← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 30

Sashe 26

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana nan zaune tarasa abinda yake mata dadi tahango dr sufyan yana kokarin shigowa cikin reception din hannunsa dauke da wata yar madaidaiciyar bag, ko kallonsa batayi ba ta dauke kanta takaishi can gefe, shikuwa kura mata ido yayi har ya bace ya nufi office dinshi,

Kimanin mintuna 30 da tafiyar mami sai gata ta dawo, tun kallon farko da Hafsat tayi mata ta fahimci cewar akwai damuwa a tattare da ita amma dai sai batayi magana ba domin daga ita har mami din kowa ba son yin maganar yake ba,

Emergency suka shiga wurin da yusleem ke kwance yana bacci, gaban gadon sukaje suna kallonsa,

"Ni wannan abu ya daure min kai, wai menene takamaimai abinda yake damunsa ne? Ni duk ban fahimci bayanin da Dr yayiba hafsat..." Mami tayi maganar idanuwanta na kan yusleem wanda yake kwance yana fitar da numfashi,

"To nima dai mami maganar dr ta daure min kai amma a iya sanina dai wannan ciwon cikin shine ke damun yaya yusleem"

"To ko komawa zanyi wurin Dr din insake tuntubarsa inji?"

"A'a mami da dai mun hakura kawai munyi yanda yace din.."

"To yanzu hafsat ina zamu samu kudaden da zamuyi hakan? Hafsat yanzu ba babu abinda muka mallaka inbanda wannan motar kwaya daya da nake hawa sai ko gidan da muke ciki..."

"Babu komai mami ki kwantar da hankalinki insha Allah komai zai zama daidai saboda Allah baya taba dorawa bawansa abinda bazai iyaba"

Ajiyar zuciya mami ta yi suka fita daga cikin emergency room din suka koma waje suka zauna,

Wuni guda cur yusleem yana bacci sai yamma yafarka, hafsat ce ta karasa wurinsa domin ita mami tatafi gida ta dawo wanda tafiyar tata bazata rasa nasaba ba dayin wanka sannan da shiryo abinci,

"Sannu yaya yusleem.."

Kai ya daga mata ya lumshe idanuwansa,

"Yaya yusleem zaka sha kunun?"

Girgiza mata kai yayi bayan ya bude idonsa, kicin kicin yaga tayi tabata fuska kamar zata saka kuka, ganin haka yasashi daga mata kai alamun zaisha,ita kanta tana lura dashi sam yanzu baya son yaga bacin ranta,

Dan murmushi tayi ta tsiyayo masa kunun acikin cup ta zauna agefen gadon, yunkurawa yayi yafara kokarin tashi ta taimaka masa, duk da cewar dakin basu kadai bane akwai mutane da yawa aciki amma haka ta rinka bashi abaki yana kurba idan kuma ya disa sai ta lashe, kallonta kawai yake yi da idanuwanshi wadanda suka dan firfito har tagama bashi duk da dai bai shanyeba amma yadan sha dayawa,

Taimaka masa tayi ya kwanta ta gyara masa kwanciyar, ta zauna tana kallonshi, hannunta taji ya riko acikin nashi tareda lumshe idanuwanshi ahaka har wani baccin ya sake daukarshi.

Zuba mishi ido tayi takai hannunta bisa kuncinshi tasoma shafawa ahankali tana jin wani irin tunani yana ratsa zuciyarta, ahaka Mami ta dawo ta isketa jikinta sukuku wanda daga gani ranta abace yake gaba daya,

Jugum sukayi babu wanda yake yin magana acikinsu har tsawon wani lokaci domin kowa shi yasan tunanin da yakeyi,sai can Mami tayi karfin halin yiwa hafsat magana,

"Hafsa kitafi gida kije kiyi wanka sai kidawo.."

Duk da bata son tafiyar amma bata musawa Mami ba haka tayi mata sallama tatafi bayan ta leka yusleem ta window nan taganshi har lokacin bacci yakeyi ga drip nan ahannunshi wanda ba ajima da daura masa ba domin duk jikinshi yayi yaushi,

Mami saida ta tabbatar da cewa hafsat tatafi sannan tatashi ta nufi office din Dr sufyan,

Kimanin mintuna samada arba'in mamin ta shafe acikin office din na dr sufyan sannan daga bisani tafito, tana zama hafsat nadawowa,

Zama suka cigaba dayi har zuwa dare, lokacin ne aka fito da yusleem daga emergency aka kaishi wani daki wanda gado ne guda daya aciki irin na marassa lafiya sai fridge dan karami sannan ga yar karamar tv nan daure ajikin bango sai dan madaidaicin bathroom aciki,

"Hajiya wannan dakin kwana uku kadai zamu bashi muna treating dinshi domin dama narigada nafada miki cewar fitar dashi outside shine kadai solution agareku, therefore nan da 3 days zamu baku sallama so sai kuje gida kuci gaba da kula dashi idan kuma before time din kun sami kudin fitar dashi outside sai ku fitar dashi.." Dr mufid yafada yana sunkuye yana rubutu ajikin file din yusleem,

Kallonshi Mami da hafsat sukayi har ya kammala jawabin sannan yafita,

"Hafsat wuce kije kitafi gida ki kwanta inyaso idan Allah ya nuna mana gobe sai musan abinyi.."

Girgiza kai hafsat tayi ta kalli mami,

"A'a Mami kibarni anan din ke kitafi gida, ni zan kwana tare dashi.."

"Hafsat kije ki huta kinji, babu komai"

"Dan Allah mami kibarni kitafi, wallahi ko naje gidan ba iya barci zanyi ba"

"To shikenan tunda kinki, bari ni naje natafi, Allah yabashi lafiya"

"Amin mami"

Saida mamin tasake duba yusleem din sannan tayiwa hafsa sallama tatafi,tana fita harabar asibitin tahango dr sufyan tsaye ajikin motarshi kirar Benz new series 2017 yana sanye cikin kananan kaya, wurinshi mami takarasa dama abisa dukkan alamu ita yake zaman jira, bude mata kofar motar yayi tashiga tazauna sannan yazagaya side dinshi bayan yarufe yaja motar suka bar harabar asibitin.

Cikin dakin hafsat tashiga ta zauna akan wata kujera tana kallon yusleem wanda keta faman barci, lokaci daya ta tashi zunbur ta isa gefen gadon ta zauna, bude idonshi taga yayi,

"Sannu yaya yusleem"

Kai ya daga mata sannan yadanyi murmushi,

"Yaya yusleem ko kana bukatar wani abu ne..?"

Kanshi ya girgiza har lokacin fuskarshi tana dauke da murmushi, shiru tayi ta dan jingina da jikin bango, gyangyadi ta dan soma yi amma da zarar baccin yafara daukarta zatayi firgigit ta bude idonta,

Matsawa yusleem ya danyi yakamo hannunta, idonta Wanda yake cike da barci ya bude domin daren jiya bata samu tayi ba,

"Kizo ki kwanta..."

"Bari inshinfida hijabina akasa kawai sai in kwanta saboda kar intakura maka"

"Gashi na matsa miki"

Girgiza kai tayi zata sauka daga kan gadon, tashi shima yayi da niyyar sauka tayi saurin rikeshi,

"Haba yaya yusleem kaida bakada lafiya,dan Allah kakoma ka kwanta"

Dakyar ya kwanta din hannunshi rikeda ita dole ta hakura ta kwanta akusa dashi,

Sassafe saiga mami tazo, office din dr sufyan tafara zuwa amma lokacin bai fitoba, wurinsu hafsa taje, hafsat din tana zaune akan kujera shikuma yusleem yana kan gado akwance,

Tare da mamin suka cigaba da zama har karfe 9 tayi lokacinne driver yakawo musu abinci amma ita mami bata samu damar cin abincin ba domin hankalinta yana can office din Dr sufyan, hajiya kubra da alhaji sa'id ne suka zo duba yusleem din bayan an dan gaggaisa mami ta zare jikinta ta fita, office din Dr sufyan tashiga wanda yake abude alamun yana ciki,

Lokacin da hafsat tafito domin raka su hajiya kubra sukayi kicibus da mami, godiya mami tayiwa su hajiya kubra sukayi sallama suka wuce ita kuma tanufi dakin da yusleem yake,

Hafsat kam saida ta rakasu har wurinda motarsu take sannan tajuya ta takoma, tana shiga cikin dakin ta iske mami tana shirya kudi rafa rafa sabbi kal yan dubu dubu acikin jakarta wadanda zasu doshi samada naira dubu dari tara, cikeda mamaki hafsat ta karasa gaban mami wacce ke zaune akan kujera.....

_Fans kuyi hakuri da jina shiru da kukayi kwana biyu, kun san jiki da jini amma alhamdulillah naji sauki sosai, hakika bani da bakin da zan gode muku,duk wadanda suka kirani suka gaisheni da wadanda suka min text nagode Allah yabar zumunci._

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_DEDICATED TO MISS XOXO_

*43*

***Gaban Mami hafsat takarasa ta tsugunna fuskarta cikeda mamaki,

"Mami wannan kudin fa?"

Fadada murmushi mami tayi batare da ta dago ta kalli hafsat ba domin hankalinta yanaga kan kudin da take lissafawa,

"Hafsat wani al'amari ne ya gudana wanda yayi sanadiyyar samuwar wannan kudin, kinga dr kwana uku kacal yabamu yace daga nan sallamace zata biyo baya to shiyasa naga gara fa intashi atsaye innemo kudi duk inda yake domin mu fitar da yusleem kasar Cairo.."

"Hakane mami, amma yanzu kin san kudi yana wuyar samuwa shiyasa nace garin yaya aka samo wadannan kudaden masu yawa.."

Rufe handbag din mami tayi ta maida hankalinta gurin hafsat da niyyar yimata bayani amma kafin takai ga farawa sukaji anturo kofar dakin da suke ciki anshigo, dukkaninsu maida idanuwansu wurin sukayi domin ganin wanda zai shigo,

Khadija ce ta shigo hannunta rikeda basket din abinci, tana sanye cikin bakar doguwar riga ta yane kanta da mayafin rigar inbanda kamshi babu abinda take zubawa,

"A'a khadija ce? Sannu da zuwa" mami tayi maganar tana fadada fara'arta,

"Yawwa sannu mami" khadija tafada tareda ajiye basket din hannunta ta durkusa kasa tagaida mami,

"Mami ina kwana? Ya mai jikin? Allah yabashi lafiya"

Cikin raha mami ta amsa gaisuwar, kallon khadija hafsat tayi tayi mata sannu da zuwa sannan suka gaisa,

Gaban gadon yusleem khadija takarasa amma har lokacin bai tashi daga bacci ba dan haka tadawo wurinsu mami ta zauna suka cigaba da zaman tare,

Zuwa can bayan yan wasu mintuna nurse tashigo ta dan dubashi tayi rubutun da zatayi tafita, fitarta babu wuya yusleem din yatashi, idanuwansa fess yasaukesu akan hafsat wacce ke zaune kusa da khadija, ita kuma khadijan sai danne dannenta takeyi awayarta,

Tashi hafsat tayi taje wurinda yake itada mami,

"Hafsat taimaka min inje bathroom.."

Ba iya hafsat dince kadai ta rikeshi ba harda mami suka taimaka mishi yasauko daga kan gadon suka rirrikeshi,

Tasowa khadija tayi tana cewa mami,

"Ayya mami barshi, kawo intayata.."

"Lahh babu komai khadija da kinyi zamanki kin huta" inji mami,

"A'a mami dan Allah barshi kije ki zauna"

Hade fuska yusleem yayi bai bari khadijan takai ga rikeshi ba yafada cikin toilet, dukkansu sororo sukayi banda khadija da ke yin dan murmushin yake,

Dukkansu komawa sukayi suka zauna hafsat ce kadai ta tsaya tana jiran yafito, bai jima sosai ba yabude kofa yafito yana faman bin bango, rikeshi hafsat tayi har zuwa gefen gadon,

"Salla fa nake son yi" yace da hafsat,

"To bari in shimfida maka dan kwalina sai kayi.."

"A'a inada carpet acikin mota bari inkawo.." Khadija tace sannan ta mike tafita, dan satar kallonshi hafsat tayi har lokacin fuskarshi kicin kicin take babu walwala,
Chapter 26 · 0% Book details