← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 30

Sashe 12

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

***Aranar da aka daura auren aranar alhaji sa'id yace aje akai Hafsat gidanta duk da hajiya kubra bata so hakaba domin ita taso ace sai washe gari za akaita amma tunda ga abinda alhaji sa'id yace dole babu yadda ta iya dan haka aka fara shirin kai amarya dakinta,

K'arfe 9 daidai aka fito da Hafsat din daga sashen alhaji sa'id bayan ya kammala yimata nasihar da ta dace duk wani uba yayiwa'yarsa a lokacin da za akaita gidan miji, haka itama hajiya kubra ba abarta abaya ba wurin yiwa Hafsat fada akan tabi mijinta kuma ta kyautata masa,

Inbanda kuka babu abinda Hafsat keyi domin tasan su hajiya kubra sunyi mutukar kokari akanta kuma sun taka muhimmiyar rawa acikin rayuwarta wanda har abada bazata manceba kuma bata da abinda zata iya biyansu da shi,

Wata tsadaddiyar mota ta alfarma kirar Lexus new series 2017 aka bude mata tashiga, nan kannen hajiya kubra suka sakata atsakiya yayinda surayya kanwar yusleem tashiga gaban motar,

Direct gidan mami aka wuce da ita inda mamin nacan ita da jama'arta suna zaman jiran zuwansu,

Yanayin farin cikin da mami ke ciki abin bazai misaltu ba domin kana ganinta zaka gane irin dunbin farin cikin da take ciki,

Har tsakiyar bedroom dinta aka shigar da Hafsat wacce ke tukunkune cikin wani babban mayafi dark blue kalar leshin dake jikinta,

Rungumeta mami tayi tana fara'a,

"Barka da zuwa cikin zuri'ata 'yata,ubangiji Allah ya baku zaman lafiya ya kauda fitina da duk wani sharri daga gareku, Allah yabaku zuri'a dayyibah, nidama tun can a matsayin 'ya na daukeki kuma yanzun ma kina nan ahaka baki sauya ba, insha Allah zamu rikeki amana"

Jin abinda mami tafada yasa kawayenta dake baibaye da ita sakin guda,basufi minti talatin agidan mami ba aka wuce da Hafsat gidanta wanda ke can wata unguwa da ake kira da babbar inuwa domin gaba daya mazauna unguwar shaharrun mutane ne wadanda sukeda hannu da shuni,

Shi kanshi yusleem fadin girman gidansa da tsarinsa abune mai wahala domin gidan yatsaru iya tsaruwa,

Cikin babban bedroom dinta aka shigar da ita ta zauna akan gefen makeken gadonta samfurin Italy,

Saida yan Kawo amarya suka fita sannan Amina kawarta da surayya suka shiga cikin dakin,

"Amarya kinsha kamshi, nidai bari inje intafi.." Inji Amina,

Dago jajayen idanuwanta Hafsat tayi ta kalleta,

"Haba Amina bazaki bari angwayen suzo ba?"

Dariya surayya tayi tareda bararrajewa akan gadon,

"Waye zai Kawo miki angwaye? Indai yaya yusleem ne Allah shi kadai zai zo gidan nan garama kibarmu muje mu tafi, nidai dama kin san gobe da sassafe zanyi miki asubanci..."

Jin abinda surayya tace yasa Amina tashi tsaye,

"To shikenan bari intafi, Hafsat sai nadawo ganin gida lokacin kin dawo cikin nutauwarki domin nasan yanzu bakya tareda ita..."

"To Amina nagode, Allah yabar zumunci, nagode"

Tashi surayya tayi tabi bayan Amina suka fita tare,

Tsuru Hafsat tayi tana bin dakin da kallo wanda yasha furniture's na alfarma kalarsu dark purple, duk tsoro yabi ya cikata saboda babu motsin komai agidan, ta wuri daya hankalinta ya kwanta shine tasan akwai masu gadi acikin gidan wanda yanzu haka suna can gate suna aikinsu,nan tazauna taci gaba da zuba idon ta Inda zataga shigowar angonta.

K'arfe 10:30 yusleem yashiga gidan mami kasancewar yan biki suna nan basu tattafi ba yasa gidan inbanda hayaniya babu abinda kakeji kamar dare baiyi ba,

Fitowa mami tayi wurinshi ta tsaya tana kallonsa, gaba daya ta fahimci bashida wata walwala,

"Yusleem..." Ta kira sunanshi tana kallonsa,

"Na'am.."

"Kasan abinda nakeso dakai? Na hadaka da girman Allah yusleem ka rike Hafsat amana, dan Allah karka cutar da ita, sannan ka taimaka ka rufa min asiri karka sakar musu 'ya, yusleem idan ka aikata daya daga cikin wadannan wallahi bazan yafe makaba sannan ka nemi wata uwar amma baniba, Allah yayi maka albarka ya baka zuri'a tagari"

Hannayenshi duka suna cikin wandon farar shaddar dake jikinsa yana tsaye yana jin mami har ta kammala,

Gyada kai yayi batare da yace komai ba ya sunkuyar da kai,

"To kaje katafi mana"

"Ehh yanzu zan tafi, inasu Abdul suke? Ko shi ko khalifa wani yazo muje yayi dropping dina saboda dama shu'aibu yaron office dinane yakawo ni kuma yawuce"

"To bari nakira maka daya daga cikinsu, ina zuwa"

Juyawa mami tayi ta nufi sashen samarin,da khalifa tafara yin arba dan haka shi takirawo ta nuna masa yusleem a inda yake tsaye ya cire hularshi yana lanlankwasa ta,

Batare data koma wurinshi ba tawuce zuwa ciki shikuma khalifa ya nufi wurinsa daga nan wurin da aka tanada domin adana motoci sukaje khalifa yadauko guda daya yusleem yabude yashiga suka fita daga cikin gidan,

"Yaya ka siyi yan abubuwanne?"

Kallon khalifa yusleem yayi,

"Mefa?"

"Wai da yaya ina nufin dan nama haka da sauransu.."

"Kaima yanzu bakada kunya kamar Abdul ko?" Yafada yana kallon titi,

"A'a yaya bahaka bane,nayi tunanin ko kamanta ne shine natuna maka"

Bai sake cemasa uffan ba har sukaje gidan nan yabude kofa yafita ya nufi ciki yana takawa ahankali.....

*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*

_Dedicated to MISS XOXO_

*23*

***Ahankali yaci gaba da takawa yana tafiya tamkar wani marar lafiya ko kuma wanda yake jin tausayin kasar,

Hularshi yatura baya zuwa keyarshi ya zuba hannuwanshi acikin aljihun wandonshi domin wani dan dari dari yakeji,

Babban falon dake girke atsakiyar part din guda biyu yabude yashiga, hanyar da zata sadashi da bedrooms din Hafsat yabi har ya isa ga dakin da take ciki,tana kishingide ta dan fara gyangyadi amma ba bacci takeyi ba,

Ahankali yatura kofar dakin yashiga, daga bakin kofa ya tsaya bayan yasake zuba hannuwanshi acikin aljihun wandonshi,

Dan gyaran murya yayi kadan wanda hakan yayi sanadiyyar bude idon Hafsa ta tashi zaune da hanzari,

"Zo...." Shine kawai abinda yace da ita cikin sanyayyiyar muryarshi yajuya yafara tafiya, tashi tayi tasauka daga kan gadon tabi bayanshi,

Saboda irin yadda yake daga kafa dakyar yana tafiya ahankali yasa harta cimmashi awani dan madaidaicin corridor, cikin falonta suka shiga,

Kan dining ya nuna mata,

"Ga abinci can idan kina jin yunwa.."

Daga haka bai sake cewa komai ba yajuya yafita ya nufi part dinshi,

Cikeda mamaki Hafsat take binshi da kallo, lallai wannan yusleem din ba kanwar lasa bane yanzu dama akan kawai zai nuna mata abinci ne yasa yatasota?

Kan dining table din takarasa, bakaken ledodi ne cikeda fruits daya ledar kuma kaji ne gasassu guda uku sai juice da fresh milk,

Dan yunwa kam tabbas tana jinta domin rabonta da cin abinci tun lokacin da aka fara hidimar bikin nan bata iya zama taci abinci ta koshi ba,

Zama tayi ta bude ledar tafara yagar kazar tana ci saida taji ta koshi sannan ta mayar ta rufe ta tashi,

Bedroom dinta takoma tashiga bathroom ta wanke hannunta da bakinta tadawo ta kwanta, Sam bata kara jin duriyar yusleem ba har asuba tayi gari ya waye,

Wanka tayi ta shirya tayi kwalliya tasaka wani jan Swiss material,

Fita tayi zuwa falo tana bin ko ina da kallo domin dukiyar da aka zuba afalon da shi kansa tsarin falon ba kadan bane,

Haka taci gaba da zama shiru har surayya tazo, shigowa tayi tana dauketa kulolin abinci,

"Amarya bakya laifi.." Surayya tafada cikeda tsokana,

"Ni dan Allah zubo min abincin nan inci yunwa nakeji"

"Ai dole kiji yunwa amaryar mu, yanzu kuwa zan Kawo miki.."

Kitchen ta shiga ta dauko filet tazubo mata wainar shinkafa da miyar agushi wacce taji kaji domin inbanda kamshi babu abinda takeyi,

"Ga abinci, ina yayan? Ko bai tashiba?"

Shiru Hafsat tayi saboda ita bata sanma me zatace ba domin rabonta da ganinshi tun jiya da daddare,

"Duk yunwar ce ne ta hanaki magana?"

Murmushi Hafsat tayi ta gutsuri wainar tafara aikawa cikinta, kan dining table surayya takoma taje ta kinkimo ledar kajin da yusleem yakawowa Hafsat jiya,

"Ai wannan baku ci bama, kun tsaya jin kunyar juna ko? To ni bari inci"

Hafsat najinta bata tankaba domin ita yusleem yayi bala'in daure mata kai saboda ko atarihi bata taba jin angon da yayiwa amaryarshi hakaba, ace kazar ma bata da darajar da zai dauka yakai mata har sai ya kirata tazo ta dauka da kanta,

Abincinta taci ta koshi ita kuma surayya tana faman yagar kazar da ta rage jiya, bayan sun gama ne surayya tajata,

"Zo muje kiga sauran bedrooms din"

Fita sukayi daga falonta suka shiga corridor din da zai sadaka da dakunan baccinta wadanda suke guda biyu ajere sai can gaba dasu daga karshe wata kofa ce itama daban, bayan sun gama dudduba dakunan ne suka shiga wannan kofar, wani lafiyayyen falo Hafsat tagani mai mutukar kyau wanda yasha kaya masu tsada sannan akwai wata babbar kofa wacce tafita tawaje har zuwa kan wata katuwar balcony,

Coffee & milk colour ne gaba dayanshi sai wani kamshi yake na musamman,

Zama surayya tayi acikin daya daga cikin kujerun falon,

"Wash kafata, kinga bedroom din can leka kigani saboda wallahi nikam nagaji.."

Batare da tunanin komai ba Hafsat ta nufi bedroom din ta murda kofar ta shiga, dakine babba wanda girmansa zaiyi girman falo, wani babban royal bed ne agirke aciki sai kamfacecen mudubi da sauran kayayyaki, kamar ance ta kalli gefenta tana kallon wurin taga wata babbar kujera mai kamada dan karamin gado, yusleem ne kwance akai ya rungume pillow akirjinsa idanuwansa arufe abisa dukkan alamu bacci yake yi,

Tafi minti biyu tana kallonshi kafin tajuya zata fita harta bude kofar taji maganarshi cikin muryarshi mai mutukar sanyi da zaki,

"Zo nan..."

Cikin tsoro ta waiwaya ta kalleshi, bude idanuwanshi yayi yana kallon sama bai kalleta ba,

Mayar da kofar tayi ta rufe takarasa inda yake,

"Gani.."

"Menene ya kawoki?"

"Babu komai.."

Shiru taji yayi baiyi magana ba sannan har lokacin bai daga ido ya kalleta ba maimakon hakama sai yajuyar da kanshi da yayi yana kallon wani wuri,

"Ina kwana..?" Tace dashi saboda tunawar da tayi bata gaidashi ba,

"Lafiya.." Taji ya amsa,

Tana nan tsaye shiru bai sake yimata magana ba dan haka tajuya tafita,

Gani tayi surayya bata inda tatafi tabarta, wucewa tayi takoma part dinta acan ta iske surayya ta kunna makekiyar tv din dake manne abangon falon ta kamo tashar zee world,
Chapter 12 · 0% Book details