzu fa bata idar da sallar ba.."
"To idan ta idar kafada mata, sannan ku fito muci abincin..."
"To mami..."
Saida ta tabbatar da cewar mami tatafi sannan ta kalleshi,
"Kuma da tashigo taganmu fa gashi kace mata wai salla nake yi.."
Murmushi yayi ya lakuce mata hanci,
"Ai bazata ma shigo ba saboda tasan nidake yau tamkar tif da taya zamu kasance...."
"To kazo muje kar taga mun dade tayi zargin ko wani abu muke yi.."
Murmushi yayi ya dauketa nan tasoma mutsu mutsu, ajiyeta yayi ta fice shikuma yashiga toilet yayi alwala yafito yayi salla,
A falo ya samesu ita da mami sun baje girke girken da aka wuni anayi saboda shi, akusa da mami ya zauna yana kallon hafsa wacce ke tsugunne tana hada salad wanda zasu ci abincin dashi,sai lokacin wai ya lura da kunshin dake hannunta duk hidimar dazu idonshi bai kai kan kunshin ba,
Tashi mami tayi zuwa kan dining domin debo wasu kwanuka,
Hannunshi yakai kan na hafsa,
"Ya akayi dazu banga kunshin nan ba sai yanzu? Koda yake ai ni yau dinne gaba daya amaryar tawa tagama rudani, ta dauke hankalina"
Murmushi hafsat tayi saboda jin abinda yace, janye hannunta tayi daga jikin nashi saboda taga mami na kokarin fitowa ganin haka shikuma ya wayance da lakuto salad din yakai bakinsa,
Kamar koda yaushe a cikin babban faranti yauma suka zuba abincin suka hadu suna ci, idan yusleem yafaki idon mami sai ya kwace abincin hafsa ya kai bakinsa,
Tun daga yanayin cin abincinsa mami da hafsa suka gane cewar lafiya ta samu domin yau yaci abinci sosai wanda rabon da yaci irinshi har anmanta,
Komai da suka girka saida yaci, kallonshi kurum hafsa keyi saboda ganin yanda ya bude ciki ya narki abinci,
Kan kujera yaje ya mike, mami na zaune kusa dashi suna dan yar hira dangane da tafiyarsa da dawowar tashi yana sanar da ita abubuwan da suka wakana,