Sashe 24
Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kibari kawai muci gaba da zama anan idan ta huce sai muje mu bata hakuri"
Girgiza kai tayi bayan ta rike hannunshi cikin nata,
"A'a yaya yusleem, mubi umarninta mu tattara kayanmu muje, bai kamata muyi watsi da maganarta ba.."
Tashi tayi batare da tajira abinda zaiceba ta shiga tattara kaya dama kuma kayan ba wadansu masu yawa bane, cikin toilet ta shiga ta kwaso inner wears dinsu dake shanye tazo ta zuba acikin trolley, har lokacin yusleem na zaune baiko motsa ba,
Kayan da tasan bazai yiyu su tafi dasu yanzuba ta tattara wuri daya ta adana sannan tafita daga dakin taje dakin maman amir tayi mata sallama, kasancewar sunyi sabo maman amir harda kuka, ita kanta Hafsat din da hawaye tadawo cikin dakin,
Tashi yayi ya rungumota jikinshi yana murmushi,
"Menene na kukan kamar ance bazaku sake haduwa ba..., sorry.."
Har lokacin hawayen basu bar zuba a idonta ba,
"Ya isa haka, kiyi shiru dan Allah"
Dakyar ta iya tsayar da hawayen yusleem ya dauki trolley dinsu suka fita acikin ranshi yana mamakin mata su babu wuya yanzun nan zasuyi maka kuka,
Har waje mutanen gidan suka rakasu duk da ba wai wani zumunci mai zurfi sukeyi ba,
Adaidaita sahu suka shiga yakaisu har gidan mami,
Gidan yana nan kamar da babu abinda ya sauya sannan ga ma'aikata nan kowa yana aikinsa kamar yanda suka saba, ganin su yusleem yasa masu gadin gidan saurin amsar kayan dake hannunsu suka shigar musu dashi ciki,kowa sai sannu da zuwa yake yiwa yusleem domin duk atunaninsu daga doguwar tafiya yadawo,
Acikin falo suka iske mami tana zaune tana shan ruwan lipton sannan ga soyayyen chips with kidney sos tana dan tsakura kadan kadan tana ci da dukkan alamu sai yanzu take yin breakfast,
Jin sallamarsu yasanyata dagowa ta kallesu bayan ta amsa, akasa Hafsat ta zauna yayinda yusleem yazauna akujerar dake kusa da ta mami,
"Hafsa ga abinci can maza tashi kije kici kinji..."
"Wallahi mami munci abinci sai dai idan anjima.."
Shiru mamin tayi batace komai ba taci gaba da kurbar ruwan tea dinta, suna nan zaune shiru babu wanda yasake magana har mami ta kammala cin abincin,
Sunkuyar da kai Hafsat tayi tasoma bawa mami hakuri,
"Mami dan Allah kiyi hakuri da abinda yafaru, wallahi ba laifinsa bane laifina ne domin nice nabashi wannan shawarar kuma nima nayi hakanne dan gudun kada mu tayar miki da hankali, amma dan Allah kiyi hakuri.."
Ajiyar zuciya mami tayi ta kalli yusleem sannan ta kalli Hafsat,
"To shikenan Hafsat nahakura, amma meyake faruwa? Nasan dai duk yanda akayi akwai abinda ke faruwa daku"
"Ehh mami da akwai, bashin banki yaya yusleem yaci sukuma kin san dokarsu idan baka biyasu ba sai sun sayar da komai naka, to shima yaya yusleem din hakance tafaru kuma lokacin nasan idan kikaji hankalinki tashi zaiyi shiyasa nace mubari tukunna sai zuwa wani lokaci sai mu fada miki..."
Tafa hannuwa mami tashiga yi tana salati,
"To garin yaya?"
Kallon yusleem tayi,
"Kai agarin yaya kaciyo bashin banki batare da sanina ba?"
"Mami tsautsayi da kaddara, saboda dama tun asali da wannan bashin nasu nayi arziki, komai da kika sani nasune, nikuma nayi hakanne dan incika burinki inzama mai wadata kamar yadda kike muradi..."
Katse shi mami tayi cikin fada tace,
"Ungo nan.." Dakuwa tayi masa sannan ta dora da cewa,
"Shikenan kuma dan ina son kayi arziki sai kaje ka aikata ba daidai ba? Ai ni bance kayi kudi kota halin kaka ba, haba yusleem meyasa zakabi shawarar zuciya? Ko dan gaba karka sake aikata makamancin wannan, yanzu da ace sun kamaka sunje sun daureka me gari yawaya?"
Dan zamewa yayi ya jingina bayanshi da jikin kujerar ya lumshe idanuwansa,
Kallon Hafsat mami tayi,
"Bashida lafiya ko?"
"Ehh mami amma da sauki, matsalar dai baya iya cin abinci"
Shiru mami tayi ta danyi tagumi,
"Hakika wannan wata jarrabawa ce daga Allah, domin ni dinma duk kudaden dake cikin account dina na turawa yan makaranta domin sun kusa dawowa, gashi na sissiyo kayan abinci wadanda zasuyi mana 1 month,ma'aikatan gidan nan ma wallahi wannan watan ko albashi ban biyasu ba nace suyi hakuri sai yusleem yadawo.."
"To ai babu komai mami duk wannan ba wani abu bane Allah zai bamu mafita" inji Hafsat,
"To hafsa rashin lafiyar tashifa? Ni duk ita tafi daga min hankali"
"Mami babu komai insha Allah zai samu lafiya, gobe zamu sake komawa asibitin ma ayi masa test..."
"To wai menene ke damunsa?" Mamin ta tambaya cikin damuwa,
"Mami harda ulcer dai saboda baya cin abinci wallahi"
"To Allah yabashi lafiya, goben sai muje asibitin mugani"
Shi dai yusleem yana jinsu baiyi magana ba da zaman kujerar ya isheshi ma dakin surayya yashiga wanda yake makotaka da na mami yaje ya kwanta akan gadonta,
Ita kuma mami afalo duk tabi ta damu sai jajanta rashin lafiyar yusleem takeyi, Hafsat dince ma mai karfin halin kwantarwa da mamin hankali tana cewa babu komai,
Saida lokacin salla yayi sannan Hafsat ta dauki kayanta ta nufi bedroom din surayya, akwance ta samu yusleem amma ba bacci yakeyi ba,
"Yaya yusleem tashi kayi salla..."
Tashi yayi yana kallonta,
"Hafsat meyasa baki fadawa mami gaskiyar abinda yafaru ba? Saboda ko dan nan gaba ya kamata ace tasani"
Zama tayi kusa dashi,
"A'a yaya yusleem fadar bata da alfanu hakan dai da akayi shine daidai"
"Shikenan.." Abinda yace kenan yatashi zai fita, bin bayanshi tayi zuwa falo ta dauki trolley din kayanshi tabishi, part dinsu Abdul ya bude yashiga, bedrooms biyu ne aciki sai falo domin suma samarin kowa da dakinshi, dakin khalifa yashiga tana biye dashi, juyawa yayi ya kalleta,
"Wai kina nufin ke adakin surayya zaki zauna?"
"Ehh mana"
Murmushi yayi ya karbi trolley din hannunta,
"Ashe dama karya kike da kikace bazaki iya kwana babu niba.."
Murmushi ne ya kwace mata tajuya zata fice yayi hanzarin rikota,
"Debo kayanki kidawo nan"
"Tohm" ta amsa amma bawai aikatawar zatayi ba domin tana jin nauyin mami ba kadanba,
Sakinta yayi tafita shikuma ya nufi cikin toilet.
Koda takoma part din mami salla tayi tafito falo nan ta hango kuku yana shirya lunch akan table, fitowar mami ne ya katse mata tunaninta,
Kan table suka hau, fried spaghetti da salad kukun yadafa sai kunun shinkafa, suna ci suna hira har suka gama, kunun Hafsat ta dauka tatafi kaiwa yusleem ko zai iya sha,
Akan carpet din salla ta sameshi yana tura sako ta email dinshi ackin laptop,
"Yaya yusleem ga kunu.."
Dagowa yayi ya karba ya dan kurba, zama tayi agefen gado, babu laifi yadan sha kunun ganin haka yasa taji dadi sosai, maganinshi ta dauko mishi ya karba ya hadiya daga nan tatashi tafita.
Wayarta ta Kunna bayan ta koma, ko minti biyu ba ayiba Ummi takirata, cikeda zumudi ta dauka suka gaisa nan take fadawa ummin cewar yau suka dawo amma suna gidan mami,
Suna gama waya da ummin kiran Amina yashigo, ita dinma korafin bata samunta awaya tayita yimata gashi ta jima da haihuwa mijinta yanata zuwa gidan domin yafada mata amma baya samunsu, Allah yaraya Hafsat tayi mata tace sunyi tafiya ne amma tunda sun dawo tana nan zuwa,
Komawa wurin mami tayi bayan sunyi sallama da Amina, nan take fadawa mami yusleem yadan sha kunun da takai masa tunda hakane zata rinka dama masa kullum.
Misalin karfe 8:30 nadare suna zaune afalo suna kallon tashar zee world itada mami sai gashi yashigo da cup din kunun data kaimasa, zama yayi yasoma kurbar kunun, Hafsat da mamine ke dan yin hira lokaci zuwa lokaci yana zaune yana jinsu,
Yana kallo hafsat ta shige daki bayan tayi musu saida safe, itama mami ba ajima ba tashiga nata dakin suka barshi afalo shi kadai, sai wurin 11 yakashe tv da sauran kayan wutar dake cikin falon, dakin surayya wadda Hafsat ke ciki ya shiga ya maida kofa ya rufe, gani yayi harta jima da yin bacci, bargon yabude yashiga yayi kwanciyarshi tareda mannuwa ajikinta.
Said a asubah sannan Hafsat tasan yana cikin dakin, tashi tayi tashiga bathroom tayi alwala tafito, ahankali tafara tashinsa saboda bata son mami ta jiyo,
Tashi yayi yana lullumshe ido alamun baccin bai isheshi ba,
"Yaya yusleem katafi saida safe..."
Hammar da yafara ya karasa sannan ya kalleta,
"Ina zan tafi?"
"Masaukinka..."
Baice komai ba yasauka daga kan gadon yanufi toilet, lokacin da yafito har ta idar da raka'atanul fijr tana kokarin tada ikamar sallar asubah,
Tashi yayi yakoma kan gadon ya kwanta bayan ya idar da sallar, yana kokarin lulluba da bargo Hafsat ta bazamo tazo tana masa magana kasa kasa,
"Dan Allah yaya yusleem katafi.."
"Ina?"
"Dakinka mana, bana son mami tazo taganka"
Kafin yabata amsa suka fara jiyo knocking abakin kofa da sauri Hafsat ta diro, maganar mami tajiyo tana cewa,
"Hafsat, Hafsat kitashi asubah tayi.."
"Na'am mami"
"Au ko kin tashi ma?"
"Ehh mami"
"To shikenan.."
Daga nan tajiyo alamun tafiyar mami,hannu ya mika mata yana daga kwance,kafada ta makale ta kwabe fuska, shi dinma hakan yayi kamar yadda tayi,
"Zo dan Allah"
Kan gadon ta hau ta mika masa nata hannun, kama hannun nata yayi yajata ya kwantar da ita yaja musu bargo.
_Fatan alkhairi ga Hajjaju, Chuchu, Maman sultan, pheey, Maman humy, Anty sis, Dshanty, Reane_Gh,meela adeel,meernah parrot,khadija sadeeq,Billy s fari, Billy s jega, ummu abrar, anty Baraka, Maman mujahid da duk wadanda ban ambata ba, wannan shafin nakune kyauta domin jin dadinku._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*Yau shafin nakune kawayena, Lubabatu mai tafsir, fiddausi sodangi,phertymah xarah Maman khadija, cwt Kausar Luv, Teemah Cool,Khaleesat Haidar, Hafsat bunza, Zee Rumah,Maman Shakur Benaxir oamar,Billy Galadanchi, ina yimuku fatan alkhairi aduk inda kuke...*
*41*
_Ina cikiyar RIRI TURAKI marubuciyar halal dina, idan sakona ya riskeki ni Ummi Shatu ina nemanki urgently._
***Misalin karfe 9 Hafsat tafarka daga bacci, juyawa tayi ta kalli yusleem wanda ke rike da hannunta yana kanannade da ita, dakyar ta iya tureshi daga jikinta ta tashi,
Wanka tashiga tayi tafito ta shirya agurguje, falo ta leka tagani ko mami tafito domin sam bata so mamin ta fahimci cewar yusleem awurinta ya kwana, ganin mami bata fito ba sai masu aiki dake faman mopping din falon yasata sakin ajiyar zuciya,
Girgiza kai tayi bayan ta rike hannunshi cikin nata,
"A'a yaya yusleem, mubi umarninta mu tattara kayanmu muje, bai kamata muyi watsi da maganarta ba.."
Tashi tayi batare da tajira abinda zaiceba ta shiga tattara kaya dama kuma kayan ba wadansu masu yawa bane, cikin toilet ta shiga ta kwaso inner wears dinsu dake shanye tazo ta zuba acikin trolley, har lokacin yusleem na zaune baiko motsa ba,
Kayan da tasan bazai yiyu su tafi dasu yanzuba ta tattara wuri daya ta adana sannan tafita daga dakin taje dakin maman amir tayi mata sallama, kasancewar sunyi sabo maman amir harda kuka, ita kanta Hafsat din da hawaye tadawo cikin dakin,
Tashi yayi ya rungumota jikinshi yana murmushi,
"Menene na kukan kamar ance bazaku sake haduwa ba..., sorry.."
Har lokacin hawayen basu bar zuba a idonta ba,
"Ya isa haka, kiyi shiru dan Allah"
Dakyar ta iya tsayar da hawayen yusleem ya dauki trolley dinsu suka fita acikin ranshi yana mamakin mata su babu wuya yanzun nan zasuyi maka kuka,
Har waje mutanen gidan suka rakasu duk da ba wai wani zumunci mai zurfi sukeyi ba,
Adaidaita sahu suka shiga yakaisu har gidan mami,
Gidan yana nan kamar da babu abinda ya sauya sannan ga ma'aikata nan kowa yana aikinsa kamar yanda suka saba, ganin su yusleem yasa masu gadin gidan saurin amsar kayan dake hannunsu suka shigar musu dashi ciki,kowa sai sannu da zuwa yake yiwa yusleem domin duk atunaninsu daga doguwar tafiya yadawo,
Acikin falo suka iske mami tana zaune tana shan ruwan lipton sannan ga soyayyen chips with kidney sos tana dan tsakura kadan kadan tana ci da dukkan alamu sai yanzu take yin breakfast,
Jin sallamarsu yasanyata dagowa ta kallesu bayan ta amsa, akasa Hafsat ta zauna yayinda yusleem yazauna akujerar dake kusa da ta mami,
"Hafsa ga abinci can maza tashi kije kici kinji..."
"Wallahi mami munci abinci sai dai idan anjima.."
Shiru mamin tayi batace komai ba taci gaba da kurbar ruwan tea dinta, suna nan zaune shiru babu wanda yasake magana har mami ta kammala cin abincin,
Sunkuyar da kai Hafsat tayi tasoma bawa mami hakuri,
"Mami dan Allah kiyi hakuri da abinda yafaru, wallahi ba laifinsa bane laifina ne domin nice nabashi wannan shawarar kuma nima nayi hakanne dan gudun kada mu tayar miki da hankali, amma dan Allah kiyi hakuri.."
Ajiyar zuciya mami tayi ta kalli yusleem sannan ta kalli Hafsat,
"To shikenan Hafsat nahakura, amma meyake faruwa? Nasan dai duk yanda akayi akwai abinda ke faruwa daku"
"Ehh mami da akwai, bashin banki yaya yusleem yaci sukuma kin san dokarsu idan baka biyasu ba sai sun sayar da komai naka, to shima yaya yusleem din hakance tafaru kuma lokacin nasan idan kikaji hankalinki tashi zaiyi shiyasa nace mubari tukunna sai zuwa wani lokaci sai mu fada miki..."
Tafa hannuwa mami tashiga yi tana salati,
"To garin yaya?"
Kallon yusleem tayi,
"Kai agarin yaya kaciyo bashin banki batare da sanina ba?"
"Mami tsautsayi da kaddara, saboda dama tun asali da wannan bashin nasu nayi arziki, komai da kika sani nasune, nikuma nayi hakanne dan incika burinki inzama mai wadata kamar yadda kike muradi..."
Katse shi mami tayi cikin fada tace,
"Ungo nan.." Dakuwa tayi masa sannan ta dora da cewa,
"Shikenan kuma dan ina son kayi arziki sai kaje ka aikata ba daidai ba? Ai ni bance kayi kudi kota halin kaka ba, haba yusleem meyasa zakabi shawarar zuciya? Ko dan gaba karka sake aikata makamancin wannan, yanzu da ace sun kamaka sunje sun daureka me gari yawaya?"
Dan zamewa yayi ya jingina bayanshi da jikin kujerar ya lumshe idanuwansa,
Kallon Hafsat mami tayi,
"Bashida lafiya ko?"
"Ehh mami amma da sauki, matsalar dai baya iya cin abinci"
Shiru mami tayi ta danyi tagumi,
"Hakika wannan wata jarrabawa ce daga Allah, domin ni dinma duk kudaden dake cikin account dina na turawa yan makaranta domin sun kusa dawowa, gashi na sissiyo kayan abinci wadanda zasuyi mana 1 month,ma'aikatan gidan nan ma wallahi wannan watan ko albashi ban biyasu ba nace suyi hakuri sai yusleem yadawo.."
"To ai babu komai mami duk wannan ba wani abu bane Allah zai bamu mafita" inji Hafsat,
"To hafsa rashin lafiyar tashifa? Ni duk ita tafi daga min hankali"
"Mami babu komai insha Allah zai samu lafiya, gobe zamu sake komawa asibitin ma ayi masa test..."
"To wai menene ke damunsa?" Mamin ta tambaya cikin damuwa,
"Mami harda ulcer dai saboda baya cin abinci wallahi"
"To Allah yabashi lafiya, goben sai muje asibitin mugani"
Shi dai yusleem yana jinsu baiyi magana ba da zaman kujerar ya isheshi ma dakin surayya yashiga wanda yake makotaka da na mami yaje ya kwanta akan gadonta,
Ita kuma mami afalo duk tabi ta damu sai jajanta rashin lafiyar yusleem takeyi, Hafsat dince ma mai karfin halin kwantarwa da mamin hankali tana cewa babu komai,
Saida lokacin salla yayi sannan Hafsat ta dauki kayanta ta nufi bedroom din surayya, akwance ta samu yusleem amma ba bacci yakeyi ba,
"Yaya yusleem tashi kayi salla..."
Tashi yayi yana kallonta,
"Hafsat meyasa baki fadawa mami gaskiyar abinda yafaru ba? Saboda ko dan nan gaba ya kamata ace tasani"
Zama tayi kusa dashi,
"A'a yaya yusleem fadar bata da alfanu hakan dai da akayi shine daidai"
"Shikenan.." Abinda yace kenan yatashi zai fita, bin bayanshi tayi zuwa falo ta dauki trolley din kayanshi tabishi, part dinsu Abdul ya bude yashiga, bedrooms biyu ne aciki sai falo domin suma samarin kowa da dakinshi, dakin khalifa yashiga tana biye dashi, juyawa yayi ya kalleta,
"Wai kina nufin ke adakin surayya zaki zauna?"
"Ehh mana"
Murmushi yayi ya karbi trolley din hannunta,
"Ashe dama karya kike da kikace bazaki iya kwana babu niba.."
Murmushi ne ya kwace mata tajuya zata fice yayi hanzarin rikota,
"Debo kayanki kidawo nan"
"Tohm" ta amsa amma bawai aikatawar zatayi ba domin tana jin nauyin mami ba kadanba,
Sakinta yayi tafita shikuma ya nufi cikin toilet.
Koda takoma part din mami salla tayi tafito falo nan ta hango kuku yana shirya lunch akan table, fitowar mami ne ya katse mata tunaninta,
Kan table suka hau, fried spaghetti da salad kukun yadafa sai kunun shinkafa, suna ci suna hira har suka gama, kunun Hafsat ta dauka tatafi kaiwa yusleem ko zai iya sha,
Akan carpet din salla ta sameshi yana tura sako ta email dinshi ackin laptop,
"Yaya yusleem ga kunu.."
Dagowa yayi ya karba ya dan kurba, zama tayi agefen gado, babu laifi yadan sha kunun ganin haka yasa taji dadi sosai, maganinshi ta dauko mishi ya karba ya hadiya daga nan tatashi tafita.
Wayarta ta Kunna bayan ta koma, ko minti biyu ba ayiba Ummi takirata, cikeda zumudi ta dauka suka gaisa nan take fadawa ummin cewar yau suka dawo amma suna gidan mami,
Suna gama waya da ummin kiran Amina yashigo, ita dinma korafin bata samunta awaya tayita yimata gashi ta jima da haihuwa mijinta yanata zuwa gidan domin yafada mata amma baya samunsu, Allah yaraya Hafsat tayi mata tace sunyi tafiya ne amma tunda sun dawo tana nan zuwa,
Komawa wurin mami tayi bayan sunyi sallama da Amina, nan take fadawa mami yusleem yadan sha kunun da takai masa tunda hakane zata rinka dama masa kullum.
Misalin karfe 8:30 nadare suna zaune afalo suna kallon tashar zee world itada mami sai gashi yashigo da cup din kunun data kaimasa, zama yayi yasoma kurbar kunun, Hafsat da mamine ke dan yin hira lokaci zuwa lokaci yana zaune yana jinsu,
Yana kallo hafsat ta shige daki bayan tayi musu saida safe, itama mami ba ajima ba tashiga nata dakin suka barshi afalo shi kadai, sai wurin 11 yakashe tv da sauran kayan wutar dake cikin falon, dakin surayya wadda Hafsat ke ciki ya shiga ya maida kofa ya rufe, gani yayi harta jima da yin bacci, bargon yabude yashiga yayi kwanciyarshi tareda mannuwa ajikinta.
Said a asubah sannan Hafsat tasan yana cikin dakin, tashi tayi tashiga bathroom tayi alwala tafito, ahankali tafara tashinsa saboda bata son mami ta jiyo,
Tashi yayi yana lullumshe ido alamun baccin bai isheshi ba,
"Yaya yusleem katafi saida safe..."
Hammar da yafara ya karasa sannan ya kalleta,
"Ina zan tafi?"
"Masaukinka..."
Baice komai ba yasauka daga kan gadon yanufi toilet, lokacin da yafito har ta idar da raka'atanul fijr tana kokarin tada ikamar sallar asubah,
Tashi yayi yakoma kan gadon ya kwanta bayan ya idar da sallar, yana kokarin lulluba da bargo Hafsat ta bazamo tazo tana masa magana kasa kasa,
"Dan Allah yaya yusleem katafi.."
"Ina?"
"Dakinka mana, bana son mami tazo taganka"
Kafin yabata amsa suka fara jiyo knocking abakin kofa da sauri Hafsat ta diro, maganar mami tajiyo tana cewa,
"Hafsat, Hafsat kitashi asubah tayi.."
"Na'am mami"
"Au ko kin tashi ma?"
"Ehh mami"
"To shikenan.."
Daga nan tajiyo alamun tafiyar mami,hannu ya mika mata yana daga kwance,kafada ta makale ta kwabe fuska, shi dinma hakan yayi kamar yadda tayi,
"Zo dan Allah"
Kan gadon ta hau ta mika masa nata hannun, kama hannun nata yayi yajata ya kwantar da ita yaja musu bargo.
_Fatan alkhairi ga Hajjaju, Chuchu, Maman sultan, pheey, Maman humy, Anty sis, Dshanty, Reane_Gh,meela adeel,meernah parrot,khadija sadeeq,Billy s fari, Billy s jega, ummu abrar, anty Baraka, Maman mujahid da duk wadanda ban ambata ba, wannan shafin nakune kyauta domin jin dadinku._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
_DEDICATED TO MISS XOXO_
*Yau shafin nakune kawayena, Lubabatu mai tafsir, fiddausi sodangi,phertymah xarah Maman khadija, cwt Kausar Luv, Teemah Cool,Khaleesat Haidar, Hafsat bunza, Zee Rumah,Maman Shakur Benaxir oamar,Billy Galadanchi, ina yimuku fatan alkhairi aduk inda kuke...*
*41*
_Ina cikiyar RIRI TURAKI marubuciyar halal dina, idan sakona ya riskeki ni Ummi Shatu ina nemanki urgently._
***Misalin karfe 9 Hafsat tafarka daga bacci, juyawa tayi ta kalli yusleem wanda ke rike da hannunta yana kanannade da ita, dakyar ta iya tureshi daga jikinta ta tashi,
Wanka tashiga tayi tafito ta shirya agurguje, falo ta leka tagani ko mami tafito domin sam bata so mamin ta fahimci cewar yusleem awurinta ya kwana, ganin mami bata fito ba sai masu aiki dake faman mopping din falon yasata sakin ajiyar zuciya,