Sashe 25
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyawa tayi tasake komawa cikin dakin, tashinsa tasoma yi tana dan bubbuga gefen pillow din da kanshi ke kai,
"Yaya yusleem...,yaya yusleem katashi"
Ido guda daya ya bude ya kalleta,
"Me zan yi miki?"
"Safiya fa tajima dayi dan Allah katashi"
Mayar da idonshi yayi ya rufe yajuya mata baya yasake jan bargo ya lulluba, tashi tayi tafita, kuku ta hango yana jera musu breakfast akan dining,
Zama tayi acikin falon tama rasa me zatayi, ajiyar zuciya tayi aranta tana fadin dama matsalar gidan masu kudi kenan ko katashi da wuri karasa abinda zakayi,
Tana nan zaune tana kallon shirin gari yawaye a tashar arewa 24 har mami tafito, kamar kullum mamin tasha kwalliya kamar me shirin zuwa gidan biki,
Sauka kasa tayi tagaida mami, cikin fara'a da sakin fuska mami ta amsa domin tana jin son Hafsat tamkar na yar da ta haifa,
Kan dining suka dunguma suka fara karyawa,suna daf da gamawa mami ta kalleta tace,
"Shi wannan sarkin baccin bai tashi bane? Ai da yatashi saboda maganar zuwa asibitin ko"
"Ehh gaskiya kam, bari nagama sai inje in tasoshi.."
Kafin Hafsat ta rufe baki sai gashi ya bude kofa yafito yana yamutsa fuska, sunkuyar da kai Hafsat tayi kamar ruwa ya cinyeta, mami kuwa dubanshi tayi ta kawar da kai,
"Ka manta da maganar zuwa asibitinne kaki tashi da wuri?"
"Wallahi ina sane mami, ban manta ba" yakarasa maganar yana kallon Hafsat ta gefen ido wadda yasan ba haka tasoba,
"To ai sai kaje kashirya.."
Wucewa yayi yafita zuwa part din su khalifa, wanka yayi yafito ya zauna domin shafa mai, yana zama Hafsat tashigo hannunta rikeda jug dan madaidaici,
"Ga kunun..."
"Babu gaisuwa?"
Yafada lokacin da yake shafa man a hannayenshi,
"Ina kwana?"
"Ni bazan amsa ba, zo nan.."
Dan sake matsawa tayi tana kallonsa,
"Gani.."
"Kinsa Mamie tana yimin fada ko, bayan kuma kece kikayi sanadiyyar makarata saboda dumin jikinki da naji"
Juyawa tayi zata fita daga dakin fuskarta dauke da murmushi,
"Zo nan, Allah karki fita"
Dawowa tayi ta tsaya, tana nan tsaye har yagama shiryawa ya dauki kayanshi yasa,
Kunun da ta Kawo mishi yasha sannan suka fita domin Tafiya asibiti,
Afalo suka iske mami cikin shiri nan suka dunguma domin tafiya amma kuma suna fitowa compound din gidan sai ga motar khadija ta kunno kai kuma tareda mahaifiyarta suke wannan dalilinne yasa mami fasa zuwa asibitin tace da yusleem da Hafsat kawai suje driver yakaisu ita kuma takoma ciki itada hajiya fa'iza da khadija,
Ganin irin gaisuwar da yusleem sukayi shida khadija yasa Hafsat yimasa magana domin daurewa khadija fuska taga yakeyi bayan kuma ita bataga laifinta ba, ganin baya son maganar yasata yin shiru ta kyaleshi.
Lokacin da sukaje asibitin Hafsat kin shiga office din dr sufyan tayi tai zamanta awaje sai yusleem ne yashiga shi kadai, ya dan jima aciki kafin yafito,
"Yaya yusleem ya kukayi?"
"Yace nanda 4 days nakara dawowa lokacin result din taste din da yayi min yafito.."
"To Allah dai ya jiyar damu alkhairi"
"Amin, muje mu tafi gida tunda babu abinda yayi saura, Dr din yana tambayarki wai yau banzo da matata ba nace tare ai muke kina waje wai ai dama yasan bazaki barni nazo ni daya ba..."
Dan murmushin yake tayi batace komai ba amma acikin ranta fadi take "Dan iskan Dr",
Lokacin da suka koma gida sai mami ita kadai domin su khadija sun tafi, ganin sun dawo da wuri mami tace Hafsat ta shirya taje driver yakaita gidansu tagaisa da iyayenta,
Garin dakakkiyar busasshiyar kubewa da kuka da daddawa wanda Maman khadija ta Kawo wa mami su mamin tabawa Hafsat tace takaiwa umminta tsaraba,
Yusleem yana kwance akan kujera mami na kujerar kusa dashi Hafsat din tafito zata tafi,
"Mami idan nadawo zan biya ta gidan amina kawata, haihuwa tayi shine zanje inga babyn.."
"To sai kin dawo, Allah ya raya.. Ki gaida hajiya kubran"
"To mami zataji"
Fita tayi nan yusleem yatashi yabita, tana daf da fita daga cikin kitchen yayi saurin rikota,
"Mami zaki tambaya unguwa saboda itace take aurenki ko? To gidanku kadai na amince kije daga nan karkije ko ina"
Juyawa yayi zai koma falo tayi saurin rikoshi,
"Dan Allah kayi hakuri yaya yusleem.. Kaji"
Shiru yayi mata ita kuma taci gaba da yimasa magiya, dakyar ya amince yace taje.
Acikin kitchen ta iske Ummi lokacin dataje gidan, ba karamin dadin ganinta hajiya kubra tajiba nan suka baje suka fara hira irinta uwa da 'ya da haka har Alhaji sa'id yazo ya samesu yadawo daga buga bugarsa domin shima ya haduda jarrabawa irinta rayuwa sai dai ita Hafsat bata saniba har saida ummi tayi mata bayanin abubuwan da suka faru na iftila'in da ya afkawa alhaji sa'id din bayan ya sayar da kadarorinsa ya tura asiyo masa kayayyaki amma har yau kayan basu fitoba gashi saboda rashin kudi kwangilar ma ba samuwa takeyi ba dan dai kawai yanada amini ne mai fada aji,
Kuka Hafsat tayi ba kadanba dalilin jin wannan labarin da hajiya kubra ta bata amma kuma tasan jarrabawa ce daga Allah shiyasa ma bata daga hankalinta ba,
Dayake sun dade basu hadu da umminba yasa Hafsat takasa tafiya da wuri har saida aka kira sallar magrib, bayan tayi sallane tatafi lokacin driver yazo daukarta, ko gidan aminan ma bataje ba gida ta wuce direct,
Mami kadai ta tarar afalo tana waya da surayya nan ta zauna har mami ta kammala wayar itama tabata suka gaisa domin rabonsu da juna tun lokacin da surayyan takoma school,
"Hafsa kin dawo? Ya kika baro mutanen gidan?" Mami ta tambaya tana kokarin ajiye wayarta,
"Lafiya lau mami, suna nan lafiya, Ummi tana gaidaki tace ayi miki godiya..."
"Babu komai wallahi, kayan ma nawa suke.."
Zama sukayi dan shiru suna kallon tv zuwa can Hafsat ta mike ta nufi bedroom, tana shiga ta iske yusleem akwance,
"Lafiya kuwa yaya yusleem?" Ta tambaya,
"Wallahi zazzabi ke damuna hafsa"
Ahanzarce takarasa kusa dashi jin jikinsa zafi zauuu tayi gashi yana dafe da cikinsa wanda ke ta faman murda masa,sannu ta shiga yimasa yana amsawa dakyar, zuwa can taji ya kamo hannunta ya dora akan cikin nasa,
Jikinta rawa yafara saboda ganin yanda yusleem yake yin murkususu gashi bata son taje tafadawa mami hankalinta yatashi,
Ruwan sanyi ta dauko tasoma shafa masa acikin nashi nan yaji ciwon yafara lafa masa ahaka har bacci ya daukeshi, ganin yasamu bacci yasa ta fita wurin mami wadda take zaune akan abin salla ta idar da sallar isha tana jan carbi,
"Hafsa ga tuwo can, wallahi yau shi naji ina sha'awa shine nace kuku yayi.."
Murmushin yake Hafsat tayi ta girgiza kai,
"Kafin nataho ma agidan Ummi saida naci abinci,wallahi na koshi.."
Wuri tasamu ta zauna amma lokaci zuwa lokaci tana dan shiga bedroom din taduba yusleem sai dai har 10 tayi bai tashiba, har sukayi sallama da mami tashiga dakinta itama ta shiga daki yusleem bacci yake,
Akusa dashi ta kwanta tana kallonshi yana rike da cikinshi, sai wurin 11 sannan yatashi yayi sallar magrib da isha wadanda ke kanshi domin bai samu damar yiba,
Kalau yayi sallar ya idar tana zaune tana kallonshi yana idarwa kuma yace sai ta dama masa kunu yasha yunwa yakeji, tare suka fita zuwa kitchen din ta tafasa ruwa ta dama masa kunun suka koma daki, saida yagama sha sannan suka kwanta, tana ji yafara tsokanarta kamar bashi bane dazu yake murkususu kamar zai mutuba,
Bata San lokacin da yagama tsokanar tataba domin bacci tayi tabarshi, can tsakiyar dare kuma kamar acikin mafarki take jin kakarin amai nan tatashi taganshi kwance yana juyi yana rikeda cikinsa, ruwan sanyi ta debo tafara shafa masa amma yanzu ji yake kamar ruwan zafi tafasasshe take Shafa masa, kunun da yasha kuwa saida yayi amansa gaba daya,rikeshi tayi nan ya kuwa kankameta kamar zai koma cikin cikinta daga shi har ita babu wanda yasake runtsawa har asuba tayi ita dai agaba tasashi tana hawaye,
Ganin abin yayi yawa gashi yana yin wani irin amai kore kore yellow yellow yasa hafsa zuwa ta sanarwa da mami lokacin karfe 5:30,
Driver mami tayiwa waya kasancewar a B/Q yake zaune, nan da nan yafito suka kama yusleem suka nufi asibitin Dr sufyan dashi,
Kallo daya zaka yiwa mami da Hafsat kagane acikin tashin hankali suke domin kowannensu fuskarshi kunshe take da tashin hankalin,
Emergency aka kai yusleem bayan kamar mintuna 30 Dr mufid yafito dauke da file din yusleem domin lokacin Dr sufyan bai fitoba,binsa mami da Hafsat sukayi abaya domin jin abinda zaice,
"Hajiya in my opinion ni ina ganin cewar is better for u idan kuka fitar da patient dinku kasar Cairo ko kuma India saboda sincerely speaking yana cikin bad condition domin cutar dake tattare dashi itace take cousing din wannan ciwon cikin da yake fama dashi, and kuma akwai wani aiki da zasuyi masa wanda mu bazamu iyaba, so idan zai yuyu in the next 3 days ku samar masa visa sai ku fita dashi domin magana tagaskiya bama karbar patients wadanda lalurarsu tazama chronic kuma worst saboda kinga nan is private hospital dole sai mun zama muna him takatsantsan..."
Yana ida wannan bayanin yagyara farin glass dinshi yayi gaba, sororo mami da Hafsat sukayi kowannensu yana tunanin hanyar da za abi har akai ga fitar da yusleem kasar waje....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
_Fatan alkhairi ga yan kungiyar haske writers association, shafin yau nakune ku kadai domin jin dadinku..._
*42*
***Daga mami har Hafsat ji sukayi kamar ruwa ya cinyesu dalilin jin bayanin da dr yayi musu nan hankalin kowanne acikinsu yakai kololuwar tashi,
Mami ce tafara magana fuskarta cikeda murmushin yake,
"Hafsat babu komai kinji, karki daga hankalinki insha Allah zamu samu yanda zamuyi..."
Wasu hawaye ne suka zubowa Hafsat tasa gefen hijabinta ta share batare da tayi magana ba,
Kama hannunta taji mami tayi suka bar wurin suka koma reception,
"Yanzu Hafsat ina zuwa bari naje gida nadawo kinji..."
"To mami sai kin dawo, Allah kiyaye hanya.."
Tashi mami tayi tafita, yayinda ita kuma Hafsat taci gaba da zama awurin zuciyarta kunshe fal da tarin tunani.
"Yaya yusleem...,yaya yusleem katashi"
Ido guda daya ya bude ya kalleta,
"Me zan yi miki?"
"Safiya fa tajima dayi dan Allah katashi"
Mayar da idonshi yayi ya rufe yajuya mata baya yasake jan bargo ya lulluba, tashi tayi tafita, kuku ta hango yana jera musu breakfast akan dining,
Zama tayi acikin falon tama rasa me zatayi, ajiyar zuciya tayi aranta tana fadin dama matsalar gidan masu kudi kenan ko katashi da wuri karasa abinda zakayi,
Tana nan zaune tana kallon shirin gari yawaye a tashar arewa 24 har mami tafito, kamar kullum mamin tasha kwalliya kamar me shirin zuwa gidan biki,
Sauka kasa tayi tagaida mami, cikin fara'a da sakin fuska mami ta amsa domin tana jin son Hafsat tamkar na yar da ta haifa,
Kan dining suka dunguma suka fara karyawa,suna daf da gamawa mami ta kalleta tace,
"Shi wannan sarkin baccin bai tashi bane? Ai da yatashi saboda maganar zuwa asibitin ko"
"Ehh gaskiya kam, bari nagama sai inje in tasoshi.."
Kafin Hafsat ta rufe baki sai gashi ya bude kofa yafito yana yamutsa fuska, sunkuyar da kai Hafsat tayi kamar ruwa ya cinyeta, mami kuwa dubanshi tayi ta kawar da kai,
"Ka manta da maganar zuwa asibitinne kaki tashi da wuri?"
"Wallahi ina sane mami, ban manta ba" yakarasa maganar yana kallon Hafsat ta gefen ido wadda yasan ba haka tasoba,
"To ai sai kaje kashirya.."
Wucewa yayi yafita zuwa part din su khalifa, wanka yayi yafito ya zauna domin shafa mai, yana zama Hafsat tashigo hannunta rikeda jug dan madaidaici,
"Ga kunun..."
"Babu gaisuwa?"
Yafada lokacin da yake shafa man a hannayenshi,
"Ina kwana?"
"Ni bazan amsa ba, zo nan.."
Dan sake matsawa tayi tana kallonsa,
"Gani.."
"Kinsa Mamie tana yimin fada ko, bayan kuma kece kikayi sanadiyyar makarata saboda dumin jikinki da naji"
Juyawa tayi zata fita daga dakin fuskarta dauke da murmushi,
"Zo nan, Allah karki fita"
Dawowa tayi ta tsaya, tana nan tsaye har yagama shiryawa ya dauki kayanshi yasa,
Kunun da ta Kawo mishi yasha sannan suka fita domin Tafiya asibiti,
Afalo suka iske mami cikin shiri nan suka dunguma domin tafiya amma kuma suna fitowa compound din gidan sai ga motar khadija ta kunno kai kuma tareda mahaifiyarta suke wannan dalilinne yasa mami fasa zuwa asibitin tace da yusleem da Hafsat kawai suje driver yakaisu ita kuma takoma ciki itada hajiya fa'iza da khadija,
Ganin irin gaisuwar da yusleem sukayi shida khadija yasa Hafsat yimasa magana domin daurewa khadija fuska taga yakeyi bayan kuma ita bataga laifinta ba, ganin baya son maganar yasata yin shiru ta kyaleshi.
Lokacin da sukaje asibitin Hafsat kin shiga office din dr sufyan tayi tai zamanta awaje sai yusleem ne yashiga shi kadai, ya dan jima aciki kafin yafito,
"Yaya yusleem ya kukayi?"
"Yace nanda 4 days nakara dawowa lokacin result din taste din da yayi min yafito.."
"To Allah dai ya jiyar damu alkhairi"
"Amin, muje mu tafi gida tunda babu abinda yayi saura, Dr din yana tambayarki wai yau banzo da matata ba nace tare ai muke kina waje wai ai dama yasan bazaki barni nazo ni daya ba..."
Dan murmushin yake tayi batace komai ba amma acikin ranta fadi take "Dan iskan Dr",
Lokacin da suka koma gida sai mami ita kadai domin su khadija sun tafi, ganin sun dawo da wuri mami tace Hafsat ta shirya taje driver yakaita gidansu tagaisa da iyayenta,
Garin dakakkiyar busasshiyar kubewa da kuka da daddawa wanda Maman khadija ta Kawo wa mami su mamin tabawa Hafsat tace takaiwa umminta tsaraba,
Yusleem yana kwance akan kujera mami na kujerar kusa dashi Hafsat din tafito zata tafi,
"Mami idan nadawo zan biya ta gidan amina kawata, haihuwa tayi shine zanje inga babyn.."
"To sai kin dawo, Allah ya raya.. Ki gaida hajiya kubran"
"To mami zataji"
Fita tayi nan yusleem yatashi yabita, tana daf da fita daga cikin kitchen yayi saurin rikota,
"Mami zaki tambaya unguwa saboda itace take aurenki ko? To gidanku kadai na amince kije daga nan karkije ko ina"
Juyawa yayi zai koma falo tayi saurin rikoshi,
"Dan Allah kayi hakuri yaya yusleem.. Kaji"
Shiru yayi mata ita kuma taci gaba da yimasa magiya, dakyar ya amince yace taje.
Acikin kitchen ta iske Ummi lokacin dataje gidan, ba karamin dadin ganinta hajiya kubra tajiba nan suka baje suka fara hira irinta uwa da 'ya da haka har Alhaji sa'id yazo ya samesu yadawo daga buga bugarsa domin shima ya haduda jarrabawa irinta rayuwa sai dai ita Hafsat bata saniba har saida ummi tayi mata bayanin abubuwan da suka faru na iftila'in da ya afkawa alhaji sa'id din bayan ya sayar da kadarorinsa ya tura asiyo masa kayayyaki amma har yau kayan basu fitoba gashi saboda rashin kudi kwangilar ma ba samuwa takeyi ba dan dai kawai yanada amini ne mai fada aji,
Kuka Hafsat tayi ba kadanba dalilin jin wannan labarin da hajiya kubra ta bata amma kuma tasan jarrabawa ce daga Allah shiyasa ma bata daga hankalinta ba,
Dayake sun dade basu hadu da umminba yasa Hafsat takasa tafiya da wuri har saida aka kira sallar magrib, bayan tayi sallane tatafi lokacin driver yazo daukarta, ko gidan aminan ma bataje ba gida ta wuce direct,
Mami kadai ta tarar afalo tana waya da surayya nan ta zauna har mami ta kammala wayar itama tabata suka gaisa domin rabonsu da juna tun lokacin da surayyan takoma school,
"Hafsa kin dawo? Ya kika baro mutanen gidan?" Mami ta tambaya tana kokarin ajiye wayarta,
"Lafiya lau mami, suna nan lafiya, Ummi tana gaidaki tace ayi miki godiya..."
"Babu komai wallahi, kayan ma nawa suke.."
Zama sukayi dan shiru suna kallon tv zuwa can Hafsat ta mike ta nufi bedroom, tana shiga ta iske yusleem akwance,
"Lafiya kuwa yaya yusleem?" Ta tambaya,
"Wallahi zazzabi ke damuna hafsa"
Ahanzarce takarasa kusa dashi jin jikinsa zafi zauuu tayi gashi yana dafe da cikinsa wanda ke ta faman murda masa,sannu ta shiga yimasa yana amsawa dakyar, zuwa can taji ya kamo hannunta ya dora akan cikin nasa,
Jikinta rawa yafara saboda ganin yanda yusleem yake yin murkususu gashi bata son taje tafadawa mami hankalinta yatashi,
Ruwan sanyi ta dauko tasoma shafa masa acikin nashi nan yaji ciwon yafara lafa masa ahaka har bacci ya daukeshi, ganin yasamu bacci yasa ta fita wurin mami wadda take zaune akan abin salla ta idar da sallar isha tana jan carbi,
"Hafsa ga tuwo can, wallahi yau shi naji ina sha'awa shine nace kuku yayi.."
Murmushin yake Hafsat tayi ta girgiza kai,
"Kafin nataho ma agidan Ummi saida naci abinci,wallahi na koshi.."
Wuri tasamu ta zauna amma lokaci zuwa lokaci tana dan shiga bedroom din taduba yusleem sai dai har 10 tayi bai tashiba, har sukayi sallama da mami tashiga dakinta itama ta shiga daki yusleem bacci yake,
Akusa dashi ta kwanta tana kallonshi yana rike da cikinshi, sai wurin 11 sannan yatashi yayi sallar magrib da isha wadanda ke kanshi domin bai samu damar yiba,
Kalau yayi sallar ya idar tana zaune tana kallonshi yana idarwa kuma yace sai ta dama masa kunu yasha yunwa yakeji, tare suka fita zuwa kitchen din ta tafasa ruwa ta dama masa kunun suka koma daki, saida yagama sha sannan suka kwanta, tana ji yafara tsokanarta kamar bashi bane dazu yake murkususu kamar zai mutuba,
Bata San lokacin da yagama tsokanar tataba domin bacci tayi tabarshi, can tsakiyar dare kuma kamar acikin mafarki take jin kakarin amai nan tatashi taganshi kwance yana juyi yana rikeda cikinsa, ruwan sanyi ta debo tafara shafa masa amma yanzu ji yake kamar ruwan zafi tafasasshe take Shafa masa, kunun da yasha kuwa saida yayi amansa gaba daya,rikeshi tayi nan ya kuwa kankameta kamar zai koma cikin cikinta daga shi har ita babu wanda yasake runtsawa har asuba tayi ita dai agaba tasashi tana hawaye,
Ganin abin yayi yawa gashi yana yin wani irin amai kore kore yellow yellow yasa hafsa zuwa ta sanarwa da mami lokacin karfe 5:30,
Driver mami tayiwa waya kasancewar a B/Q yake zaune, nan da nan yafito suka kama yusleem suka nufi asibitin Dr sufyan dashi,
Kallo daya zaka yiwa mami da Hafsat kagane acikin tashin hankali suke domin kowannensu fuskarshi kunshe take da tashin hankalin,
Emergency aka kai yusleem bayan kamar mintuna 30 Dr mufid yafito dauke da file din yusleem domin lokacin Dr sufyan bai fitoba,binsa mami da Hafsat sukayi abaya domin jin abinda zaice,
"Hajiya in my opinion ni ina ganin cewar is better for u idan kuka fitar da patient dinku kasar Cairo ko kuma India saboda sincerely speaking yana cikin bad condition domin cutar dake tattare dashi itace take cousing din wannan ciwon cikin da yake fama dashi, and kuma akwai wani aiki da zasuyi masa wanda mu bazamu iyaba, so idan zai yuyu in the next 3 days ku samar masa visa sai ku fita dashi domin magana tagaskiya bama karbar patients wadanda lalurarsu tazama chronic kuma worst saboda kinga nan is private hospital dole sai mun zama muna him takatsantsan..."
Yana ida wannan bayanin yagyara farin glass dinshi yayi gaba, sororo mami da Hafsat sukayi kowannensu yana tunanin hanyar da za abi har akai ga fitar da yusleem kasar waje....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_DEDICATED TO MISS XOXO_
_Fatan alkhairi ga yan kungiyar haske writers association, shafin yau nakune ku kadai domin jin dadinku..._
*42*
***Daga mami har Hafsat ji sukayi kamar ruwa ya cinyesu dalilin jin bayanin da dr yayi musu nan hankalin kowanne acikinsu yakai kololuwar tashi,
Mami ce tafara magana fuskarta cikeda murmushin yake,
"Hafsat babu komai kinji, karki daga hankalinki insha Allah zamu samu yanda zamuyi..."
Wasu hawaye ne suka zubowa Hafsat tasa gefen hijabinta ta share batare da tayi magana ba,
Kama hannunta taji mami tayi suka bar wurin suka koma reception,
"Yanzu Hafsat ina zuwa bari naje gida nadawo kinji..."
"To mami sai kin dawo, Allah kiyaye hanya.."
Tashi mami tayi tafita, yayinda ita kuma Hafsat taci gaba da zama awurin zuciyarta kunshe fal da tarin tunani.