← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 30

Sashe 27

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Karbar dardumar hafsa tayi bayan khadija ta Kawo ta shimfida masa,yahau yatada salla,

Tashi yayi yakoma kan gadon bayan ya idar da salla, gaishe da mami yayi tai masa sannu sannan suka gaisa da khadija,

Tea Hafsa tatashi ta hada masa takai masa,

"Yaya yusleem wannan bata fuskar duk na menene? Ka saki ranka mana"

Hannunta yariko tareda cup din ruwan zafin yana dan murmushi,

"Ai kece kika sani yin fushin..?"

"Saboda me?" Tafada tana dan zame hannunta daga nashi,sake rike hannun yayi yaki saki,

"To ai gani nayi kunyi min rufdugu alhalin ke daya ma zaki iya rikeni..."

Murmushi tayi ta dan kalli wurin dasu mami ke zaune nan taga hankalinsu ma kwata kwata ba akansu yakeba domin hirarsu sukeyi itada khadija,

"Yaya yusleem kenan..."

Cup din da hannunta yahada yarinka kaiwa tea din bakinsa yana kurba har yakusa kammalawa, muryar mami ce ta katsesu,

"Hafsat ina zuwa bari mu fita tareda khadija tayi dropping dina saboda ayau zuwa gobe nake so agama komai na tafiyar yusleem ban son abun yadauki lokaci.."

"To shikenan mami sai kin dawo, Allah yasa adace"

Sallama sukayi da khadija suka fita tareda mami, kwanciya yusleem yayi ya tallafe kumatunsa da hannunsa guda daya yana kallonta,

"Kici abincin ki tayani wanka"

Sunkuyar da kanta tayi taci gaba da tsiyayo tea acikin cup,

"Uhmm, ko bakiji ba?"

"Naji yaya yusleem"

Ido ya tsura mata lokacin da tafara kurbar ruwan tea din, ganin ya kafeta da ido yasata tashi ta bar wurin ta matsa can nesa dashi, murmushi yayi ya lumshe idanuwansa.

Tunda mami tatafi bata samu dawowa ba har yamma abincima sai khadija ce takawo musu kuma yanzun ma kamar da safe bataga sakin fuska awurin yusleem ba amma hafsat ita kam ta karbeta hannu bibbiyu domin bataga aibunta ba,

Alla Alla hafsat tarinka yi mami tadawo domin ta kosa taji hanyar da mamin tabi tasamo makudan kudade haka masu wuyar samuwa.

Mami bata samu dawowa ba sai bayan sallar isha, lokacin Dr yazo ya rubuta musu sallama bayan mami ta bibbiya kudaden da yakamata su biya asibitin,

Driver ne ya daukesu suka nufi gida kuma dama jikin yusleem din yadanyi sauki ba kamar ranar da sukazo ba domin yanzu ko aman yadaina,

Afalo suka zauna dukkaninsu hafsat tagama matsuwa da son jin abinda mami zatace amma taji mamin tayi shiru sai lissafe lissafen kudi taketa faman yi,

"Yusleem nasamu munyi nasara komai ya kammala insha Allah nanda kwana biyu zaka tafi kasar Cairo domin ance visa din kasar tafi saurin samuwa fiyeda ta kasar India.."

"To mami Allah yasaka da alkhairi Allah yakaimu lokacin"

"Amin, Allah yasa asamo abinda akaje nema Allah yabaka lafiya"

"Amin mami, bari inyi wanka" yace da mami bayan ya mike yana yiwa hafsat kallon zo ki rakani, taganshi sarai amma saita dauke kanta tayi kamar bata ganiba dolenshi yajuya ya fice shi kadai,

Bayan fitarshi hafsat ta kalli mami,

"Mami kodai gwala gwalanki kika siyar?"

Dakatawa mami tayi daga yin abinda take ta kalli hafsat,

"Hafsa ai ni yanzu banida gwalagwalai, jiya darana bakiga nakoma asibiti raina abace hankalina atashe ba?

Wallahi infada miki dawowa nayi na iske safe dina wurin da nake ajiyar gold din abude an kwashe babu komai aciki, koda nakira mai gadi na tambayeshi sai yace min wai bakuwa nayi kuma yace mata babu kowa agidan amma tace ehh zata shigo ta jirani, ban san wacece ba amma duk yadda akayi itace ta sace min wadannan gold din kuma dama iya saiti daya gareni sauran duk nasayar bana gasken bane.."

Zaro ido hafsat tayi saboda jin satar da akazo har gida aka yiwa mami,

"Mami Allah ya kiyaye gaba, Allah yamayar miki da alkhairi, yanzu kuma ya akayi?"

"Shine naje nasamu shi shugaban asibitin wannan yaron sufyan nace masa zan sayar da kodata (kidney)guda daya sannan suma su khalifa shida Abdul idan sun dawo za aciri tasu guda dai dai tunda dama guda dayace ke amfani ajikin dan adam.."

Zabura hafsat tayi ta zazzaro ido, cikin rawar baki tace,

"Haba mami, ya za ayi kisayar da kododinku? Ai bai kamata dan za agyara wani kuma abata wani ba.." Takarashe maganar hawaye nabin kuncinta,

"Ai magana takare hafsat tunda shima sufyan din yabani shawara ta hanyar cewar idan inada wata kadara kamar gida ko fili gara insiyar akan insaida kodata data yarana, to kinga yanzu bamuda wasu kadarori inbanda wannan gidan kwaya daya shine yace to mahaifinsa zai sai gidan kuma insha Allah zaiyi mana taimako ta hanyar bamu aron gidan muci gaba da zama har zuwa ranar da zamu mallaki namu,adaren jiya mukazo muka ga gidan bayan ya debo dillalai kuma sunyiwa gida kudi, ansiya miliyan daya.." Mami takammala maganar tana dan murmushin yake domin zuciyarta wani zafi takeyi mata.

Hafsat ji tayi tasamu yar nutsuwa saboda jin bayanin mami,

"Allah ya rufa asiri mami, Allah yasa adace kuma"

"Amin hafsat, kinga yanda rayuwa ta juya mana ko? Mun kawoki kinata faman shan wahala"

"Dan Allah mami kidaina fadin haka, ai yanda Allah ya tsara min kenan.."

"Allah yayi miki albarka, insha Allah gobe zamu yi signing atakardar gidan daga nan sai inbasu copy.."

Shiru hafsat tayi tana jin tausayin mami yana kwaranya acikin ranta domin tasan karfin hali kawai mamin keyi amma ita kadai tasan yanayin da take ciki,

Ganin mami ta tashi tashiga cikin bedroom dinta yasa itama hafsat tatashi tashiga dakin surayya,

Kayan jikinta ta cire tashiga wanka, lokacin da tafito ta hangi yusleem kwance saman gado yayi d'ai d'ai, hijabinta ta janyo ta saka tana kallonshi, shi dinma juyawa yayi yana kallonta daga kasa har sama......

_Fatan alkhairi ga aminiyata maryam Qaumi, Amira zango,zeebells tareda Xarah b~b_

*_Ummi A'isha_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*44*

***D'auke kanta tayi daga kallon yusleem taje gaban mirror tafara shiryawa, shikuwa sai faman binta da idanuwa yake domin duk wani motsi da zatayi akan idonshi ne,

Tashi tayi da niyyar ta dauki kaya tasa amma ganin ya kafeta da ido yasata shiga bathroom tasa kayan sannan tafito,

"Yaya yusleem dan Allah katashi katafi,ni wallahi bacci nakeji, kaga dai 2 days banyi bacci ba..." Tafada cikin shagwaba bayan ta zauna agefen gadon, hannunta ya kamo yarike cikin nashi,

"To ai yanzu ba hanaki baccin nayi ba, zo ki kwanta"

"Ni gaskiya katafi, bana son mami ta..."

Saurin katseta yayi ta hanyar jawota jikinshi,

"Karyar kunya kikeyi nanah, saboda Kinga mami fa tajima da sanin cewar tare muke kwana tunda ko lokacin da tararmu agidan haya muna zaune adaki daya ta tarar damu ba dakuna biyu ba.."

Jin ya ambaci gidan haya yasa taji Maman amir ta fado ranta,

"Kaga kuwa dazu da rana Maman amir ta kirani tana gaisheka tace inyi maka sannu..."

"Ina amsawa kawar Maman amir..."

Murmushi tayi tafara kokarin zamewa daga jikinsa amma ya riketa gam,

"Ba kince bacci zakiyi ba, to kiyi mana"

Shiru tayi domin dama bawai baccin takeji ba ita dai kawai tana kunyar mami tasan anan yake kwana,

"Ya kukayi da mami? Ta fada miki a inda tasamo kudaden nan kuwa? Saboda wallahi sam hankalina yaki kwanciya" yayi maganar cikin raunin zuciya yana shafa kanta,

"Ehh ta fada min yaya yusleem, wannan gidan ta saida kasan lafiyarka tafi komai muhimmanci agaremu yanzu..."

"Hakane to amma..."

Katseshi hafsat tayi ta hanyar kai hannu ta rufe masa baki, shiru yayi yana jin yanda take shafar kasumbarshi dake baibaye a fuskarshi,

"Ai yaya yusleem babu abinda yakai uwa dadi, kowacce uwa tana son danta acikin kowanne irin yanayi koda kuwa duk duniya zata ki shi to ita zataso kayanta, kasan meyasa nafadi haka?"

Girgiza kai yayi alamun a'a,

"To da mami kidney dinta tayi niyyar sayarwa da tasu Abdul..."

Gani tayi idanuwanshi sun firfito waje ya yunkura yana kokarin tashi, mayar dashi tayi ya kwanta takoma jikinshi ta dora kanta akirjinsa,

"Ka kwantar da hankalinka ai bata sayar ba, gidan nan ta siyar shine aka samu kudaden da zaka tafi Cairo..."

Ajiyar zuciya yayi yakai hannu ya rungumeta,

"Dole hankalina yatashi hafsat, idan mami da yan uwana suka sayar da kidney dinsu menene ribar? Babu riba at all saboda nan gaba za azo ana facing problems a lot,tunda kinga akwai kidney disease ko wani abu mai kamada haka"

"Hakane amma tunda Allah ya takaita abin ai shikenan karka daga hankalinka, Allah yabaka lafiya, ni yanzu babban burina shine inga kasamu cikakkiyar lafiya kamar kowa"

Murmushi yayi ya kamo hannuwanta,

"Kin kosa insamu lafiya ayi wacce za ayi ko?"

Dariya tayi ta boye fuskarta akirjinsa,

"Kai yaya yusleem ni wallahi ba abinda nake nufi ba kenan"

"To me kike nufi?"

"Ni kawai inganka lafiya kadaina wannan zazzabin da amai da ciwon ciki shine kadai burina"

Kanta yafara shafawa yana murmushi,

"Nikuwa kin ga babban burina shine idan nasamu lafiya inbawa matata dukkan hakkoki wanda addini ya rataya min awuyana, sannan inmaidata mace sosai..."

Boye fuskarta tayi tana dariya,

"Kai yaya yusleem.."

"Kai nanah hafsat, da kin zaci zamu zauna ahaka ne? Uhm"

Shiru tayi masa tana dariya har lokacin bata bari yaga fuskarta ba,

"Uhmm?" Yasake tambayarta, shirun tasake yimasa, hannunta yakama yakai bakinsa yayi kissing dinshi, ji tayi ya rungumeta tsam tsam,

Kunyace ta lullubeta domin abin na yusleem yau yagirmama duk da dai dama yasaba rike hannunta ko ya dafa kafadarta ko yaja mata yan yatsun kafarta ko kuma yadafa kafadarta amma bai taba yunkurin kissing dinta ba sai yau,

Wasu wasanni masu nauyi yau yake yimata wanda bai taba yimata ba, sun jima cikin wannan yanayin kafin ya rungumeta yana fitar da numfashi ahankali, kwanciya tayi luf ajikinsa da haka har bacci ya dauketa domin dare yayi sosai.

Tunda tafara baccin ba ita ta tashi ba sai karfe 7,ita kanta tayi mamakin makarar da tayi, dudduba gefenta tayi nan taga babu yusleem babu alamunsa,

Wanka tashiga tayi agurguje tafito tayi salla taci gaba da zama shiru, tana zaune akan abin sallar taji shigowar mami,

"Hafsat yau makara kikayi ne? Naji shiru baki fitoba"

Tashi Hafsa tayi tana ninke dardumar da tayi salla,

"Ehh wallahi mami, ina kwana?"

"Lafiya lau, idan kin shirya kifito ga breakfast nan yana jiranki"

"To mami bari inzo.."
Chapter 27 · 0% Book details