Sashe 13
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganinta yasa surayya fara yin dariya kasa kasa,
"Amarya da alama dai jiya yaya bai gayyaceki dakin nashi ba shiyasa har nakaiki baki san can bane"
Zama Hafsat tayi tana yamutsa fuska,
"Dama kin san dakinsa ne shine kika ce inshiga ko?"
Dariya surayya tayi,
"To ba gashi kinyi gaisuwar safe ba.."
Kyaleta Hafsat tayi batace komai ba amma yanzu ta fahimci miskilin mutum Allah ya hadata zama dashi,
Haka suka cigaba da zama itada surayya har yan uwan hajiya kubra suka zo suka tafi suna tafiya yan uwan mami da kawayenta suma suka zo, duk wanda yazo gidan sai yasa albarka kuma sai yaji yayi sha'awarsa domin yayi sosai, amma wasu daga cikin kawayen mami da sukazo suka ga gida sannan suka ga Hafsat saida tausayinta yakamasu domin sun san itama kwana nawane yusleem zai tarkatata yakorata da saki dai dai dai dai har uku.
Har dare surayya tana gidan sai bayan sallar isha dasu khalifa suka zo tace zata bisu tatafi,
Hafsat kallon samarin tayi wato Abdul da khalifa duk da bata taba ganinsuba amma tasan dai kannen yusleem ne domin ga kama nan sai dai duk cikinsu shine fari domin har surayya batafi Hafsat din fariba shikuwa yusleem farine sol,
"Kinga kannen yaya, yakika gansu? Sunfishi kyau ko?"
Murmushi Hafsat tayi, "ke kika sani"
Gaisawa sukayi daga nan sukai mata sallama suka tafi,
Tunda suka tafi kuma tazauna shiru ita kadai daga karshema taji tsoro yafara shigarta dan haka ta tattara takoma bedroom dinta tayi shirin bacci ta kwanta.
Tun daga wannan ranar bata sake saka yusleem acikin idonta ba,kullum tareda surayya suke wuni har dare, da haka har tayi sati daya agidan,
Rabonta da ganin yusleem kuwa tun ranar da surayya tazo last wanda yashigo falon yace mata gobe kukun da yasamo mata zai fara zuwa tace a'a zata rinka girkinta da kanta, juyawa yayi gurin surayya tatashi ya maida ta gida, tun daga ranar Hafsa bata kara ganinshi ba gashi yanzu surayya bata nan sati biyu kenan da tafiyarta Kaduna gidan kanwar mami,
Haka take wuni ita kadai babu abokin hira, bata san fitar yusleem ba bare tasan dawowarsa.
Ranar alhamis da safe misalin karfe 11 saiga mami tazo gidan,
Da murna Hafsat ta karbeta, bayan sun gaisa mamin ke tambayarta yusleem din tashi tayi tafita tace bari ta kirashi,
Faduwa gabanta yafara yi lokacin data doshi dakin nasa, ahankali ta tura ta shiga, tayi sa'a kuwa yana nan,
Yana kan gado akwance yana bacci,
"Yaya... Yaya.." Tafara kiranshi, bude idonshi yayi, kallo daya yayi mata ya maida idanuwanshi ya rufe,cikin sanyayyiyar muryarshi mai dadi yace,
"Menene?,idan ina bacci ba a tashina"
"Mami ce tazo shine tace inkira ka,amma kayi hakuri"
Ganin bashida niyyar amsa mata yasata juyawa zata fita, har takai bakin kofa taji muryarsa,
"Zo.." Komawa tayi wurinshi,
"Bude drewar dinnan ki miko min t shirt dina"
Budewa drewar din tayi ta dauko masa t shirt guda daya ja ta mika masa,
"Ajiye anan"
Ajiyewa tayi ta juya zata fita,
"Kinga..."
Dawowa tasake yi,
"Kin iya dafa tea?"
"Ehh na iya"
"Ki dafa min, kicewa mami ina zuwa"
Da "to" ta amsa tajuya tafita tana mamakinshi acikin ranta domin sam bashida alkibla tarasa gane inda yasaka gaba......
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*24*
***Wurin mami Hafsat takoma tafada mata cewa yusleem din yace yana zuwa daga nan ta tashi ta shiga kitchen domin dafa masa tea din,
Dama indai fannin girki ne to bata da matsala domin zaman da tayi agida bawai zama tayi ta zuba ido sai dai adafa abata taci ba, tare suke yin komai da hajiya kubra, wata rana ma ita kadai ce keyin girkin,
Dankali ta fere ta soya masa bayan tagama dafa tea din sannan ta dan jajjaga kayan miya kadan ta yimasa sos din kwai, akan babban faranti ta dauki kayan tafita,
Zaune ta iskesu shida mami ya sunkuyar da kai yana zaune akan kujerar dake facing din ta mamin abisa dukkan alamu wata maganar suke yi mai muhimmanci, agabanshi ta ajiye tiren tajuya ta koma kitchen ta dauko na mami ta Kawo mata itama ta ajiye, sai binta da kallo mamin keyi cikin farin ciki tana yi mata sannu,
Ganin kamar maganar da sukeyi mai muhimmanci ce yasata kin zama awurin dan haka tana kammala ajiye musu abincin ta juya takoma kitchen ta hada yan kayayyakin da tayi amfani dasu tasoma wankewa,
Acan falo kuwa koda Hafsat ta fita mami kallonshi tayi,
"Yusleem anya kuwa kana zama tareda yarinyar nan kuyi hira kuyi wasa da dariya a matsayinku na ma'aurata?"
Sunkuyar da kai yayi,
"Mami me kika gani?"
"To ai gani nayine kamar tana dan dari dari dakai, dan ko lokacin da nace ta kiraka saida naga tayi wani dan jimmm"
Murmushi ne ya kwace masa saboda abinda yaji mami tace wanda har hakan yayi sanadiyyar ajiye cup din dake hannunsa,
"Mami kenan, wallahi babu komai kuma ki tambayeta kiji"
"Ehh ai zan tambayeta din, amma kasani wallahi muddin naji kana takura mata ko wani abu mai kamada haka to sai ranka ya baci..."
Murmushi yayi ya dauki shayin yaci gaba da kurba domin ba karamin dadi yayi ba kasancewar da kayan kamshi Hafsat ta dafashi shiyasa in banda kamshi babu abinda yake yi,
"Kaci dankalin mana gashinan, kai mai son dankali.." Yaji muryar mami tana yimasa magana, shifa sam bai taba cin a abincin Hafsat ba, bama wannan ne abin mamakin ba abin mamakin shine har yau baisan kamanninta ba domin ko kallon minti 1 bai taba yimata ba bare har yaga yadda take,
Bude flask din data zubo masa dankalin yayi yadiba a filet yadebi sos din yadora akai yafara ci,
Yana ci suna maganar da suka fara da mami har saida ya cinye dankalin domin baifi kwaya biyar ba wanda yabari acikin flask din,
Hafsat kam tana kitchen bayan tagama aikinta ma wuri ta samu ta zauna saboda bata son taje tasaka su mami agaba ta hanasu sakewa suyi zancen da suke,
Tana zaune akan kujera ta jingina da jikin deep freezer taji kamshin turarensa na oud abyad,sam bataji shigowarsa ba bare tafiyarsa,
Akanta ya tsaya kamar wani soja yana kallon wani wuri,
"Me kikeyi?"
"Aiki nagama yanzu shine nazauna ina hutawa.."
"To zo.."
Yace da ita tareda juyawa yayi gaba, tashi tayi tabi bayansa tana kallon irin yanda jar rigar da yasaka ta kara haskashi,
"Hafsat kizo ki zauna ki huta mana, inata kiranki bakiji ba,sannu kinji, tunda nazo gidan nan baki zauna ba sai aiki kike tayi..."
Murmushi tayi saboda jin abinda mami tace, akasa ta zauna kusa da kujerar da mamin ke kai,
"Mami ai aikin bashida yawa..."
"Duk da haka dai Hafsa ai kina kokari, gashi kin hadu da miji mai tsirfa Wanda ba kowanne abinci yake ciba, kin ganshi nan haka yake kamar wani marar lafiya sam bashi son cin abinci..."
"Uhm.." Kawai Hafsat tace ta danyi murmushi domin ita kwata kwata ma yusleem bai taba cin abincinta ba,
"Bari intashi inje intafi, akwai ta wurin da zan biya dama cewa nayi bari inkaraso inganku, Hafsat ai babu matsalar komai ko?"
Takarashe maganar tana dafa kafadar hafsa,
"Wallahi mami babu komai.."
"A'a hafsa idan da wani abu ki fada min saboda nasan halin yusleem sarai, bahagon mutum ne koni da na haifeshi ban fiya gane mishi ba.."
"Allah mami babu komai da ace akwai wani abu ai zan fada miki.."
"To shikenan, taso muje akwai abinda nakawo miki"
Mikewa mami tayi itama Hafsat din ta tashi, kallon yusleem mami tayi,
"Kai kayi zamanka basai ka tasoba saboda ina son zan ganta ita kadai.."
"To mami asauka lafiya" yusleem ya amsa mata yana kokarin kishingida ajikin kujerar da yake zaune,
Kama hannunta mami tayi suka fita,
"Hafsat kikace babu komai? Idanfa akwai wani abu ki sanar dani"
"A'a mami babu komai"
"Baya takura miki?"
"Wallahi mami babu abinda yake min"
"To shikenan dama haka nake son ji, bari ga wani sako da na Kawo miki,turare ne na tsugunno tun daga chadi wata kawata ta aiko miki dashi,ki tsugunna akai kamar saura awa biyu ko uku kafin kije dakinsa"
Jin abinda mami tace yasa hafsa taji kunyar duniya ta rufeta,
"Hafsat ai ni babarki ce menene abin kunya? Ki dauka haifarki ne kawai banyi ba amma babu abinda bazanyi mikiba a duniya"
Karbar turaren tayi tana yiwa mamin godiya,
"To mami nagode Allah yakara girma"
"Amin, ai babu komai Hafsat"
Har gaban motar mamin tarakata ta bude ta shiga, tana tsaye har saida taga fitarta sannan ta juya ta koma ciki,
A wurinda suka fita suka bar yusleem yanzun ma anan ta tarar dashi ya kwanta akan doguwar kujera ya kunna tv yana kallon ball, har zata wuce tatafi bedroom dinta taji k'asa k'asa yace,
"Zo nan.."
Dawowa tayi tazo inda yake,
"Gani..."
Shiru yayi mata baiyi magana ba, tafi minti biyu atsaye, ganin yaki magana yasata fadin,
"Intafi ne?"
"Tafi in bazaki rage tsawo ba, kinzo kin wani tsaya min aka.."
Zama tayi akujerar dake makotaka da tashi,
"Bani inga abinda mami tabaki.."
Kallon mamaki ta wurga masa nan taga idanuwanshi suna kan tv,
"Ni babu abinda tabani.."
"Karya kike yi.."
Shiru tayi saboda jin abinda yafada domin dama tun lokacin da zata shigo ta cusa kullin turaren acikin zaninta,
"Muga hannunki.."
Dagasu tayi babu komai aciki,
"Idan baki baniba tashi zanyi in cajeki fa"
"Ehh nayarda.."
"Tashi kije"
Mikewa tayi tawuce bedroom dinta taje ta bude drewar din madubinta ta jefa aciki tafito ta shiga kitchen.
Girkin rana ta dora ta dafa shinkafa da taliya da miya, abin mamaki har ta kammala girkin ta fito daga cikin kitchen yusleem yana nan awurin da yake kwance yana kallon ball da alama yau babu inda zaije domin ko shirin fita baiyi ba,
Kan dining table taje ta jere abincin data girka tazo inda yake kwance akan doguwar kujera,
"Yaya ga abinci angama"
Kai kurum ya daga mata alamun yaji, bedroom dinta tawuce taje ta watsa ruwa tayi alwala domin taji anfara kiraye kirayen sallar azahar,
Bayan ta shirya ne ta koma falon, yusleem baya ciki amma ga filet nan da spoon alamun ya danci abincin data dafa,
"Amarya da alama dai jiya yaya bai gayyaceki dakin nashi ba shiyasa har nakaiki baki san can bane"
Zama Hafsat tayi tana yamutsa fuska,
"Dama kin san dakinsa ne shine kika ce inshiga ko?"
Dariya surayya tayi,
"To ba gashi kinyi gaisuwar safe ba.."
Kyaleta Hafsat tayi batace komai ba amma yanzu ta fahimci miskilin mutum Allah ya hadata zama dashi,
Haka suka cigaba da zama itada surayya har yan uwan hajiya kubra suka zo suka tafi suna tafiya yan uwan mami da kawayenta suma suka zo, duk wanda yazo gidan sai yasa albarka kuma sai yaji yayi sha'awarsa domin yayi sosai, amma wasu daga cikin kawayen mami da sukazo suka ga gida sannan suka ga Hafsat saida tausayinta yakamasu domin sun san itama kwana nawane yusleem zai tarkatata yakorata da saki dai dai dai dai har uku.
Har dare surayya tana gidan sai bayan sallar isha dasu khalifa suka zo tace zata bisu tatafi,
Hafsat kallon samarin tayi wato Abdul da khalifa duk da bata taba ganinsuba amma tasan dai kannen yusleem ne domin ga kama nan sai dai duk cikinsu shine fari domin har surayya batafi Hafsat din fariba shikuwa yusleem farine sol,
"Kinga kannen yaya, yakika gansu? Sunfishi kyau ko?"
Murmushi Hafsat tayi, "ke kika sani"
Gaisawa sukayi daga nan sukai mata sallama suka tafi,
Tunda suka tafi kuma tazauna shiru ita kadai daga karshema taji tsoro yafara shigarta dan haka ta tattara takoma bedroom dinta tayi shirin bacci ta kwanta.
Tun daga wannan ranar bata sake saka yusleem acikin idonta ba,kullum tareda surayya suke wuni har dare, da haka har tayi sati daya agidan,
Rabonta da ganin yusleem kuwa tun ranar da surayya tazo last wanda yashigo falon yace mata gobe kukun da yasamo mata zai fara zuwa tace a'a zata rinka girkinta da kanta, juyawa yayi gurin surayya tatashi ya maida ta gida, tun daga ranar Hafsa bata kara ganinshi ba gashi yanzu surayya bata nan sati biyu kenan da tafiyarta Kaduna gidan kanwar mami,
Haka take wuni ita kadai babu abokin hira, bata san fitar yusleem ba bare tasan dawowarsa.
Ranar alhamis da safe misalin karfe 11 saiga mami tazo gidan,
Da murna Hafsat ta karbeta, bayan sun gaisa mamin ke tambayarta yusleem din tashi tayi tafita tace bari ta kirashi,
Faduwa gabanta yafara yi lokacin data doshi dakin nasa, ahankali ta tura ta shiga, tayi sa'a kuwa yana nan,
Yana kan gado akwance yana bacci,
"Yaya... Yaya.." Tafara kiranshi, bude idonshi yayi, kallo daya yayi mata ya maida idanuwanshi ya rufe,cikin sanyayyiyar muryarshi mai dadi yace,
"Menene?,idan ina bacci ba a tashina"
"Mami ce tazo shine tace inkira ka,amma kayi hakuri"
Ganin bashida niyyar amsa mata yasata juyawa zata fita, har takai bakin kofa taji muryarsa,
"Zo.." Komawa tayi wurinshi,
"Bude drewar dinnan ki miko min t shirt dina"
Budewa drewar din tayi ta dauko masa t shirt guda daya ja ta mika masa,
"Ajiye anan"
Ajiyewa tayi ta juya zata fita,
"Kinga..."
Dawowa tasake yi,
"Kin iya dafa tea?"
"Ehh na iya"
"Ki dafa min, kicewa mami ina zuwa"
Da "to" ta amsa tajuya tafita tana mamakinshi acikin ranta domin sam bashida alkibla tarasa gane inda yasaka gaba......
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*24*
***Wurin mami Hafsat takoma tafada mata cewa yusleem din yace yana zuwa daga nan ta tashi ta shiga kitchen domin dafa masa tea din,
Dama indai fannin girki ne to bata da matsala domin zaman da tayi agida bawai zama tayi ta zuba ido sai dai adafa abata taci ba, tare suke yin komai da hajiya kubra, wata rana ma ita kadai ce keyin girkin,
Dankali ta fere ta soya masa bayan tagama dafa tea din sannan ta dan jajjaga kayan miya kadan ta yimasa sos din kwai, akan babban faranti ta dauki kayan tafita,
Zaune ta iskesu shida mami ya sunkuyar da kai yana zaune akan kujerar dake facing din ta mamin abisa dukkan alamu wata maganar suke yi mai muhimmanci, agabanshi ta ajiye tiren tajuya ta koma kitchen ta dauko na mami ta Kawo mata itama ta ajiye, sai binta da kallo mamin keyi cikin farin ciki tana yi mata sannu,
Ganin kamar maganar da sukeyi mai muhimmanci ce yasata kin zama awurin dan haka tana kammala ajiye musu abincin ta juya takoma kitchen ta hada yan kayayyakin da tayi amfani dasu tasoma wankewa,
Acan falo kuwa koda Hafsat ta fita mami kallonshi tayi,
"Yusleem anya kuwa kana zama tareda yarinyar nan kuyi hira kuyi wasa da dariya a matsayinku na ma'aurata?"
Sunkuyar da kai yayi,
"Mami me kika gani?"
"To ai gani nayine kamar tana dan dari dari dakai, dan ko lokacin da nace ta kiraka saida naga tayi wani dan jimmm"
Murmushi ne ya kwace masa saboda abinda yaji mami tace wanda har hakan yayi sanadiyyar ajiye cup din dake hannunsa,
"Mami kenan, wallahi babu komai kuma ki tambayeta kiji"
"Ehh ai zan tambayeta din, amma kasani wallahi muddin naji kana takura mata ko wani abu mai kamada haka to sai ranka ya baci..."
Murmushi yayi ya dauki shayin yaci gaba da kurba domin ba karamin dadi yayi ba kasancewar da kayan kamshi Hafsat ta dafashi shiyasa in banda kamshi babu abinda yake yi,
"Kaci dankalin mana gashinan, kai mai son dankali.." Yaji muryar mami tana yimasa magana, shifa sam bai taba cin a abincin Hafsat ba, bama wannan ne abin mamakin ba abin mamakin shine har yau baisan kamanninta ba domin ko kallon minti 1 bai taba yimata ba bare har yaga yadda take,
Bude flask din data zubo masa dankalin yayi yadiba a filet yadebi sos din yadora akai yafara ci,
Yana ci suna maganar da suka fara da mami har saida ya cinye dankalin domin baifi kwaya biyar ba wanda yabari acikin flask din,
Hafsat kam tana kitchen bayan tagama aikinta ma wuri ta samu ta zauna saboda bata son taje tasaka su mami agaba ta hanasu sakewa suyi zancen da suke,
Tana zaune akan kujera ta jingina da jikin deep freezer taji kamshin turarensa na oud abyad,sam bataji shigowarsa ba bare tafiyarsa,
Akanta ya tsaya kamar wani soja yana kallon wani wuri,
"Me kikeyi?"
"Aiki nagama yanzu shine nazauna ina hutawa.."
"To zo.."
Yace da ita tareda juyawa yayi gaba, tashi tayi tabi bayansa tana kallon irin yanda jar rigar da yasaka ta kara haskashi,
"Hafsat kizo ki zauna ki huta mana, inata kiranki bakiji ba,sannu kinji, tunda nazo gidan nan baki zauna ba sai aiki kike tayi..."
Murmushi tayi saboda jin abinda mami tace, akasa ta zauna kusa da kujerar da mamin ke kai,
"Mami ai aikin bashida yawa..."
"Duk da haka dai Hafsa ai kina kokari, gashi kin hadu da miji mai tsirfa Wanda ba kowanne abinci yake ciba, kin ganshi nan haka yake kamar wani marar lafiya sam bashi son cin abinci..."
"Uhm.." Kawai Hafsat tace ta danyi murmushi domin ita kwata kwata ma yusleem bai taba cin abincinta ba,
"Bari intashi inje intafi, akwai ta wurin da zan biya dama cewa nayi bari inkaraso inganku, Hafsat ai babu matsalar komai ko?"
Takarashe maganar tana dafa kafadar hafsa,
"Wallahi mami babu komai.."
"A'a hafsa idan da wani abu ki fada min saboda nasan halin yusleem sarai, bahagon mutum ne koni da na haifeshi ban fiya gane mishi ba.."
"Allah mami babu komai da ace akwai wani abu ai zan fada miki.."
"To shikenan, taso muje akwai abinda nakawo miki"
Mikewa mami tayi itama Hafsat din ta tashi, kallon yusleem mami tayi,
"Kai kayi zamanka basai ka tasoba saboda ina son zan ganta ita kadai.."
"To mami asauka lafiya" yusleem ya amsa mata yana kokarin kishingida ajikin kujerar da yake zaune,
Kama hannunta mami tayi suka fita,
"Hafsat kikace babu komai? Idanfa akwai wani abu ki sanar dani"
"A'a mami babu komai"
"Baya takura miki?"
"Wallahi mami babu abinda yake min"
"To shikenan dama haka nake son ji, bari ga wani sako da na Kawo miki,turare ne na tsugunno tun daga chadi wata kawata ta aiko miki dashi,ki tsugunna akai kamar saura awa biyu ko uku kafin kije dakinsa"
Jin abinda mami tace yasa hafsa taji kunyar duniya ta rufeta,
"Hafsat ai ni babarki ce menene abin kunya? Ki dauka haifarki ne kawai banyi ba amma babu abinda bazanyi mikiba a duniya"
Karbar turaren tayi tana yiwa mamin godiya,
"To mami nagode Allah yakara girma"
"Amin, ai babu komai Hafsat"
Har gaban motar mamin tarakata ta bude ta shiga, tana tsaye har saida taga fitarta sannan ta juya ta koma ciki,
A wurinda suka fita suka bar yusleem yanzun ma anan ta tarar dashi ya kwanta akan doguwar kujera ya kunna tv yana kallon ball, har zata wuce tatafi bedroom dinta taji k'asa k'asa yace,
"Zo nan.."
Dawowa tayi tazo inda yake,
"Gani..."
Shiru yayi mata baiyi magana ba, tafi minti biyu atsaye, ganin yaki magana yasata fadin,
"Intafi ne?"
"Tafi in bazaki rage tsawo ba, kinzo kin wani tsaya min aka.."
Zama tayi akujerar dake makotaka da tashi,
"Bani inga abinda mami tabaki.."
Kallon mamaki ta wurga masa nan taga idanuwanshi suna kan tv,
"Ni babu abinda tabani.."
"Karya kike yi.."
Shiru tayi saboda jin abinda yafada domin dama tun lokacin da zata shigo ta cusa kullin turaren acikin zaninta,
"Muga hannunki.."
Dagasu tayi babu komai aciki,
"Idan baki baniba tashi zanyi in cajeki fa"
"Ehh nayarda.."
"Tashi kije"
Mikewa tayi tawuce bedroom dinta taje ta bude drewar din madubinta ta jefa aciki tafito ta shiga kitchen.
Girkin rana ta dora ta dafa shinkafa da taliya da miya, abin mamaki har ta kammala girkin ta fito daga cikin kitchen yusleem yana nan awurin da yake kwance yana kallon ball da alama yau babu inda zaije domin ko shirin fita baiyi ba,
Kan dining table taje ta jere abincin data girka tazo inda yake kwance akan doguwar kujera,
"Yaya ga abinci angama"
Kai kurum ya daga mata alamun yaji, bedroom dinta tawuce taje ta watsa ruwa tayi alwala domin taji anfara kiraye kirayen sallar azahar,
Bayan ta shirya ne ta koma falon, yusleem baya ciki amma ga filet nan da spoon alamun ya danci abincin data dafa,