← Book details Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 30

Sashe 22

Alwashi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Amma shi mijin naki meyasa yaci taki amanar yaje maza suka bata masa rayuwa? Shifa da maza yan uwanshi ma yarinka alaka,Bari infada miki gaskiya kidaina wahalar da kanki akan mijunki domin situation din da yake ciki yanzu bazai taba kallonki a matsayin mace ba bare har ya iya kusantarki saboda lalurar dake tare dashi, gaba daya bayanshi yakusa lalacewa domin sperm din dake shiga ciki babu wurinda zai fice shine sai yarinka taruwa yana taruwa har idan yakai wani stage sai wurin ya lalace har tsutsotsi su rinka fita ta wurin dan haka kidaina wahalar da kanki abanza, ni zan rinka bashi magani kyauta duk da tsadarshi mutukar kin amince da bukatata domin nan asibiti nane wadannan magungunan kuma tun daga India nake iyo ordersu ake kawo min.....!"

Sassauta muryarshi yayi cikeda yaudara da son janyo hankalinta,

"Kinga maimakon ki zauna kina yimasa wahala bayan bazai iya amfana miki komai ba gara kisamu wanda zai rinka debe miki kewa duk lokacin da kika so...!.

*_Ummi Shatu_*👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

_Kuna ina? Group members na Duniyar makaranta group 1&2 wannan shafin mallakinku ne domin jin dadinku...!_

*36*

***Kafin ta k'arasa wurin yusleem tayi karfin halin tsaida hawayen dake yi mata ambaliya akan kuncinta,

Murmushin karfin hali ta kakaro tayi lokacin da ta isa wurin yusleem,

"Yaya yusleem tashi muje..., anjima zan dawo na sai maka maganin saboda yanzu kudin hannuna bai kai ba"

Kallonta yayi yana jingine ajikin kujerar dake jere acikin reception din,

"Nawa ne?"

"Ka tashi muje kawai yaya yusleem..."

Bai sake yin magana ba yatashi, hannunshi ta rike suka fita, suna fita suka samu keke napep suka shiga,

Lokacin da suka koma gida ruwan zafi kadai ta dafa mishi domin baya iya cin abinci komai yaci sai yayi amansa, tana kokarin fita maman amir ta aiko mata da dan wake,

Kasa zaunawa taci tayi saboda idan har ba kudin nan taje ta nemo ta siyowa yusleem magani ba hankalinta bazai taba kwanciya ba,

Wurin kafintocin da suka siyi kujerunta takoma tasake kai musu tallar dayan kujerun nata na babban falo babu bata lokaci suka tafi gidan taje ta bude musu,

Duk haduwar kujerun nan da kyawunsu amma sai kafintocin sukayi mata tayin wulakanci wai dubu 60 zasu siya, kin siyarwa tayi nan suka kara dubu goma yazama dubu saba'in,ganin kudin basu cikaba yasata fito musu da wani show glass dinta wanda aka zuba mata humra da turaren wuta aciki, dubu goma sha biyar suka siya,

Saida suka fitar da kayan sannan ta rufe gidan tatafi, kai tsaye asibitin da sukaje da yusleem ta koma taje pharmacy ta siyo mishi maganin sachet daya,

Lokacin data koma gidan samunshi tayi yana bacci dan haka ta ajiye mishi maganin ta shiga wanka tafito, harta shirya bai tashi ba sai da ta idar da salla sannan taji motsinshi, juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu yaya yusleem"

"Yawwa, kin dawo?"

"Nadawo lokacin kana bacci.."

Mikewa tayi taje kusa dashi ta zauna,

"Yaya yusleem ga maganin nasiyo maka"

Kallonta yayi bayan ya gyara zamansa,

"A ina kika samo kudin da kika siyo?"

"Yaya yusleem kujerun nan naje nasiyar, lafiyarka yanzu ni tafi min komai.."

Hannunshi ya dora akan nata,

"Amma meyasa kika zabi sayar da kayanki? Ba ga nawa kayan ba wayoyina da laptop dina"

Girgiza masa kai tayi,

"Nawa kayanma naka ne, sannan nasan yanzu aduniya baka mallaki komai ba sai wayarka da laptop wannan dalilinne yasa bazan bada goyon bayan mu siyar dasu ba.."

"Nanah agaskiya ban san da wanne baki zan yimiki.."

Saurin rufe masa baki tayi bata barshi yakarasa ba,

"Inbaka maganin kasha yanzu ko zaka dan ci abincin da Maman amir ta Kawo min?"

"Bazan ci komai ba, bani maganin kawai nasha"

Tashi tayi ta dauko mishi ta hado da ruwa, abin mamaki kwata kwata kwayoyin maganin kwallo 6 ne aciki bamasu wani yawa bane sai dan karen tsada abinda yayi mutukar tayar da hankalin Hafsat,

Saida taga yasha maganin sannan ta dauko dan waken da maman amir takawo mata taci,

Hannu ya mika mata bayan tagama cin abincin ya kwantar da ita akusa dashi, kasa kasa yake yi mata magana suna yin yar hira.

Tunda Hafsat taga yakusa shanye maganin hankalinta yatashi nan tasake komawa wurin kafintoci ta sayar musu da gadajenta gaba daya taje ta siyo mishi magunguna saboda sam bata son ta doshi umminta ko abbanta da lalurar yusleem domin tasan asirinsu yana iya fallasa,

Haka taci gaba da daga kayanta tana sayarwa tana siya masa magani wanda yanzu haka bata da komai domin hatta su fridge dinta da sauran kayan kallonta duk ta siyar ta hada kan kudin ta ajiye wani kuma ta saiwa yusleem magani, yanzu abu dayane ke damunta shine kullum yusleem yana shan magani amma sauki baya samuwa kuma har yanzu baya iya cin abinci sai ruwan zafi gashi kusan 3weeks da zuwansu asibitin,

Sake shiryawa sukayi suka koma asibiti ganin dr sufyan, bayan yagama dudduba yusleem sun kama hanyar fita har sun kai kusa da gate Hafsat ta dakatar da yusleem,

"Yaya yusleem tsaya zo mukoma wurin dr akwai abinda nake son fada mishi"

"To Nana shiga kifito mana, bari injiraki anan"

Komawa office din dr sufyan Hafsat tayi, zaune tasameshi yana rikeda cup yana kurbar tea,

"Madam ya akayi?"

"A'a babu komai likita dama cewa nayi ko zaka sauya mana wani maganin saboda wannan din yayi tsada da yawa kuma har yanzu bai warkeba gashi baya iya cin abinci..."

Tunda tafara jawabi ya kura mata ido baya ko kiftawa har saida ta gama, ajiye cup din dake hannunshi yayi ya dora hannuwanshi akan table,

"Wato madam abinda zaki fahimta shine mijinki dan homo sexual ne wanda kusan lalurar ma taci karfinsa so dole sai magani mai karfi zai rinka sha, wannan maganin ba ako ina ake samunsa ba saboda tsadarshi dan inajin ma gaba daya garin nan baifi chemists guda uku zaki samu ba wadanda suke kawoshi, amma ni zan taimaka miki zan rinka baki maganin free mutukar zaki amince da abinda zan fada miki.."

"Likita ni sassauci nake son kayi mana ka sauya mana wani maganin wanda bai kai wannan tsada ba.."

"To ai madam condition din da mijinki yake ciki yanzu dole irin wannan maganin zai rinka sha,amma ni zan taimaka miki.."

"To nagode dr, nagode madalla.."

"A'a ai ba wani abu bane, zan baki card wanda yake dauke da address din gidana dake cikin G. R. A. Governor road.." Yakarashe maganar yana lasar lips dinshi,

Sai lokacin Hafsat ta fahimci inda maganar tashi ta nufa,

"Dr aini ba yar iska bace sannan banyi kamada matan banza ba wadanda zasu iya cin amanar mazajensu ba..."

Hannu ya daga mata,

"Amma shi mijin naki meyasa yaci taki amanar yaje maza suka bata masa rayuwa? Shifa da maza yan uwanshi ma yarinka alaka,Bari infada miki gaskiya kidaina wahalar da kanki akan mijunki domin situation din da yake ciki yanzu bazai taba kallonki a matsayin mace ba bare har ya iya kusantarki saboda lalurar dake tare dashi, gaba daya bayanshi yakusa lalacewa domin sperm din dake shiga ciki babu wurinda zai fice shine sai yarinka taruwa yana taruwa har idan yakai wani stage sai wurin ya lalace har tsutsotsi su rinka fita ta wurin dan haka kidaina wahalar da kanki abanza, ni zan rinka bashi magani kyauta duk da tsadarshi mutukar kin amince da bukatata domin nan asibiti nane wadannan magungunan kuma tun daga India nake iyo ordersu ake kawo min.....!"

Sassauta muryarshi yayi cikeda yaudara da son janyo hankalinta,

"Kinga maimakon ki zauna kina yimasa wahala bayan bazai iya amfana miki komai ba gara kisamu wanda zai rinka debe miki kewa duk lokacin da kika so...!.

*_Ummi Shatu_*👌🏻
© *HASKE WRITERS ASSO.*

*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_Dedicated to MISS XOXO_

*38*

***Kallon mamaki Hafsat ke yiwa khadija lokacin da ta fita kofar dakin domin ganin ko wacece ke sallama ganin khadijan yasata shiga cikin mamaki domin bata taba ganinta ba,

Dan gyara tsayuwarta kadan khadija tayi bayan ta zubawa Hafsat idanuwanta tana yimata kallon kurulla domin tun daga kafarta tafara kallonta har zuwa samanta,

"Baiwar Allah wakike nema?" Hafsat ta katse shirun nasu ta hanyar tambayar khadija,

"Ammm yusleem nagani shine nabiyoshi saboda ina son yin magana dashi.."

Shiru Hafsat tayi kafin tasake yin magana,

"Ok to amma daga ina kike kuma wa zance mishi?"

"Anan garin nake, kice mishi khadija mu'az ce.."

"To ina zuwa.." Hafsat tace tareda juyawa takoma cikin dakin,

Bin dukkan lungu da sako na gidan khadija keyi da kallo tana mamakin yanda akayi har yusleem yake iya yin rayuwa acikin wannan gidan na haya wanda babu komai na alatun more rayuwa aciki,

Acan cikin daki kuwa koda Hafsat takoma wurin yusleem zama tayi agefenshi gabanta yana faduwa,

"Yaya yusleem watace tazo nemanka wai sunanta khadija.."

Dan damm taga yayi kafin ya yunkura yatashi zaune,

"Yanaji kayi shiru ko akwai matsala ne? Ni tsoro nakeji kar asirinmu ya tonu,kar taje tafadawa mami.."

"Babu abinda zai faru insha Allah, ki shigo da ita"

Tashi Hafsat tayi ta sake lekawa inda khadija ke tsaye tana faman touching din phone dinta,

"Yawwa bismillah shigo.."

Tare suka shiga cikin dakin, ganin yanda dakin yake awani takure yasa khadija sake shiga cikin tsananin mamaki,

"Yusleem... Dagaske kaine anan? Me yafaru? Lafiya kuwa? Me yakawoka rayuwa a irin wannan gidan?"

Duk wadannan tambayoyin khadija ta jero sune cikeda mamaki lokacin da take yunkurin zama akasan carpet din dake dan shimfide agaban katifarsu,

"Yusleem wai dagaske kai dinne kodai idanuwana ne kemin gizo.."

"Khadija nine nan.." Yusleem yabata amsa yana kallonta,

Jijjiga kai tayi tagyara zamanta,

"To meya faru dakai har kazo nan? Saboda ni ban san wani abu yafaru dakaiba domin ko jiya agida da yamma muna tareda mami agidanmu.."

"Khadija wata matsala aka samu babba wadda ta tilasta min dawowa nan.."

"Amma dai mami bata saniba ko?"

"Ehh to gaskiya ban bari tasani ba har yanzun nan danake yimiki bayani saboda wani dalili.."

"To amma yusleem meyasa zakazo nan wurin kazauna? Irin wannan rayuwar sam bata dace dakai ba, dubi yanda duk kabi kasauya ka dawo wani kala..."

Murmushi yusleem yayi,
Chapter 22 · 0% Book details